Friday, 9 December 2016

SALLAR JUMA'A DA WASSU DAGA CIKIN HUKUNCE- HUKUNCENTA ( ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺃﺣﻜﺎﻣﻬﺎ )

SALLAR JUMA'A DA WASSU
DAGA CIKIN HUKUNCE-
HUKUNCENTA ( ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺃﺣﻜﺎﻣﻬﺎ )

Bismillahir rahmanir rahim.
Wassalatu wassalamu ala rasulillah,
Bayan haka:

A nan –da izinin Allah- zamu gabatar da bayanai ne akan "sallar juma'a" da
wassu daga cikin hukunce-hukuncenta,
kamar haka:

Na Daya: Hukuncin yin sallar juma'a da
dalilinsa: Zuwa sallar juma'a farilla ce akan mazaje; saboda fadin Allah madaukaki:

}ﻳَﺎ ﺃَﻳُّﻬَﺎ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺁﻣَﻨُﻮﺍ ﺇِﺫَﺍ ﻧُﻮﺩِﻱَ ﻟِﻠﺼَّﻼَﺓِ ﻣِﻦْ ﻳَﻮْﻡِ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ، ﻓَﺎﺳْﻌَﻮْﺍ ﺇِﻟَﻰ ﺫِﻛْﺮِ ﺍﻟﻠﻪِ ﻭَﺫَﺭُﻭﺍ ﺍﻟْﺒَﻴْﻊَ { ‏[ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ : ٩‏]

Ma'ana: (Ya ku wadanda suka yi imani
idan aka kira sallah a ranar juma'a to
ku tafi zuwa ga ambaton Allah, kuma ku bar kasuwanci) [Jumu'a: 9]. Da kuma saboda fadinsa (SAW):

"ﺭَﻭَﺍﺡُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺤْﺘَﻠِﻢ "‏( [1]‏) .

Ma'ana: (Tafiya sallar juma'a wajibi ne
akan kowani baligi). Da kuma saboda
fadinsa (SAW):

" ﻟَﻴَﻨْﺘَﻬِﻴَﻦَّ ﺃَﻗْﻮَﺍﻡٌ ﻋَﻦْ ﻭَﺩْﻋِﻬِﻢُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺎﺕِ، ﺃَﻭْ ﻟَﻴَﺨْﺘِﻤَﻦَّ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻰ
ﻗُـﻠُﻮﺑِﻬِﻢْ، ﺛُﻢَّ ﻟَـﻴُﻜﻮﻧﻦَّ ﻣِﻦَ ﺍﻟـﻐَـﺎﻓِﻠِﻲﻥ "‏( [2]‏) .

Ma'ana: (Wassu mutane su hanu kan
barin halartar juma'o'i, ko kuma Allah
ya yi rufi akan zukatansu, sa'annan su
kasance daga cikin gafalallu
rafkanannu).

Annawawiy yana cewa:
" ﻓﻴﻪ : ﺃﻥّ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻓﺮﺽُ ﻋَﻴﻦ "‏( [3]‏) .
Ma'ana: (A cikin wannan hadisin akwai
bayani dake nuna cewa lallai sallar
juma'a wajibi ce ga kowani mutum). Da
kuma saboda hadisi mai zuwa bayan
Dan lokaci kaxan , wanda a cikinsa aka ce:

"ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔُ ﺣَﻖٌّ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺴْﻠِﻢ "...‏( [4]‏) .

Ma'ana: (Juma'a haqqi ne na wajibi
akan kowani musulmi…).

NA BIYU: Ga wa juma'a take wajaba?

"SALLAR Juma'a" tana wajaba ga kowani musulmi, namiji, da , baligi, mai hankali, wanda ke da ikon halartarta, mazaunin gida; Bata kuma wajaba ga: Bawa, ko mace, ko yaro, ko mahaukaci, ko maras lafiya, ko matafiyi; wannan kuma saboda faxinsa (SAW):

"ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔُ ﺣَﻖٌّ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺴْﻠِﻢ ﻓِﻲ ﺟَﻤَﺎﻋَﺔٍ ﺇِﻻ ﺃَﺭْﺑَﻌَﺔً : ﻋَﺒْﺪٌ ﻣَﻤْﻠُﻮﻙٌ، ﺃَﻭِ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓٌ، ﺃَﻭْ ﺻَﺒِﻲٌّ، ﺃَﻭْ ﻣَﺮِﻳﺾٌ "‏( [5]‏) .

Ma'ana: ("Juma'a" haqqi ne na wajibi
akan kowani musulmi, ya yi ta a cikin
jama'a, sai mutum hudu: Bawa da ake
mulkarsa, ko mace, ko yaro, ko maras
lafiya).

Matafiyi kuma juma'a bata zama wajibi
akansa saboda Annabi (SAW) bai
kasance yana sallatarta ba a halin
tafiye-tafiyensa ba, kuma yinin
ARAFAH –a zamaninsa- ya dace da
ranar JUMA'A, amma tare da haka sai
ya sallaci AZAHAR, ya kuma hada ta da
LA'ASAR.

Amma matafiyin da ya sauka a garin da ake tsayar da juma'a to mafificin lamari akansa shine ya sallace ta tare da 'yan'uwansa musulmai.

Kuma idan da bawa ko mace ko yaro ko maras lafiya ko matafiyi suka halarci sallar juma'a to sallarsu ta inganta, kuma ta isar musu; ba sai sun yi sallar azahar ba.

Na UKKU: Lokacin sallar juma'a:
Lokacin yinta shine lokacin yin sallar
azahar; daga bayan rana ta yi "zawali"
zuwa inuwar kowani abu ta zama kamar tsawonsa; wannan kuma saboda hadisin Anas dan Malik (RA) lallai Annabi (SAW) ya kasance yana yin sallar juma'a a lokacin da rana take
karkacewa([6] ).

Wannan kuma shine abinda aka rawaito daga sahabban Annabi (SAW) daga aikinsu ([7] ). Don haka; duk wanda ya riski raka'a daya kafin lokacinta ya fita to haqiqa ya riski
juma'a, in kuma ba haka ba sai ya
sallaci azahar; saboda fadinsa (SAW):

" ﻣَﻦْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺭَﻛْﻌَﺔً ﻣﻦ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻓَﻘَﺪْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺍﻟﺼَّﻼﺓ " ‏( [8]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda ya riski raka'a
Daya daga sallah to haqiqa ya riski
wannan sallar).

NA HUDU: Menene ya haramta a ranar
juma'a? Haramun ne "mamu" ya yi
magana alhalin limami yana huduba ;
saboda faxinsa (SAW):

" ﻣَﻦْ ﺗَﻜَﻠَّﻢَ ﻳَﻮْﻡَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻭَﺍﻹِﻣَﺎﻡُ ﻳَﺨْﻄُﺐُ ﻓَﻬُﻮَ ﻛَﺎﻟْﺤِﻤَﺎﺭِ ﻳَﺤْﻤِﻞُ
ﺃَﺳْﻔَﺎﺭًﺍ"‏( [9]‏) .

Ma'ana: (Duk wadda ya yi magana a
ranar juma'a alhalin limami yana
huduba to kamar jaki ne da ke dauke da
laftun littatafa). Da kuma saboda
fadinsa (SAW):

" ﺇِﺫَﺍ ﻗُﻠْﺖَ ﻟِﺼَﺎﺣِﺒِﻚَ : ﺃَﻧْﺼِﺖْ، ﻭَﺍﻹِﻣَﺎﻡُ ﻳَﺨْﻄُﺐُ ﻓَﻘَﺪْ ﻟَﻐَﻮْﺕَ "‏( [10]‏) .

Ma'ana: (Idan kace wa sahibinka: Yi
shiru, alhalin limami yana huduba to
lallai ka yi wargi). ''Lagawu'' shine:
magana na barna yasashshe.

Kuma haramun ne mutum ya tsallake wuyan mutane a lokacin huduba ; wannan kuma saboda fadinsa (SAW) ga mutumin da ya ganshi yana qetare wuyan mutane

"ﺍﺟْﻠِﺲْ ﻓَﻘَﺪْ ﺁﺫَﻳْﺖ"‏( [11]‏) .

Ma'ana: (Ka zauna saboda ka cutar).
Lallai kuma cikin wannan aikin akwai
cutar da masu sallah, tare da shagaltar
dasu ko hana su sauraron huduba .

Amma shi kuma limami ba laifi ya
tsallake wuyan mamu idan ba zai iya
zuwa wajen minbari ba har sai ya
aikata hakan. Kuma ''makruhi'' ne a raba tsakanin mutum biyu; wannan kuma saboda fadinsa (SAW)

" ﻣَﻦِ ﺍﻏْﺘَﺴَﻞَ ﻳَﻮْﻡَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ... ﺛُﻢَّ ﺭَﺍﺡ ﻓَﻠَﻢْ ﻳُﻔَﺮِّﻕْ ﺑَﻴْﻦَ ﺍﺛْﻨَﻴْﻦِ ﻓَﺼَﻠَّﻰ ﻣَﺎ ﻛُﺘﺐَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻟَﻪ ... ﻏُﻔِﺮَ ﻟَﻪُ ﻣَﺎ ﺑَﻴْﻨَﻪُ ﻭَﺑَﻴْﻦَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ
ﺍﻷُﺧْﺮَﻯ "‏( [12]‏) .

Ma'ana: (Wanda ya yi wanka a ranar juma'a,… sa'annan ya tafi sallah, bai
rabe tsakanin mutane biyu ba, ya kuma
sallaci abinda aka qaddara masa… an
gafarta masa abinda ke tsakaninsa da
juma'a ta daban –ta gaba-).

NA BIYAR: Da me ake riskar sallar juma'a? Ana riskar sallar juma'a ne da
riskar raka'a guda daya tare da limami;
saboda ya zo daga Abu-hurairah (RA),
daga annabi (SAW) yace:

" ﻣَﻦْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﺭَﻛْﻌَﺔً ﻓَﻘَﺪْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺍﻟﺼَّﻼﺓ"‏( [13]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda ya riski raka'a
guda daga juma'a to haqiqa ya riski
wannan sallar).

Amma idan ya riski abinda ke qasa da raka'a to a nan sai ya sallaci azahar.

NA SHIDDA: Shin juma'a tana da wata
nafila? Juma'a bata da wata sunna ta
nafila da ake sallatarta a gabaninta, sai
dai wanda ya sallaci gamammiyar
nafila gabanin shigan lokacinta babu
laifi ga hakan; saboda kwadaitarwan
annabi (SAW) kan hakan, kamar yadda
ya zo a cikin hadisin Salman (RA) da
ambatonsa ya gabata anan kusa da ke
cewa: (Wanda yayi wanka a ranar
juma'a, … sa'annan ya tafi sallar
juma'a, bai rabe tsakanin mutane biyu
ba, ya kuma sallaci abinda aka qaddara
masa). Da kuma saboda sahabbai (RA)
sun aikata hakan, Sannan kuma ''sallar
nafila'' tana da girman falala.

Sai dai kuma ba za a yi "inkari" ga
mutum ba idan har bai yi sallar nafila
gabanin sallar juma'a ba; wannan
kuma saboda ''sunna ratiba'' ta kan
kasance ne, bayan yin sallar juma'a;
raka'oi biyu, ko hudu, ko shida; saboda
annabi (SAW) ya aikata hakan, kuma ya
yi umurni da cewa a aikata shi; Ya zo
cewa:

"ﻛَﺎﻥ ﻳُﺼَﻠِﻲ ﺑَﻌْﺪَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﺭَﻛْﻌَﺘَﻴْﻦِ "‏( [14]‏) .

Ma'ana: (Annabi ya kasance yana
sallatar raka'oi biyu bayan ya yi
juma'a), An samu kuma cewa annabi
(SAW) yace:

" ﺇِﺫَﺍ ﺻَﻠَّﻰ ﺃَﺣَﺪُﻛُﻢُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔَ ﻓَﻠْﻴُﺼَﻞِّ ﺑَﻌْﺪَﻫَﺎ ﺃَﺭْﺑَﻊَ ﺭَﻛَﻌَﺎﺕٍ "‏( [15]‏) .

Ma'ana: (Idan dayanku ya sallaci juma'a to ya sallaci raka'oi hudu a bayanta), a wata riwayah kuma:

" ﻣَﻦْ ﻛَﺎﻥَ ﻣِﻨْﻜُﻢْ ﻣُﺼَﻠِّﻴًﺎ ﺑَﻌْﺪَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻓَﻠْﻴُﺼَﻞِّ ﺃَﺭْﺑَﻌًﺎ"‏( [16]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda zai yi sallah daga
cikinku bayan juma'a to ya sallaci
raka'oi hudu).

Amma dangane da raka'oi shida kuma:

To saboda ya zo daga Abdullahi dan
Umar (RA) cewa lallai shi idan ya
kasance a garin Makka sai ya sallaci
sallar juma'a, to ya kan zakuda gaba sai ya sallaci raka'oi biyu, Sannan ya qara zakudawa gaba ya sallaci raka'oi hudu, idan kuma a garin Madina ya sallaci juma'ar; to sai ya koma gidansa ya sallaci raka'oi guda biyu bayanta, ba
zai yi sallah a masallaci ba, sai aka
masa magana, sai ya ce:

"ﻛَﺎﻥَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠﻪِ r ﻳَﻔْﻌﻞُ ﺫَﻟِﻚ"‏( [17]‏) .

Ma'ana: (Manzon Allah –SAW- ya
kasance yana aikata haka). Daga abinda ya gabata sai ya bayyana cewa: lallai mafi qarancin ''sunna ratiba ta bayan juma'a'' shine: raka'oi biyu, mafi yawanta kuma shine: shida. Wassu malamai kuma suna ganin cewa: in za a yi ''sunna ratiba'' ranar juma'a a masallaci to sai a sallace ta raka'oi hudu, in kuma a gida za a sallace ta sai a yi raka'oi biyu ([18] ).

Da wannan sai ya zama ana sallatanta akan halaye daban-daban.

NA BAKWAI: Ta yaya ake yin sallar juma'a? Sallar juma'a raka'oi ne guda
biyu, ana bayyana karatu a cikinsu;
saboda Annabi (SAW) ya kasance yana
aikata haka, aikinsa kuma wani yanki
ne na sunnarsa, kuma malamai sun yi
"ijma'i" akan haka. Kuma sunna ne
limami ya karanta ''suratu aljumu'at" a
raka'ar farko bayan ya karanta ''fatihah'', a ta biyun kuma ''suratu
almunafiqun ([19] )'', ko kuma ya karanta ''suratu al'aalah'' a raka'ar farko, a raka'a ta biyun kuma ''suratu
algashiyah ([20] )''; saboda annabi (SAW) ya aikata haka.

Wannan shine abinda ya sauwaqa na
bayanai akan sallar juma'a, da wassu
daga cikin hukunce-hukuncenta, da
fatan Allah ya fahimtar da mu addininsa, amin!

([1]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1371, 3/89), kuma Albaniy ya inganta
shi (Sahihu aljami'i, lamba:  3521).

([2]) Muslim ya rawaito su (lamba:
865).

([3]) Sharhin Annawawiy ga sahihu
Muslim (6/152).

([4]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1054), Albaniy ya inganta shi (Irwa'u
algalil, lamba: 592).

([5]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1054), Albaniy ya inganta shi (Irwa'u
algalil, lamba: 592).

([6]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
904).

([7]) Ka yi dubi cikin littafin (Fat'hu
albariy, 2/450).

([8]) Abu-dawud ya rawaito shi, (lamba:
875), da Ibnu-majah (lamba: 468), kuma Albaniy ya inganta shi a cikin
(Irwa'u algalil, lamba: 496).

([9]) Ahmad ya rawaito shi (10230),
Alhafiz Ibnu-hajar a cikin Bulugu almaram yace: ''isnadinsa bashi da
laifi'' (Subulu assalam, 2/101-102,
hadisi mai lamba: 421).

([10]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
394), da Muslim (lamba: 851), ka duba
littafin (Irwa'ul galil, 3/84).

([11]) Abu-dawud ya rawaito shi
(lamba: 1118), da An-nasa'iy (3/103),
da Alhakim (1/288) kuma ya inganta
shi, Azzahabiy ya masa muwafaqa ,
kuma Albaniy ya inganta shi (Sahihu
Ibni-majah, lamba: 910).

([12]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
910). ([13]) Ibnu-majah ya rawaito shi
(lamba: 1121), kuma Albaniy ya
inganta shi (Sahihu Ibni-majah, lamba: 927, 928).

([14]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
937), da Muslim (lamba: 882).

([15]) Muslim ya rawaito shi (lamba:
881). ([16]) Muslim ya rawaito shi (lamba: 881).

([17]) Abu-dawud ya rawaito shi
(lamba: 1130).

([18]) Duba littafin (zadu alma'ad,
1/440).

([19]) Muslim ya rawaito shi (lamba:
877).

([20])Muslim ya rawaito shi (lamba:
878).

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Fri 09-12-2016

Thursday, 8 December 2016

MATSAFI YA FADA HANNUN 'YAR MADIGO

MATSAFI YA FA'DA HANNUN 'YAR MADIGO
********
Na hadu da wani daga Cikin Abokanai da na dau kusan Shekara 3 zuwa 4 bamu hadu ba, Sai dai a waya ko kuma A kafar sadarwa ta Facebook.

Ya bani Wani Labari da ya Girgizani tare da tunanin Anya kuwa irin wannan labari zan barshi a dunkule ba tare da na 'dan fincina wa mutane na shi ba. Ko ba komai wasu zasu fadaku tare da sanya Ido ga 'ya'yansu da Qannensu da matansu.

Shi Wannan abokin nawa yana da wani aboki wanda kusan baya jin shawararsu duk yanda suka bashi shawara (kuma zama dashi ya zamar musu dole ne.

Ablinda ke faruwa shine wannan abokin nasu ya kasance yana son wata kyakykyawar yarinya Qin wanda ya rasa Son wanda ya samu.

Yayi juyin duniyar nan akan ta so shi amma kuma ba ta ko sauraren shi balle har ya samu ta amince masa (ta yarda da soyayyarsa).

Kwatsam sai Zuciyarsa ta bashi shawara akan cewa, ai yaje ya kai ta wajen Wani wanda duk mai hankali ba zai so a kirashi da malami ba. Saboda yana amfani da malantaka ne yana bokanci.

Ya je ya sami bokan ya gaya masa shakkuwarsa. Nan take wannan bokan Sai ya je yayi tsibbace-tsibbacensa tare da kulle-kullensa da siddabaru akan yarinya ta so wannan yaron.

Ai kuwa cikin kan kanen lokaci sai wannan yarinya ta fada tarkon Aljannun da wannan yaron ya sa aka turo mata domin su rika nuna mata shi a matsayin masoyi.

Kwana tashi Sai ya zamo wannan yarinyar duk duniya bata ganin kowa face, wannan yaron. Shi kuma sai ya fara Jin dadi akan aikin boka yayi kyau.

To meya faru? Kwatsam sai Wata babbar macce ta kirayi wannan abokin nawa mai bani labari tare da gargadarsa akan ya yi maza ya umurci abokinsa ya rabu da wannan yarinyar saboda kayan su ne. Ina fatan wannan hausar ta fito da kyau.

Ma'ana Budurwarsu ce da suke yin madigo da ita (wa'iyazu billahi). Ya amince akan zai bashi shawara akan ya rabu da ita. Haka kuwa akayi ya kira abokinsu ya bashi shawara amma yaqi ji.

Bayan da wannan labari ya zowa saurayin sai kawai ya fara tunani a zuciyarsa cewa, dama wance tana madigo? Ai nan take ya shiga bincike akan ya gano gaskiya.

Ai kuwa sai ya gano Cewa, ashe tana Madigo kuma tafi kusan Shekara biyar tana wannan muguwar 'dabi'a (kenan wannan shibe dalilin da yasa taki amincewa da soyayyarsa tun farko, Sai da yaje wajen boka).

Nan ya fara nadama marar amfani. Eh nadama marar amfani kuwa saobda a duniya ya tsani yar madigo ko 'dan luwadi. Amma kash yau gashi ammasa Baiko da 'yar madigo.

Nan yaje wajen Bokansa akan a raba wannan magani da akayi domin ta soshi. Ai kuwa boka ya aiwatar da abinda ya umurce shi da yi (ya raba wannan magani).

Nan take taji bata sonsa kuma gashi an musu baiko. To meya faru ashe Ita ma tana da nata boka sai taje ta koka masa matsalarta.

Wannan boka yayi na shi tsafi ya gano cewa, tun daga farko magani yaron yayi mata. Ai kuwa da aka gaya mata sai tace ita ma ayi masa magani yaji duk duniya kowa baya so sai ita.

Nan take Wannan bokan ya aiwatar shi kuma wannan yaro sai gashi ya fada tarkon so da kaunar yarinyar baji ba gani.

Ganin irin yanda yake binta take wulaqantashi (kuma aurensu ya kusa), shi ya sanya wannan abokina mai bani labari ya shirya zama da yarinyar don yaji meye matsalar take yiwa abokinsa wulaqanci.

Ai kuwa sai ta fafe masa biri har wutsiya tare da gaya masa cewa, babu shakka ita 'yar madigo ce. Kuma ta lalata yara babu adadi kuma zata ci gaba da lalatawa.

Kuma auren abokinsa babu mahani domin tunda yayi mata magani ita kuma sai ta gwada masa ko wacece. Domin sai ta aure shi kuma bayan auren sai ta mayar da gidansa Kasuwa ta Safarar mata domin yin madigo (Wa'iyazubillahi).

Yanzu dai kam An kusa Aure.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Thus08-12-2016

Wednesday, 7 December 2016

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

"Musulunchi ba Yana Nufin Ka dauki Wuka ko Adda ba kayi kabbara ka kashe wani. A'a musulunchi na nufin zaman lafiya da kyakykyawar mu'amula."___ Cewar, Sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar III.

"Ga Wani gwaji da yakamata muyi domin samun Kyakkyawar dangantaka da mu'amula."

"Mazaje Ku taimaki matayenku a aikace-aikacen gida, Sannan Idan zakuci abinci (misali da dare) ku dauka da hannunku ku ciyar dasu. Idan ka ciyar da ita to ita ma ta sanya hannunta ta ciyar da kai."___Cewa, Mufti Menk.

"Rayuwarka Kamar Photo Ce, Shi kuma Musulunchi Kamar Gidan sanya photo ne. Idan har kai musulmin kirkine, to ka dauko gidan photon nan ka sanya shi ciki. Kayi amfani da ilmin da kaji. Ka tafiyar da maganganu a aikace musulunchi ya zamo a cikin kirjinka. Kayi maganar gaskiya kada ka karkatarda magana. Kuma kada kayi da'awar abinda baka da shi sannan ka aiwatar da musulunchi a dukkanin rayuwarka."

"Babu wata kasa ko Al'umma da zasu ci gaba makawar basu bi dokokin Allah ba Sannan basu girmama Shuwagabanninsu ba, kuma basu bi koyarwar malamansu ba. Ka mu'amulancin malamai tsawon kwanakki bakwai dake cikin sati. Ka roki Allah tsayuwa akan Ibada ba saudaya ba domin ita ke bunkasa kasa" ___ Cewar, Sheik Assim Al-Hakeem.

"Allah yana Son Masu son Junansu ba don komai ba sai domin Allah. Makasudin samun nasara a wannan rayuwa shine dukkannin mu mu zama abu guda saboda Allah"

"Kada mu bari Zuciyoyinmu su jamu zuwaga ganin kyashin juna ko kuma Yawaita ganin laifin juna idan muka hadu wuri daya hakika zamu kai ga dacewa. Mu rika yiwa junanmu godiya. Sannan mu so makwaftan mu kamar yadda muke son kawunan mu. Hakika murmushi abincin ruhine mu zama masu gaskiya game da rubutun mu. Ina rokon Allah ya taimake mu duka. Mu rika rokon hadin kai ba rarrabara kawuna ba."__ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Nawane ake Sayarda Manyan Gidaje a Abuja da Lagos? Hakika farashin da zaka biya ka shiga Aljanna Shine, ka yafewa dan uwanka duk laifin da yayi maka. Hakika hakkine akan kowanen mu akan ya yada zaman lafiya kuma umurnine akan mu rika yafewa juna. Ya ku mutane! Ku yada zaman lafiya tsakanin ku. Sannan ku ciyarda matalauta da masu jin yunwa. Ku sowa dan Uwanka/'yar uwarka abinda kake sowa kanka. Hakika ba zaka zama mai Imani ba har sai ka sowa dan uwanka abinda kake sowa kanka. Allah yana son masu gaskiya."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Idan har da gaske kana Son Manzon Allah (SAW) to kabi Allah sannan ka zama mai yafiya ka zama mai son Juna, Ka ajiye duk wani rudani gefe kada ka nuna kafi kowa iyawa domin yana kai mutum zuwa ga dolanci. Ka zama mai taka tsan-tsan ga lamurranka kada ka bari zuciyarka ta rufe ga gaskiya. Musulunchi ba addini ne kawai ba, A'a musulunchi hanyar Rayuwa ce. Nemi ilmin gaskiya. Allah ya Albarkacemu da kyakkyawar fahimta ka tsare mu da Ilmi mai yawa saboda ilmi mai yawa Wani lokaci cuta ne."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kayi hankali da yawan ganin laifin mutane da yawan ganin Laifin Shuwagabanni. Ka yarda da kanka ka gyara halayenka wannan shi zai cenja gidajenmu, da 'yan uwanmu da Al'ummar mu dama Duniya gaba ki daya ka yarda da kanka ka kauracewa miyagun halaye ka tuna cewa Adanannar dukiyarka na Aljanna. Ka yarda da Allah kada ka taba debe tsammani kayi kaffa kaffa kada ka taba debe tsammani daga rahamar Allah. Allah Yace; "KA GAYAWA BAYINA WAYANDA SUKA CUCI KAWUNANSU KADA SU TABA DEBE TSAMMANI DAGA RAHAMAR ALLAH"..Ya Allah ka hada mu a lambun Aljanna."____ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kada ka shagaltu da ilmin da ka samu na Wannan taro (na wa'azi) na kwana biyu kace ya isheka kawai. Kayi godiya ga malaman kasarku da suka dade suna karantarda ku tare da tarbiyantar da ku."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Allah ya kara mana Imani. Hakika addinin Musulunchi addini ne na Zaman lafiya ba na rikici ko tashin Hankali ba. Mu tashi tsaye kada mu sanya gajiyawa. Mu zama masu Alfahari ba masu girman kai ba."____Cewar, Ustaz Abubakr Sadiq

Ni da na fassara Ina fatan Wayannan Gwala-gwalan Kalamai zasu samu wurin zama a cikin Zukatan mu.

Anyi Wannan Wa'azin ne a  dakin taro da ke Abuja a Ranar 3 da Ranar 4  ga watan 12. 2016.

Fassarawa, Jamilu Sani Rarah Sakwkwato.

Monday, 5 December 2016

MEYE LAIFIN SHUGABAN KASA BUHARI GA SADAKIN ZARAH?

MEYE LAIFIN SHUGABA BUHARI A CIKIN SADAKIN ZARAH?
*******
Tunkusan Lokacin da Akayi Sadakin Zarah 'yar Gidan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na ke samun Sak'onni akan ba'aji nayi sharhi ba game da wannan Sadakin.

Alhamduli Lahi bayan 'yan Uzurukka da suka sha gabada Sai yau Allah ya kaddare ni da Cewa wani abu game da wannan Sadaki.

Har yau har gobe Ina Kara kira ga 'yan Arewar mu akan Don Allah su daina Sanya Kansu cikin Kwano ko k'ok'o suna tunani su rika bude kawunansu suna tunani.

Da farko ina son mutane su san Wanene Ahmad Indimi sannan suyi tunani mai kyau game da shi Kafin Su rika yanke Hukunci game da duk wannan Sadaki na shi.

Kafin Nayi bayani akan Ahmad Indimi bari na fara bayani akan Jahar Borno (In da Cen ne Garin Su Ahmad da Mahaifansa).

Wani daga cikin Masu son jin ra'ayina game da wannan Sadakin ya min tambaya game da wannan sadaki na Zarah Buhari.

Amma mai makon In bashi amsa sai na kyale shi Na kira wata baiwar Allah Wacce 'yar asalin maiduguri ce.

Bayan na kira ta dauka sai na saka Speaker domin yaji me zamu tattauna ana akai. Bayan mun gaisa sai na tambayeta Cewa, "Shin har yanzu A maiduguri Miliyan daya ake Sadaki?"

Sai tayi dariya tace dani, "Humm yanzu wannan Recession da ake ciki wa zaiyi wani sadaki milion 1"

Sai nace, "To nawa ake yin Sadaki Maiduguri a yanzu?" Sai tace dani, "Dubu d'ari bakwai, d'ari biyar Ida kuma mutum bai da shi sosai Cikin Anyi hankuri an matse sai ya biya Naira dubu dari biyu da hamsin ko kuma dubu d'ari da Ashirin."

Bayan mun gama magana mukayi Sallama na kashe waya ta. Tare da tambayar wannan mai tambaya ta ko kaji wayar da nayi? Sai yace da Ni "Eh yaji ashe haka maiduguri suke."

Sai nace dashi to Wanda yayi wa Zarah Buhari Sadaki 'dan Maiduguri ne, kuma a maidugurin ma su ne manyan masu kuddi.

Baban Ahmad Wato Muhammad Indimi Surukine ga Tsohon Shugaban Kasa Ibrahim Badamasi Babangida IBB.

Sannan Muhammad Indinmi Shike da kamfanin nan na Oriental Energy Resources Limited, kamfanin da ke da rijiyoyin mai har guda uku da suka hada da: OML 115 da ta Oldwok da kuma ta Ebok.

Sannan Shi Ahmad Indimi yana daga Cikin Manyan Daretoci na Kamfanin domin Shine daracta na Ukku a kamfanin.

Sannan Ahmad Indimi din da kake ji yana daga Cikin Matasan Samari da ke da taimako domin IDPs INTERNAL DISPLACE PERSONS (Wato mutanen da rikici yasa suka bar mazauninsu) ya taimakesu kusan da Naira Miliyan d'ari biyu har da wani abu.

Sannan Idan ka koma B'angaren Ita kanta Zarah Duk kusan Cikin 'ya'yan Manyan Kasarnan Kaf (ban cire ma kowa ba daga cikinsu), ta fisu taimako tare da Neman Dukiya. Domin har Ophanage (gidan marayu) take da shi.

To mene A Ciki don Shi Wannan matashin Mai kuddi ya bi Al'adar Garinsu ta yin Sadaki da Tsada? Tun da dai ba'a kaiyade kuddin Sadakin ba a musulunce.

A musulunce Kuddin Sadakin Bana yanda malamai suka yi kiyasi shine naira 8400, Shin don Allah akwai wanda yaga In da akayi Sadaki 10,000 a bana? In kuwa babu inda akayi to me yasa don shi yayi al'adar garinsu (na yin sadaki da tsada) abu zai zama abin Ganin Laifi.

Ni banga laifin Wannan Ba Gaskiya sai dai abinda muke cewa da Su Wayannan Samarin Sunyi kwaikwayo da Sunnar Manzon Allah (Saww) na Takaita Sadaki da Sun kyauta. Domin Manzon Allah (saww) yake cewa, Aure Mafi albarka shine wanda sadakinsa ya zamo mafi sauki".Kuma da Sun bar tarihi a kasarnan.

Da kuma sun kwaikwayi auren Nana Fatima da Sayyidina Aliyu da Sun burge duk wani ma'abocin Sunnah.

Lokacin da Sayyidina Aliyu (Rta) ya nemi Auren Nana Fatima (rta) bayan Annabi (Saww) ya tambayeta kuma ta amince sai Manzon Allah (Saww) ya cewa Sayyidina Aliyu (RA): "Ya Aliyu, shin kana da wani abu da zan daura maka aure da shi (sadaki)?".

Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya ce: "Sai takobina da garkuwata, sai kuma rakumina na ban ruwa ", (a wata ruwayar an ce doki ne maimakon rakumin)

Sai Manzon Allah (Saww) ya ce: "Amma takobinka kana da bukatarsa, za ka yi yaki da shi a tafarkin Allah kuma ka kashe makiya Allah da shi.

Rakuminka kuma kana shayar da (gonar) dabinonka da shi, haka kana daukar kaya da shi, kuma yana daukarka a tafiye-tafiyenka.

Don haka je ka yi yadda za ka yi da
garkuwarka". Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya je ya sayarwa Sayyidina Usman bin Affan (RA) da garkuwarsa a kan farashin dirhami 480, sai ya kawo wa Manzon Allah (saww).

Daga nan Manzon Allah (Saww) ya sanar da Musulmi zancen auren.

Haka kuma na So ace Zarah Buhari ta kwaikwayi Ummu Sulman An Ruwaito Cewa Sahabbai (RA) suna
Cewa, "FIYAYYEN AURE SHINE AUREN UMMU SULMAN (RA), DOMIN ITA SADAKINTA MUSULUNCI NE."

Ummu Sulman Itace Mahaifiyar Anas Bin Malik (Hadimin Manzon Allah (Saww)), lokacin da mahaifinsa ya rasu, taqi yin aure har Saida Abu Talha ya fito yana Sonta sannan ta amince zata aure shi amma da sharadi zaya Musulunta (Musuluntarsa Shine Sadakinta).

Bayan manyan attajirai da Masu mulki da Sadaukai sunyi ta fito mata amma taki amincewa dasu. To da ace Zarah Buhari ta Bukaci kada sadakinta Yayi tsada haka to babu shakka da ta kyauta.

Kuma ba zanga Laifinta ba ko na wanda zata aura ko mahaifanta don anyi mata sadaki naira miliyan 44, sai dai muna cewa a kamanta Sunnah ga dukkanin Abubuwa yafi.

Subhanallah...!

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Mon 5/12/2016

Wednesday, 30 November 2016

LABARIN YAJUJ WAMA JUJ

LABARIN YAJUJU DA MAJUJU.
*********

 
Allah (Swt) a Cikin Al-Qur'ani mai Girma Yana Cewa;

ﺣَﺘَّﻰ ﺇِﺫَﺍ ﻓُﺘِﺤَﺖْ ﻳَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻣَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻫُﻢ ﻣِّﻦ ﻛُﻞِّ ﺣَﺪَﺏٍ ﻳَﻨﺴِﻠُﻮﻥ


Ma'ana "Har sa'ad da aka bude Yajuju da Majuju alhali kuwa suna gaggawa daga kowane tudun kasa." (Suratul Anbiya aya ta 96(

Yajuju da Majuju, tsatso ne, na daya daga cikin ‘ya'yan Annabi Nuhu (Alaihis Salam).

A zamanin Annabi Ibrahim (Alaihis Salam) da akwai wani sarki da ake kira da Zulkarnaini, shi wannan sarki, Allah ya bashi iko da kuma Mulki tun daga Bangon Gabas har zuwa yamma.

Shine mutumen da ya zagaye duniya tun daga farkon Inda rana take fitowa har Inda take faduwa.
Wasu ma suna ganin Zurkarnaini Annabine, amma dai maganar gaskiya zurkarnaini Sarki ne kuma mutumin kirki ne da ya shimfida Adalci, shine ya gina wannan Katanga da ta raba wannan duniya da Yajuju da Majuju. Haka kuma, wannan Katanga an gina tane da narkakken karfe da
duwatsu da kwalta da ruwan dalma.

A zamanin Zulkarnain wadannan al’umma (Yajuju da Majuju) sun addabi mutane, shine al’ummar da
Zulkarnaini yake mulka suka rokeshi da ya gina musu katangar da zata rabasu da Yajuju da Majuju.
Yajuju da Majuju sunyi ta kokarin fasa wannan Katanga su fito amma kuma sun kasa.
Sunyi dukkan irin dabarunsu su yi tsalle su fito amma Allah bai basu iko ba, shine tun daga wancan lokaci har kawo yau suna nan suna kwakwule wannan Katanga domin su samu su fito, amma Allah ba zai basu iko ba, sai a karshen duniya.

Ibn Mas’ud (Rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (Saww) cewa. A daren da Manzon Allah (Saww) yayi Isra’I ya hadu da Babansa Annabi Ibrahim da Annabi Musa da kuma Annabi Isah, dukkansu sun tattauna akan shin yaushe ne Alkiyama zata tsaya, sun fara tambayar Annabi Ibrahim yace bai
sani ba.

Daga nan Annabi Musa yace shima bai sani ba, daga nan sai Annabi Isah yace babu wanda ya san wannan ranar sai Ubangiji shi kadai.

Sai Annabi Isa (Alaihis Salam) ya cigaba da cewa, abinda Ubangijina ya gayamin shine a karshen duniya, Dajjal zai bayyana, ya zama fitina daga karshe sai a sauko dani, idan ya hadu da ni zai dinga narkewa yana zagwanyewa, Haka nan Allah zai halakar da shi (Dajjal).

Sannan Musulmi zasu yaki kafurai, har sai takai matsayin da Idan kafiri ya buya a bayan wani dutse ko bishiya, zasu yi Magana su kirawo musulmi suce masa zo ga kafiri ka kashi shi.
Daga nan kuma, adalci zai yadu a ban kasa tsakanin Musulmi, can kuma sai Allah ya fito da Yajuju da Majuju. Zasu barko cikin wannan duniya ta gabas da yamma kudu da Arewa, suna shanye ruwa, suna cinye dukkan wani abu da suka yi arba das hi. A lokacin ne al’umma zasu je ga Annabi Isah suna mai rokonsa da ya roki Ubangiji Allah ya kade musu wannan Masifa da Bala’I na Yajuju da Majuju.

Sai Annabi Isah ya daga hannu ya roki Ubangiji, Allah mai girma da daukaka ya amsa, sannan ya dinga saukar musu da tsutsotsi daga sama, suna halakar da su, bayan sun mutu duniya gabaki daya zata cika da warin gawarwakinsu da jinanansu.

Daga nan kuma Sai Allah ya saukar da Ruwan Sama wanda zai wanke duniya gabaki daya ya wanke dukkan dattin gawarwakin Yajuju da Majuju.

Annabi Isah (Alaihis Salam), ya cigaba da cewa, daga zarar Allah ya saukar da wannan ruwa, to babu wani abu da yake gab da zuwa face Alkiyama.

Haka kuma An karbo hadisi daga Abu-Huraira (Rta), Cewa, Manzon Allah (Saww), ya ce “A kowacce rana wasu al’umma (Yajuju da Majuju) suna nan suna hake wata Katanga, da zasu shigo cikin wannan duniya.

Sai sun yi haka har sun gaji, sannan zasu fara hango harsken rana, abinda yake nuna hakarsu ta kusa cimma ruwa (ma'ana sun kusa bige ginin), sai kawai shugabansu, ya umarce su da su koma su kwanta su huta gobe zasu dawo su cigaba.

Cikin hukuncin Ubangiji washe gari suna zuwa, sai su tarar Allah (Swt) ya shafe wannan Katanga ta kara karfi da kwari, sama da yadda suka sameta a jiya. Haka zasu sake cigaba da tone wannan Katanga, su sake komawa, washe gari su sake ganinta kamar basu taba haketa ba.

Haka nan zasu yi ta yi, har sai lokacin da Allah ya hukunta fitowarsu. Idan sunyi aiki har sun bula katangar sun fara hango hasken rana, anan ne shugabansu zai umarce su da su koma su
kwanta, gobe idan sun dawo zasu cigaba, amma a wannan Ranat zai ce IN SHAA ALLAHU.
Bisa fadin IN SHAA ALLAHUN da shugabansu ya yi sai Allah ya amsa, washe gari idan sun komo zasu sami wannan Katanga yadda suka barta jiya! Bayan dawowarsu ne, washe gari, zasu ci gaba da yin aikinsu na bugun wannan Katanga.

Kuma cikin nufin Allah, zasu buge wannan gini su shigo cikin duniya daga katangesu da Allah yayi da al’umma, idan suka fito zasu shanye dukkan wani ruwa da sukayi ido hudu dashi, sannan zasu cinye dukkan wani abinci da suka gani, kai kusan dukkan wani abu da suka gani sai sun cinye shi.

kama daga Bishiya tsirrai da dabbobi, sannan zasu shiga kisan mutane babu ji babu gani!
A wannan lokacin Yajuju da Majuju zasu dinga harba kibau sararin samaniya. Suna harba kibiyoyi da masuna, sannan suna fadowa kasa suna masu digar da jini a jikinsu, anan ne Yajuju da Majuju zasu ce, mun gama da al’ummar da take a ban-kasa sannan kuma wadan da suke sama suma mun gama da su!
A lokacin da suka yi wannan ikirari ne kuma, Allah zai yi musu ruwan wasu irin tsutsotsi wadan da zasu dinga makalemusu a wuya suna cizonsu, haka nan, wannan tsutsa zata hakalasu gabaki dayansu a
cikin dare daya!

A duba a Cikin kitaab al-fitan, (hadisi 4080), 2/1364.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tues 30/08/2016

SANARWA MAI MUHIMMANCHI GAME DA MADIGO DA LUWADI

SANARWA MAI MUHIMMANCI
********
Ka karanta tabbas Zai amfaneka idan ma bai amfaneka ba zai amfani 'danka, 'yarka ko kuma qanenka ko 'dan uwanka. Tun kusan Watan January nayi Rubutu akan 'yan Mata masu 'dabi'ar yin Madigo (Lesbian), tun kusan wancen lokaci na samu kira daga wata baiwar Allah Wadda ta bayyanamin Dalilin shigarta harkar madigo da kuma halin da take ciki.

Yarinyar wacce mun dau kusan Mintuna arba'In mun waya ta shaida min dalilin shigarta Harkar madigo, In da ta bayyana min a makarantar gaba da Secondry aka koyar da Ita wannan muguwar 'dabi'ah.
"Bayan kaini makaranta mu hudu ne a dakin da nake, kuma nice karama a duk cikin wayanda muke daki 'daya da su, ranar da nazo na fara fahimtar 'yan Iska ne, domin kuwa a gado 'daya naga suna yin bacci duk da kowace nada nata gado."

"A haka har na fahimci me suke yi domin kuwa wani lokacin a gabana suke sheke ayarsu."
Yarinyar taci gaba da gayamin cewa, a hankali idan suna yi sai taji sha'awa ta taso mata, kwatsam rannan sai suka bukaci ta shiga cikinsu domin jin dadi. Da farko sai ta nuna musu ai ita bata sha'awar wannan mu'amula kuma tana ma son ta chanja 'daki ne domin kada ta takura musu.

Anan ne suka nuna mata ai babu damuwa tayi zamanta a dakin nasu domin halayenta na burgesu.
Kwatsam sai ranan suka nuna mata ai ta shigo cikinsu yafi tunda Allah bai fadi azabar da za'ayiwa mata 'yan madigo ba sai 'yan Luwadi. Sannan kuma tayi wannan shi ya fiye mata da taje tayi zini ko ta aikata Mistabution (ISTIMINA'I).

Ta shaida min da irin wayannan kalamai aka sanya ta a madigo kuma wallahi yanzu bata sha'awar kowane namiji, haka kuma bata sha'awar aure.

Ta kara shaidamin Cewa, Ita kadai ta lalata yara bata san adadiba, kuma yanzu tana son ta tuba amma ba ta san yanda zatayi ba.

Anan na bata wasu shawarwari tare da nuna mata muddin ta mutu bata tuba ba to kuwa akwai matsala domin Allah zai mata Ukuba fiye da yanda take tunani.

Wannan yarinyar tayi godiya ta kuma bukaci duk ranar da na samu lokaci don Allah Inyi fadakarwa game da Irin Wannan 'yan madigon Masu nunawa mutane madigo bai da wata azaba da aka tanadarwa masu yinsa, haka kuma macce zata ji dadi ba tare da ta rasa budurcin ta ba. Bayan Wannan Jiya14 ga watan October Jaridar Aminiya ta fitarda wani rubutuna game da Maza 'yan Luwadi.

Kusan karfe 10 na dare wani bawan Allah ya kirani, daga daukan wayan na san hankalinsa a tashe yake muryarsa na karkarwa. Ya shaidamin yana 'daya daga cikin masu neman Maza kuma kusan Shekarar sai 15 yana wannan lalata yanzu kuma kusan shekarar sa 10 da aure amma har yanzu ya kasa dainawa.
Yace min hakika babu yanda baiyi ba domin ganin ya bar wannan muguwar 'dabi'ah amma ya kasa.
Bayan gama wayar da shi tare da gama bashi shawarori akan ya tuba ya kuma kauracewa wayanda suke wannan ta'adi.

Cen kusan karfe 12 na dare wani ya kirani ya shaidamin daga wata jami'ah (dake arewa ) yake kira na, ya shaidamin yanda aka sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta luwadi (Wa'Iyazubillah).
Ya gaya min Cewa, wani ne ya sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta hanyar nuna masa ya zo su rika yin Romace ba tare da sun sadu ba. Wannan yafi yaje yayi zina.

Ya gayamin a hakan ya amince domin a tunaninsa Romac ba komai ba ne, ya gayamin a cikin Romace din ne kawai wata rana ya afka masa yayi masa luwadi.

Ya shaidamin hakika yanzu baya sha'awar macce, Sai dai maza, yace min wani lokaci har kashisa yake dauka ya shafa a al'aurarsa idan wannan sha'awar ta taso masa (Wa'Iyazubillahi).
Yan da kyau 'Yan Uwa mu rika Kula da Suwa Qannenmu da 'ya'yanmu da Abokananmu ke mu'amula domin gudun yin dana sanin a gaba.

Duk wanda yace maka kazo kuyi romace yafi kaje kayi Zina Wallahi karya yake maka Yana so ne kawai ya halaka maka rayuwa.

Sanan yana da kyau 'yan mata su san cewa, da madigo da Luwadi duka daya ne babu banbanci a wajen Azaba a gobe Qiyama. Sannan yana da kyau su san anya mafi sauri ta kamuwa da cutar Infection Itace ta hanyar yin madigo (lesbian). Su kuma samari su sani daga ranar da aka yi maka luwadi daga ranar Kashi ba zai taba tsayama ba. Daga kaji kashi da yazo.

Sannan masu yi yana da kyau su sani daga ranar da kayi sanadiyar wani fadawa cikin Muguwar 'dabi'ah to kuwa duk lokacin da akayi dashi ko yaje yayi sai an rubuta maka zunubi koda kana Cikin kabari ne.
Wannan Muhimmiyar Sanarwa Ce, Idan ka taimaka wajen Yada ta to ka taimaka wajen ya'da Alheri. Idan kuma ka qi yadawa to ka yi hasarar tarin Ladar da Za'a samu.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 15/10/2015

Tuesday, 29 November 2016

NAZARI AKAN YAWAITAR ZAZZABI (MALERIYA)

HUJEWAR OZONE LAYER YA FARA KAWO ANNOBA A CIKIN AL'UMMA.

Tun Kusan Lokacin da Na samu Labari akan k'aruwar Hujewar OZONE LAYER ( Bargon da ke matsayin kariya tsakanin duniya da kuma cutukkan rana), nake ta tunani akan wannan lamari.
A bangare daya kuma Yawaitar Mace-macen hadi da rashin lafiya da Suke Faruwa a Jahar mu ta Sokoto sai na tsaya nayi nazari tare da Bincike mai zurfi game da Wannan Lamari. Sai naga gaba days an dau wannan matsala kacokan an daurata ga zazzabin Cizon Sauro. Wanda kuwa ga dukkan alamu ba haka lamarin yake ba.

Shi dai Wannan OZONE LAYER masana suka ce abu ne tamkar bargo a sararin saman duniya kuma kariya ne ga (Sama) da kuma Mutane.

Suka kara da Cewa, shi wannan Bargon da ake kira ozone layer, yana shinfide ne a Sararin Samaniya domin ya zama kariya ga halittun kasa daga sinadaran da suke zubowa daga zafin rana wanda zasu cutar da 'dan Adam ta hanyar sanyawa mutane cututtuka (masu wuyar Sha'ani). To idan sinadirai masu cutarwa suka zubo sai su makale a jikin wannan Bargon na Ozone layer.

Babu Shakka Wannan Zance na Masana Ilmin Kimiya ba karya bane game da Wannan Bargon.
Domin tun Kusan Shekaru 1400 da suka Gabata Al-qur'ani Mai Girma ya gaya mana labarin wannan Bargon da ke Sama.A Cikin Al-qur'ani Mai Girma Allah (Swt) Yana Cewa, 

ﻭَﺟَﻌَﻠْﻨَﺎ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﺀَ ﺳَﻘْﻔًﺎ ﻣَّﺤْﻔُﻮﻇًﺎ ۖ ﻭَﻫُﻢْ ﻋَﻦْ ﺁﻳَﺎﺗِﻬَﺎ ﻣُﻌْﺮِﺿُﻮﻥَ

MA'ANA, "Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhali kuwa su daga ayoyinta masu bijirewa ne" (Suratul Anbiya aya ta 31). Sannan a Wata Ayar kuma Allah (Swt) Yana Cewa,

ﻭَﺍﻟﺴَّﻘْﻒِ ﺍﻟْﻤَﺮْﻓُﻮﻉِ


MA'ANA, "Da rufin nan da aka ɗaukaka." (Suratu At-Tur aya ta)
.
A Wani Wuri Kuma Allah (Swt) ya gaya mana Cewa, Wannan bargo kariya ne ga Mazauna kasa.

ﻗَﺪْ ﻣَﻜَﺮَ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻣِﻦ ﻗَﺒْﻠِﻬِﻢْ ﻓَﺄَﺗَﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑُﻨْﻴَﺎﻧَﻬُﻢ ﻣِّﻦَ ﺍﻟْﻘَﻮَﺍﻋِﺪِ ﻓَﺨَﺮَّ ﻋَﻠَﻴْﻬِﻢُ ﺍﻟﺴَّﻘْﻒُ ﻣِﻦ ﻓَﻮْﻗِﻬِﻢْ ﻭَﺃَﺗَﺎﻫُﻢُ ﺍﻟْﻌَﺬَﺍﺏُ ﻣِﻦْ ﺣَﻴْﺚُ ﻟَﺎ ﻳَﺸْﻌُﺮُﻭﻥَ

MA'ANA "Lalle ne waɗanda suke a gabaninsu sun yi makirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsa-shensa, sai rufi ya faɗa a kansu daga bisansu, kuma azaba ta je musu daga inda ba su sani ba." (Suratul An-Nahl aya ta 26).

Friedrich Schonbein Shine mutunen da ya gano Ozone a shekarar 1839, In da a Shekarar 1840 Gordon Miller ya gano amfanin wannan bargo na Ozone layer. Shi dai wannan bargon ya fara hujewa tun kusan shekarun 1980 inda wannan hujewar ta rika fadada tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu, in da a wannan shekarar ta 2016 aka gano wannan bargon yayi qatuwar hujewa.

Masana dai sun riga sun fadi Cewa, Wannan hujewar ta kan iya haifar da kafewar manya da kananan koguna, da kuma karuwar yawan ruwan da ke cikin manyan kogunan
wannan duniya.

Haka Kuma Sun fadi Cewa, Wannan hujewar barazana ce ga lafiyar 'yan Adam din dake rayuwa a wannan duniya musamman sassan duniyar dake fama da yanayin zafin rana. Domin ana samun karin sabbin cututtukan da suke da alaka da fata masu Wuyar magani.

Wannan abu hakika ya fara tabbatuwa domin kuwa a watan juli din wannan shekara ta 2016 (Wato July 2006), a North America an samu mutuwar a kalla mutane 225. Wanda kuma duka bincike ya tabbatar da cewa, dukansu sun samu cutukkane ta dalilin yawan zafin rana.

Haka Wannan Annoba ta mace-mace da rashin lafiya ta yawaita a Wani kauye dake Cikin Erteria In da kusan Sai da 'yan kauyen Suka yanke kauna da rayuwa. Kwatsam kuma Sai gashi Wannan Annoba ta Rashin Lafiya da Mace-mace Sun yawaita a Cikin Tsakiyar Garin Sokoto In da a Rana 'daya zakaji an Rasa fiye da Mutum 50. Babu Shakka Annoba Jarabawa Ce Da Allah Ke yiwa Bayinsa Ko dai don Ya Jarabesu ko Kuma don Gargadesu akan Su tuba daga miyagun laifuka.

....Subhanallah!!!
Jamilu Sani Rarah Sokoto
Wed 26/10/2016

Wednesday, 12 October 2016

ME YA FARU A RANAR 10 GA WATAN AL-MUHARRAM.

ME YA FARU A RANAR 10 GA WATAN AL-MUHARRAM.
*******
A Rana mai kamar ta yau ne, Ranar Goma Ga Watan Al-Muharram aka Kashe Jikan Annabi (Saww) wato Sayyidin Husaini (Rta). Sayyidina Husaini (Rta) An haife shi shekara daya bayan haihuwar wansa wato Sayyidina Hassan (rta), Dukansu suna da kama da Manzon Allah (Saww) daga cibiya har ya zuwa qasa. Annabi (Saww) ne ya sanya masa suna Hussaini.

Sayyidina Husain ya yi shada a ranar 10 ga watan Muharram a Karbala. Sakamakon rikici da ya faru a lokacin Mulkin Yazidu dan Sayyidina Mu'awiya. Sayyidina Husaini da Abdullahi bin Zubayr dukansu basu yarda da jagorancin Yazidu dan Mu'awiya ba. Dalilin Kin yardarsu da Mulkin kuwa lokacin da Sayyidina Mu'awiya (rta) yake kan Shugabanci, Sai ya bar Wasiyar Cewa, idan har Allah ya karbi ransa a bawa 'dansa Yazidu mulki.

Wannan dalili shiyasa Sayyidina Husaini Jikan Manzon Allah (saww) da Abdullahi bin Zubayr Jikan Sayyidina Abubakar (rta) suka ki amincewa da mulkin Yazidu. Saboda a ka'idar Mulkin musulunci a wancen zamani ba zaka ce a idan ka mutu a bawa danka ba sai dai su musulmi su zabi mutane masu daraja suyi musu kuri'ah duk wanda Allah ya bawa shikenan.

 Bayan Wannan abu ya faru Sai Sayyidina Husaini (rta) ya bar Madina ya koma makka da zama shi da Abdullahi bin Zubayr. Bayan An kashe Abdullahi bin Zubayr a Makka Sai ‘yan Shia daga kufa suka aiko masa wasika akan ya zo za su yi mashi mubaya’a. Sai Sayyidina Husaini (rta) ya tura 'dan uwansa Muslim ibn Aqeel akan yaje Kufa ya dubo masa shi wayannan wasikun da gaske ne ko kuwa karya ne.

 Daga nan sai Muslim ibn Aqeel yaje Kufa suka yi masa tarba ta arziki suka nuna masa ai da gaske ne su zasu taimaki Sayyidina Husaini (rta), nan take Muslim ibn Aqeel ya turawa da Sayyidina Husaini da Wasika akan yazo babu shakka da gaske suke akan zasu yi masa mubaya'a.

Da ya zo sai ya gane yaudaran sa suka yi, bai ga kowa ba sai rundinar UbaidulLahi ibn Ziyad.
A ranar 9 gawatan Muharram sayyidina Hussaini ya ce wa jama’arsa gobe akwai yaqi tsakani na da gwabnan Kufa duk mai son komawa gida ya bi dare ya tafi.

Rundunar gwabnan Kufa su 4000 shi ko sayyidina Hussaini ‘yan rakiyarsa 72, gari na waye wa sai yaqi ya barke, aka fafata aka fafutuka sahabi Hussaini ya nuna barde ne domin ya kashe jama’a masu yawa kafin yayi shahada. Ana cikin Wannan yakin ne Wani 'dan Shi'a mai suna Zur’atut Tamimi ya fara saransa a kafada daga nan sai Sinanu dan Annas wanda shima 'dan Shi'a ne ya soke shi da mashi a maqogwaronsa ya kuma qara cakansa da mashin a qirginsa.

kafin Sahabi Hussaini ya kai qasa sai Khuli al-Asbahi (La'anannen Allah) ya sa takobi ya sare kan sahabi Hussaini.(Ya Allah kar ka kai rahama ga wadannan mutanan da suka kashe sahabi Hussaini Ya Allah ka tabbatar da la’antarKa ga wadan da suka kashe Hussaini). Kafin a kashe sahabi Hussaini
ya nuna jarunta matuqa. Wannan yaqin ya faru ne bayan mutuwar sahabi Muawiyya da shekara biyu shi kuma Yazidu dan Sayyidina Muawiyya yana Sham. Bayan sun sare kansa sai suka Dauki kan sayyidina Hussaini suka tafi da shi Sham daga baya aka kai kan Sayyidina Hussaini a Madina aka rufe shi bayan kusan sati da faruwan yaqin. Ya Allah ka qara aminci ga jikan Annabinka ya Allah Ka qara daukaka darajansa amin.

'Yan Shi'a sun dauki ranar goma ga watan Muharram rana ce ta baqin ciki saboda a wannan ranar
ce a ka kashe jikan Annabi (Saww) a yaqin Karbala, wato Sayidna Hussaini (rta) wanda kuma Alhali sune suka kashe-shi da kansu. In da zaka kara gano 'yan Shi'a Munafukaine a Ranar ta goma ga watan Al-Muharram din da aka kashe Sayyidina Husaini hakama qannansa Abubakar da Umar da Usaman dukkan su ‘ya ‘ya ne ga sayyidina Aliyu (rta).

Amma abin ban mamaki ‘Yan Shi’a basa baqin ciki sauran yaran, sai Sayyidina Hussaini (rta) kawai
Allah sarki wannan zai ka qara fahitar damu cewa tsakanin sayyidina Aliyu (rta) da sauranan sahabai duk daya ne, tun da ga shi har yasa sunanayen sahabai Abubakar da Umar da Usman kuma tarihi ya tabbatar da cewa su ‘yan Shia da kansu su ka kashe Sayyidina Hussain A duba a littafin Shi’a Muntahal A’amal1 Shafi na 450 da I’ilamul wara na dabaris Shafi na 203 da Maqtalu Hussain shafi na 147 da Ma’alimi Madaratina shafi na 62 da kitabul Raudha dukkanin wadannan littafan na masu bi addini Shia ne da kansu su ka fada cewa 'Yan Shia ne su kashe Hussain bayan sun aika ma sa da wasiqu ya zo suyi masa mubaya’a, amma kuma suke baqin ciki na yaudara.

 Haka kuma Za'a iya Dubawa a Cikin Littafen Imamu Zahabi Mai Suna Siyar A'alamun Nubla. Sai mutum ya duba tarihin Sayyidina Aliyu, Dana Mu'awiya dana Sayyidina Husaini In shaa Allahu zaka fahimci makircin Shi'ah.

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Wed 12/10/2016

Tuesday, 2 August 2016

TARIHIN DAULAR MUSLINCHI TA ANDALUS 2

TARIHIN DAULAR MUSLUNCI TA ANDALUS (Spain) Fitowa ta 2
*******************************************************


Ga wayanda Basu samu damar karanta Fitowa ta Farko ba Su latsa nan domin karantawa; jamilrara.blogspot.com/…/…/tarihin-kasar-andalus-spain.html…

Ci Gaban Tarihin;

Kasar Andalus Sai da ta Shekara 800 a cikin musulunci kuma daular musulunci. Amma a Ranar da Yahudawa sunka saka Andalus a gaba sai da wannnan kasa ta fita daga hannun Musulmi (ta tashi daga daular musulunci).

kasan cewa duka ka'idodin musulunci da ake bi a kasar da kewaye har sai da ta kai kafirai basa sha'awan shiga kasar, amma randa yahudawa suka bulla a kasar ba'a dauki shekaru 50 ba saida suka juyar da musuluncin. sunka rushe duk wani abu na musulunci akasar suka cenja Sunayen garin (daga na musulunci zuwa nasu na kafirci).

Har sai da ta kai ta kawo Gaba daya kasar ba'a yarda ayi addinin musulunci ba.
Babban abinda ya kawo haka a kasar kuwa rashin hadin kan da yahudawa suka sanya a tsakanin 'yan kasar. Wato babu hadin kai tsakanin kiristoci na asali da musulman da aka tilasta masu shiga adinin kirista. Haka ma tsakanin musulmin su kansu babu hadin kai.

To daga nan Sai tattalin arzikin kasar ya rika fadawa cikin nakaso da samun matsala tare da tabarbarewa.
Sakamakon ganin Tattalin Arzikin na tabarbarewa sai aka yi wani zaman tattaunawa (Metting) a Ingila don idan har aka bari tattalin arzikin kasar yana rushewa to mutanan kasar zasu watsar da kiristiyaniti zasu koma musulmai.

A zaman tattaunawar ne sunka yanke shawarar cewa za'a kirkiro da wani abu wanda zai hada kan 'yan kasar. A cikin tattaunawar akayi ta kawo abubuwan da ake ganin zasu karbu ga musulmi da kafirai amma duk wanda aka kawo aga bayayi. Anan ne wani ya bada shawara akan a kirkiro da gasar kwallon kafa a kasar domin zata karbu (musamman ga matasa musulmi da Kirista).

To anan ne aka kirkiro da kwallon kafa akasar ta spain. Wannan ne yasa aka debi dalibai akaje dasu kasar Ingila aka karantar dasu kwallon kafa da dabarunta tare da yanda zasu sanyawa mutane Sha'awarta.
Bayan sun kware sai aka turosu kasar ta spain don su karantar da matasan kasar kwallon ta kafa.
Anan ne aka kirkiro da wani kulob na kwallon kafa mai suna sevilla (Wanda asalin sunan wani garine na musulunci da ke cikin kasar ta Spain mai suna Ishbiliya).

Sevilla shine kulob na farko da aka kirkiro akasar ta Spain. (Wannan yafaru ne a shekarar 1890 zuwa 1899). daga baya aka kirkiro da spanish king cup. Wato copa del ray, Shi wannan kofin an kirkiroshi ne wajan bikin bada sanda ga sarkin kasar.

Haka a Shekarar 1905 aka samar da kulob din real madrid. sai kum kulob din Barcalona Sai Espenyol da ganan sai visaya. Wayannan kulob kulob din su sunka maye madadin musulunci a kasar. har sai da ya kasance musulmi yafi son kirista dan kulob dinsu da musulmi wanda ba dan kulob dinsu ba.

Haka sarkin spain mai suna king alfanso yace suna da wata kalma ta kiristoci wadda su sunka san sirrin dake cikinta (Wannan kalmar).kalmar tana da wani sirri.wanda sai dan kungiyar yahudawa yasan sirrinta.
Wannan kalmar itace real. wannan kalmar sarkin ya bada ita a shekarar 1927 yace duk kulob din dake son kalmar ya dauki wannan kalmar yabashi aronta.

Nan take kulob fiye da 10 sunka dauketa anan ne anka samu real zaragoza wanda ainihin sunan garin musulunci ne wanda ake kira saraqusda.

Sai Real betis, Real soceida, Real valadolid wanda shima asalin sunan garin musulunci ne mai suna valadu walid, Sai Real murcia, Real union, Real sporting gijon sai Real madrid. (In shaa Allahu zan kawo bayanin ma'anar Real anan gaba).

Haka ma a can baya akwai wani bayahude makiyin musulunci na gaske wanda yana cikin wayanda sunka yaki musulunci akasar ta Spain sunan sa santiago to shine aka sakama stadium din Real Madrid domin Girmamawa gareshi da girmama kwazonsa.

To ta hakane akaci musulunci da yaki akasar. yanzu yawan musulmai akasar ta spain akalla akwai musulmai dubu 500 kacal. Yayin da mutanan kasar kuma yawansu ya kai miliyan 36. wanda tarihi ya nuna kasar ta spain tayi zama kashi 95 cikin 100 musulmai ne kamar yadda na fada a baya
Kuma a cikin yawan musulmin a kasar dubu 500 to dubu 400 ba ainahin 'yan kasar bane bakine (wato ba yan asalin kasar bane).

Daga cikin Musulmi Mutum Dubu 100 kacal sune 'yan kasa. cikin dubu 100 din mutum dubu 20 sabbin musulmai ne dubu 80 ne kawai tsofaffin musulmai. Hakika da kwallo aka Shiga Kasar Spain aka Karya Kashin gadon bayan Musulunci a kasar ta Spain. Kuma dama yahudawa sunce kwallo addini ne mai zaman kanshi. kuma duk wanda ya shiga cikinta yau da gobe sai ya aje addininshi ya rungumeta don zai samu tarin kudin da ba zai iya samun kwatan-kwacinsu a addininsa ba. Haka kuma zai kashe mata kuddin da ba zai iya kashewa a addininsa ba. Kuma Zai bada lokacinsa lokacin da bazai iya ba addininsa ba.
Akwai wata waka da akayi a 2008 mai suna "Football is religion". haka ma shugaban fifa a lokacin Sep Blater yace Football is more than sport is a religing.

Kuma Wannan Gadkiya ne Saboda kiyasin da akayi a akwai masu sha'awar kwallon kafa sama da mutum biliyan 5. Yayin da yawan mutanan duniya gaba daya biliyan 7 ne. yayin da musulmai yawan mu be kai biliyan 2 ba. kunga masu kwallo da sha'awarta sun lunka yawan musulmai aduniya. Haka yanzu yan kwallo sune masu kudi a duniya.

Dan wasan Real madrid duk minti yana amsar sama da naira dubu 9 koda yana baccine. A duniya Bayan Bill gate 'dan Kasar America da yafi kowa Kuddi a duniya Sai Mutumen Spain mai suna Amancio Ortega shine na Biyu da kuddi a duniya wannan mutumen a talaka ya tashi amma ta dalilin yin tufafe wa 'yan kallo yanzu ya zama shine yafi kowa kuddi a kasar ta Spain kuma shine mai kuddi na biyu a duniya. (Shima zuwa gaba zan kawo tarihinsa da kuma yanda ya samu kuddinsa In shaa Allahu).

Mutane da yawa suna tambayar wai ina kulob kulob din nan ke samun wayannan makuddan kudade ne?
Watakila in na samu dama nan gaba zan kawo bayanai game da haka tare da kawo mutu wasu abubuwan da suka Shafi Daular musulunci ta kasar Andalus (Spain a yanzu In shaa Allahu).

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Mon 25/07/2016.

SOYAYYAH DA DADI

SOYAYYA DA DADI GA MA IYANTA
********************************

Wata Mata Ce ta yanke Shawarar tsokanar mijinta akan ta gwada shi ta gani ko yanda yake sonta
Wata Rana ya fita aiki, Cen kusan lokacin da zai dawo sai ta Janyo Biro da takarda ta fara rubutu kamar haka; "BA ZAN IYA YI MAKA SALLAMA BA A CIKIN WANNAN RUBUTUN, SABODA RAINA A BACE, KAI TSAYE INA SON IN GAYA MA NE CEWA, NI NA GAJI DA ZAMA DA KAI KUMA DAGA YAU BA ZAKA SAKE GANI NA BA, INA FATAN ZAKA CIRE NI DAGA RANKA"

Bayan ta gama Sai ta nemi Wuri ta zauna tana jiran Isowarsa, Cen Sai taji Sallamar Sa ya Shigo gidan.
Ta ajiye takardar a kan gado, Tayi maza ta buya a bayan dirowa a cikin dakin domin taga yanda zai yi idan ya karanta wannan takarda.

Ya shigo falo yayi Sallama amma shiru ba kowa (ba'a amsa ba), kai tsaye ya shiga cikin daki.
Anan ma yayi Sallama amma shiru ba'a amsa ba, Sai takarda da Biron da ya hanga saman Gado.
Ya dauki takardar ya karanta tsaf. Cikin farin cikin ya dauko wayarsa daga Aljihu ya latsa kiran wata number. Cen sai yace; "Hello my Sweet heart. Albishirinki matata ta tafiyarta yanzu ke ga mun huta da boyo don haka yanzu ma ki shirya gani nan zuwa in dauki ki." Bayan ya gama wayar ya ajiye wayar. Sai yace, kai Yau gaskiya ina cikin farin ciki da annashuwa, bari ma in dan taka rawa. Anan yayi rawa bayan ya gama sai ya juya takardar yayi wani rubutu akai.

Daga nan sai ya kama hanya ya fita ya bar dakin. Wannan mata cikin tsananin kishi da jin haushi ta fito daga in da ta buya. Tayi Sauri don ta same shi amma ina ya riga yayi nisa har ya bar gidan. Sai tace; "Ai kuwa yau ana yin ta domin sai nayi maganin wannan shegiyar karuwa."

Nan take ta dauko karamar tukunya ta zuba ruwa ta daura ruwan zafi. Tazo daki ta zauna tana cika da batsewa. Cen Sai ta tuna da ai taga yayi rubutu a takardar cen ta janyo takardar ta fara karanta rubutun da yayi akan takardar. "NI BARI IN FARA DA YI MIKI SALLAMA ASSALAMU ALAIKUM, AI NA GANKI KIN BUYA A BAYAN DIROWA KUMA KO BAN GANKI BA NA SAN KINA NAN A BOYE DOMIN KAMSHIN TURARENKI MA BA ZAI BARKI KI BUYA BA."
"DON HAKA NI DAI NA TAFI NA SAYO BURODI DA FATAN KAFIN IN DAWO KI DAURA RUWAN ZAFI DOMIN YUNWA NAKE JI. NA BARKA LAFIYA SAI NA DAWO MATATA ABIN ALFHARINA."

Jamilu Sani Rarah Yace; Kenan Ruwan da aka daura domin antayawa wacce zata shigo, Buredi Za'a antayawa su. Hahahah.

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Sun 17/07/2016

ME YASA AKE SON AYI JUYIN MULKI A TURKIYA?

ME YASA AKE SON AYI JUYIN MULKI A TURKIYA?
**********************************************

Tayyip Erdogan Shine Prime Ministan Kasar ta Turkiya tun Shekarar 2002 ko kuma 2003, Tayyip ya kasance Musulmi mai son Ci gaban musulunci da Musulmi a kasar ta Turkiya.
Babu Shakka kasar turkiya kasace ta Musulunci, amma a gaskiya wasu musulmin kasar a yanzu basa kula da hakkokin musulunci.

Idan nace basa kula da hakkokin Musulunci Ina nufin, wasunsu basa bin koyarwar ta addinin musulunci.
Domin wani marubucin Kafiri 'dan kasar ta turkiya ya taba rubuta wa a cikin Littafensa Cewa, "Da ace yanda musulmin Turkiya suke haka Sauran Al-ummar musulmin duniya suke da an zauna lafiya a Duniya."
Dalilin da yasa ya fadi haka kuwa shine, Musulmin Turkiya zai iya jan Kafiri su je cikin masallachi suyi fira har da kyakkewa, wanda ni a ganina sam ba koyarwar addinin musulunchi bace.

Wannan shiyasa ma wasu daga cikin kafirrai basa daukar wasu daga cikin musulmin turkiya na yanzu a matsayin musulmi. Amma zaman Tayyip Shugaban kasa a Shekarar 2013 sai ya fara sauya halin musulmin kasar izuwa turbar Addinin musulunchi.

Daga cikin wannan juyarwa akwai lokacin Majalisar Dinkin duniya suka bada umurnin fara yin tsarin hana haihuwa a kasar. Daga jin haka nan take Tayyip ya fito a kafafen watsa labarai yake cewa; "Daga yau daga Rana mai kamar ta yau kada gidan musulmin da naji ance suna amfani da tsarin kayyade Iyali."
"Hakika addinin musulunci yana bukatar al'umma masu yawan gaske don haka kada wata macce ta kuskura ta ajiye haihuwa ba tare da dalilin musulunci ba". "Musulmi dole ne mu bi Allah da Manzonsa domin Annabin mu Mai girma yace, Mu haifafa domin yayi alfhari damu."

Baya ga wannan Shugaba Tayyip na daga cikin Shugabanin da basa tsoron Isra'il hasalima adawarsa a garesu tafi ta sauran shuwagaanni tsanani. Ko wane taro ake yi ko mai muhimmancin taron idan lokacin Sallah yayi Tayyip yakan Fita yaje yayi Sallah. Haka ma akwai wani 'dan majalisarsa mai suna Huseyin Sahin yake Cewa, "Mu musulmi hakika Shugaba Tayyip ya zamar mana wani babban Jigo domin duk zaman da muke idan lokacin Sallah yayi yakan tashi tare da umurtarmu mu je muma muyi sallah."

Tayyip Erdogan shugaba ne adili mai son Ci gaban kasarsa da addinin musulunchi don haka yana da kyau taya shi addu'ah ta samun cikakken samun kariya daga makiya masu son hanbarar da Mulkinsa.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 16/07/2016

DAB PICTURE SAI MAHAUKACI KO DABBA

DAB PICTURE SAI MAHAUKACI KO JAKI
******
Hausawa Suna karin Magna Suka Ce, "Idan Baka San Gari Ba Saurari daka." Ga dai abinda wasu turawa ke cewa game da "Dab Dance" ko "Dab Picture."

BOO WOO Yace; "Dab hanya Ce da Mashaya tabar Iblees (Wiwi) ke amfani da Ita a duk lokacin da Kwakwalwarsu ta karbi mayen tabar ta (marjuana)."

AVANT Yace; "Naje hutun karshen sati a calfonia, ina cen Sai Matata ta turomin fiye da photo guda ashirin (20 pic) na kanwarta tayi Irin daukar Wannan photo, Sai nace da matata, itama tana daga Cikin wayanda Ibless ke juya tunaninsu?"

J.ZAY Yace; "Mu Iblees ne ya bamu daukaka da Arziki da dukiya kuma shi ke karemu don haka dole ne Muyi dab a gareshi"

CAM NEWTON Yace; "Idan har ba zamu yi Dab zuwa ga Ibless ba ai mun nuna bama son Gode masa."

MIGOS Yace; "A rayuwata Iblees ya bani komai shi yasa na kirkiro da yanda zan gode masa, amma ba da nufin wasu su kwaikwaya daga gareni"

Zaku Iya Bincika wa a nan bossip.com/1260484/bow-wow-dab-origin/
Ni kuma Nace; Duk Wanda Ya san da cewa dab dance ko Picture Bautar Ibless ce kuma Yaci gaba da yi babu Shakka Zai hadu da hasara da tabewa duniya da lahira.
Hakika duk lokacin da kayi wannan dab din to kana yiwa Ibless Sujada ne, kuma sanin kowa ne ya dauki alkawari tun Wajen Allah (Swt) akan Cewa, Sai ya batar 'yan Adam.
Da Fatan Zamu Sanarda 'yan Uwan mu game da Wannan matsala da kuma kalaman da su wayannan mutane da suka kawo wannan dabi'a suka ce.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Thu 14/07/2016

Monday, 11 July 2016

GYARAN MOTAR MALAM AUDU



WAJEN NEMAN GIRA AN RASA IDO. GYARAN MOTAR MAL AUDU.
***********************************************************
****
Gidansu malam Audu gidane na talakawa, Gidane da basu mallaki komai ba face tufan sanyawa, gidane da basu da wani abu da zasu nuna su yi bugun gaba da shi.

Gidan na su Malam Audu ya tara mutane maza da mata (kama daga kananan yara matasa, budare da zawarawa).

Ganin irin talaucin da Su malam Audu da yayyansa da kannensa suke ciki ya sa Alh. Musa (wani makwafcinsu malam Audu). Ya sayi sabuwar mota ya ba su malam Audu domin su rika yin jigilar mutane gari-gari domin su samu kuddin da zasu rika ciyarda kansu da tufantarda 'ya'yansu.

Bayan su malam Audu sun karbo motar suka zauna domin a tsara yanda abin zai kasance. A gidan akwai dakuna guda ukku ne.

Dakinsu Mal. Audu sun kasance Su biyar ne macce ukku da kuma yayan Malam Audu wato Idi sai malam Audu din.

Sai daki na biyu mai dauke da Mutane 4 Namiji biyu macce biyu. Daki da ukku kuma duka maza ne.

Bayan an zauna anyi shawarar za'a rika yin karba-karba na tsawon Shekara daya-daya. Idan ta shekara hannun wannan ta shekara hannun wancen.

Duk wanda yake shi zai rika ciyarda yaran da kuma tufatan dasu. Haka kuwa akayi kowa ya rika yana yin nashi kokari amma Mal. AUDU kullum fadin yake yayyen nan nasa basa yin dai-dai.

Akwana a tsahi mota tayi shekara ukku, yanzu lokacine da za'a bawa Malam Audu mota domin shima ya Taimakawa gida da wannan motar.

Mazan gidansu Malam Audu dama sun dade suna son suga wannan ranar domin suga irin kokarin da malam Audu zaiyi ganin yadda ake cewa basu yi abin azo a gabi ba.

Matan Gidan kuwa Sai Murna Suke ganin Cewa, Wanda Ke ta ganin ba'a kyautata musu mota ta kai hannunsa (Alhamdulillahi).

Ashe kai Malam Audu Motar da Ya Iya Automatic Ce ba Manual ba. Kuma gashi motar ta tsufa tana bukatar cenjen Tayoyi da Shokshovers.

Nan take aka bawa Malam Audu Makullin Mota domin ya kai ta Gareji a cenja wayannan abubuwa masu neman Cenji.

Malam Audu na Shiga Mota ya tarar da Ita Manual ba Automatic ba nan take ya rude tare da tunanin mafita. Yayi statar mota ta tashi nana take Qannensa mata Suka Hau sowa da tafi (matsalarsu tazo Qarshe).

Ai kuwa yana saka Giya Sai mota ta mutu (domin bai rike kuloch ba). Nan wasu suka fara tantamar ko dai malam Audu bai iya motar ba.

Da Malam Audu ya fahimci haka sai ya leko ta merrow Yace; "KADA FA KU MANTA SUN RIKA SUN TSUDAR DA MOTAR DUK TA LALACE", Malam Audu ya Sake tayar da Motar tare da Rike kulochi.

Allah ya bada sa'ah mota ta tashi Malam Audu ya fara tafiya da ita, amma fa idan tayi nan mota tayi cen (sai ya tabo karshen titi ya tabo karshen titi).

Yanzu dai mota na hannun Malam Audu ya kama hanyar wajen gyara ko dai yakai lafiya ko kuma motar ta ida lalacewa (Imma bai ture wasu suka mutum ba). Kar wajen neman gira a rasa Ido.

Jamilu Sani Rarah.
Sat 14/05/2016.

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI TARE DA BAYANIN SU.
***********************************************************
Wannan Rubutu da Zan Fara gabatarwa ba yana nufin yin Suka ga wata akida ba ko kuma nufin munana matsalar wata akida ba.

A'a rubutune da zai taimaka kwarai da gaske domin fahimtar kowacce akida da kuma tsare-tsaren ta da kuma banbancin ta da saura domin ganin An Samu fahimtar juna.

Yana da kyau mutum ya tsaya da kyau ya karanci wannan rubutun tare da fahimtarsa domin ganin an daina samun sabanin da ake samu a cikin musulmi.

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDININ DA KE AKWAI.

1. Izala.
2. Wahahiyyah.
3. Salafuyyah.
4. Diyobandiyya.
5. Bareliyya.
6. 'Yan Islama.
7. Kur'aniyyah.
8. Shi'ah.
9. Shi'ah Ashriyyah.
10. Shi'ah Nizariyyah.
11. Shi'ah Musta'aliyyah
12. Shi'ah Shi'ah Alebiyyah.
13. Shaykiyyah.
14. Shi'ah Usuliyyah.
15. Shi'ah Akhbariyyah.
16. Shi'ah Isma'iliyyah.
17. Shi'ah Zaidiyyah.
18. Sufanci.
19. Darika.
20. Darikar Kadiriyyah.
21. Nasiriyyah-Kaduriyyah.
22. Tijjaniyyah.
23. Ibrahimiyyah-Tijjaniyyah.
24. Chishtiyyah
25. Suhrawardiyyah.
26. Bektashiyyah.
27. Nakshibandiyya.
28. Uwaisiyyah.
29. Mu'utazilawa.
30. Kalamanci.
31. Kadiriyyah.
32. Jabariyyah.
33. Ash'Ariyyah.
34. Maturidiyya.
35. Athariyyah.
36. Murjiyyah.
37. Khwarij.
38. Ibadiyya.
39. Surfriyya.

Abin da Zamu lura da shi anan shine, Kowacce kungiyya a cikin wadannan kungiyoyi dana zayyano suna da magoya baya dai-dai nasu, kuma addinin da kowacce cikinsu ke taqama da shi shine musulunci.

Musulunci kuma shine tafarki madaidaici wato addinin da Allah ya ambace shi da addini.

Allah (Swt) a Cikin Suratul Al'imran yana Cewa; "LALLE NE ADDINI A WURIN ALLAH, SHINE MUSULUNCI" (suratul Al'Imaran Aya ta 19).

Kowane daga cikin wayannan kungiyoyin yana ikrari ne akan cewa, shi mabiyin addinin Islama ne. In shaa Allahu kowannensu zan kokarta kawo bayannan su tare da hujjojinsu domin kokarin fadintar sabanin da yake tsakani.

Jamilu Sani Rarah
Fri 13/05/2016.

YA ZAMU KOYAWA 'YA'YAN MU SALLAH?



YA ZAMU KOYAWA 'YA'YAN MU SALLAH?
*************************************

'Ya ta Shekaranta 12 amma sallah ta zamar mata kamar wasu kaya a ka (domin duk yanda nayi da ita bata yin Sallah).

Wata Rana na Umurce ta da taje tayi Sallah. Na tsura mata ido har ta tafi taje ta dau sallaya ta shiga 'daki bata yi wani dogon dadewa ba ta fito a zuwan tayi sallah din amma ni na san bata yi sallar ba.

Na tambayeta ko ta gabatar da Sallar ta kuwa? Ta amsa min da "Eh", amma ni na san bata yi sallar ba. Cikin tsananin fushi na wanke ta da mari har sai da ta kife a kasa.

Daga baya kuma sai tausayin ta ya kamani, amma ba yanda zanyi domin saboda na gaji da halinta (na rashin yin Sallah). Nayi nadamar marinta da nayi na dauki alkawarin ba zan kara marin ta haka ba.Domin na san wannan ba zai amfani 'yata da komai ba.

Wata rana wata Qawata ta gaya min Cewa, takai ziyara wajen wata Qawarta, kuma Qawarta ta ba wata mai kula da addini ba ce sosai, amma a duk lokacin da aka kira sallah takan lura da 'ya'yan Qawartata sukan yi sauri su ta shi suje Sallah ba tare da an tsawatar musu ko tunatar musu ba.

Qawar tawa taci gaba da gayamin cewa, tayi mamaki kwarai a lokacin da ta ga yanda yaran nan ke lura tare da kula da Sallah. Sai ta tabbayi Qawartata Cewa, "Ko me yasa na ga yaranki daga zarar an kirayi sallah suke tashi ba tare da ke tsawatar musu ba?"

"Sirrin abin tun kafin Inyi aure na kasance Ina karanta Wannan addu'ar kowace rana kuma har yau ban daina karantawa ba". Haka ta gayawa Qawata.

Qawar tawa ta bani shawarar ni ma idan ina son 'ya'yana su kasance haka to nima In dukufa wajen karanta wannan addu'ar a koyaushe.

Tun lokacin da na dukufa wajen karanta wannan addu'ar 'yata ita ce ta farko wajen gabatar da sallah a gidan mu ba tare da an tsawatar mata ba.

Takan kuma tashi sallar asuba ba tare da ta saka alam ba. Haka ma duka 'yan uwanta da aka haifa daga baya suna sallah a lokaci.

Har ma dai aka kai itace ke tayar da mu sallar asuba kuma ita ke gaya mana lokacin sallah idan yayi Na san kun Matsu kuji Wace addu'ah ce nake karantawa to aya ta 40 ce a cikin Suratul Ibraheem
ِ
Wato, "Rabbi-Ajal'ni muqeema salaati, wa min Dhurriyyati, rabbana wataqabbal duaa" Hakika duka baya shiryar da 'ya'ya addu'ah ce ke shiryar dasu. Da fatan za'ah rika karanta wannan ayar da niya.

Jamilu Sani Rarah
Thu 19/05/2016


SABODA ME ZAMU KARANTA AL-QUR'ANI ALHALI BAMA JIN LARABCI?



SABODA ME ZAMU KARANTA AL-QUR'ANI ALHALI BAMA JIN LARABCI?
******************************************************************
***
Ina mamakin yadda kakana a koda yaushe yake kokarin Karatul Al-Qur'ani alhali baya jin abinda ake fadi (ma'ana baya jin Larabci).

Kamar kullum safe da rana da dare yake wannan karatu na al-qur'ani, yau dai da rana ne ya zauna yana karanta al-qur'anin sai gani nazo.

Abin nema ya samo dama ina bukatar in ganshi yana karanta wannan al-qur'ani domin in tambayesa dalilinsa na karanta al-qur'ani alhali baya jin larabci.

Na samu wuri na zauna ina jiransa domin ya kai aya muyi magana. Na zauna har tsawon mintuna 2 sannan daga baya ya tsayar da karatun da yake yi.

Nace dashi, Ya kai mahaifin babana akoda yaushe ina so inyi maka wata tambaya ce amma ban samu dama ba sai yau, Allah yasa zaka amsa min wannan tambayar tawa ba tare da kaji haushina ba.

Ya girgiza kai yayi min ishara da hannu da cewa in fadi tambayar yana jina. Nan sai na fara da cewa, "Naga kai ba balarabe ba, kuma kai ba Malami ba, kuma kai ba wanda ya zauna kasashen larabawa ba, hasalima kasashen turawa kayi karatun ka amma me yasa a kullum kake kokarin karanta Al-qur'ani Alhali baka jin yaren Larabci?"

Kakana ya nisa ya danyi tari, uhuk! uhuk! Sannan ya dubeni ya sake dubin gefensa na hagu sai ya dubi wani kwando (ga alama anyi aikin laka) da kwandon domin duka laka ya bata shi.

Sai yace dani, "Dauki wancen kwando je ka debomin ruwa a rijiya" taya yaya kwando zai iya diban ruwa? Nace da kakan nawa.

Kakana Yace dani, In shaa Allahu zai debo je kawai ka debo ruwan a cikin kwando. Ba tare da bata lokaci ba na tashi na dauki kwando na je rijiya na yi ta zuba ruwa a cikin kwandon amma dana zuba da ruwan sun zube a kasa.

Na zuba ruwan yafi a kirga amma da na zuba suke zubewa, nayi nayi har na gaji. Sai na dauki wannan kwandon naje na kaiwa kakana nace da shi, wallahi kwando ba zai iya debo ruwa ba amma idan ruwan kake so da gaske to bani wani abu (wanda ba kwando ba) inje in debo ma ruwan.

Kakana yace, a'a ni a kwando nake so kaje ka debomin ruwan. Anan na nuna masa kwando fa ba zai debo ruwa ba, amma ya matsamin akan sai naje na debo. A hakan na hakura na koma rijiyar domin debo ruwan a karshe dai na dawo ba tare da na debo ruwan ba. Saboda duk sa'adda na zuba ruwa a cikin kwandon zubewa sukeyi a kasa.

Bayan na dawo kakan nawa yace dani, har yanzu ka kasa debo ruwan ne? Nace masa, Eh bazasu debu ba. Sai yace dani, To shikenan amma dubi kwandon ka gani haka kaje dashi wajen debo ruwan?

Na dubi kwandon da kyau sai na ganshi yayi haske duk wannan lakar da ke manne a jikinsa ta debe kuma kwandon ya kara kyau, saboda wannan hasken da yayi.

Sai kakana Yace, TO HAKA AL-QUR'ANI YAKE A DUK LOKACIN DA KA KARANTA SHI KO BAKA JIN ABINDA AKE FADI TO ZUCIYARKA ZATA WANKE FES (Idan kana karantashi zai wanke ma daukar Hassada, Cuta, dasauran abubuwa).

Hakika tun daga ranannan na koma kamar Kakana Wajen Karanta Al-Qur'ani. Hakika naga fa'idar Karanta shi domin na kasance a cikin hassada da Kyashi kuma kullum nine gulma da sa'ido amma Cikin Ikon Allah duk na daina yin Wayannan abubuwan.

Jamilu Sani Rarah
Mon 23/05/2016.

LABARI MAI MA'ANAR GASKE


WANNAN WANI LABARI NE MAI BAN SHA'AWA NA WATA MATA MAI SUNA LAYLA 'YAR KASAR MOROCCO WADDA ALLAH YA JARABA DA CUTAR CANCER.

Likitoci sun taimaka matuka domin samarwa

da Wannan Mata Lafiya, amma Allah bai sa andace ba, hatta ita kanta Layla din ta debe tsammani daga Samun Waraka.

Ga abinda LAYLA ke cewa; Shekara tara Ina fama da Cutar Cancer duk wanda ya sanni ya san ina fama da wannan matsalar, kai hatta sunana aka fada Sai mutane sun tausaya min kasancewa Ina cikin wani hali na rai kwai-kwai mutu kwai-kwai.

Nayi tunanin in je in Kashe Kaina amma kuma tunanin irin hukuncin da zan tarar a Wajen Allah da kuma son da nake yiwa Mijina da 'ya'yana ya sanya dole na daina wannan tunani.

A lokacin da muka ziyarci Belgium, muje mun samu wasu likitoci game da matsala ta.

Shine suka gayawa Mijina Dole za'a debe nono na daya, sannan kuma zasu hadani da wasu maganguna.

Lokacin da suka bayyana mana sunan magungunan, sai naga ai da dadewa na taba amfani dasu.

Sukan sanya gashin kai na Zuba, sukan kuma sanya idona Fitar da kwantsa. Haka kuma sukan sanya Akaifun hannayena Kakkaryewa tare da sanya hakorana karyewa.

Kasan cewa, na san wannan maganungunan muka ki yarda da hakan. Na fiso in mutu da in koma amfani da wayannan magunguna.

Na buka ci likitocin da su cenja min magungunan saboda wayannan suna bani matsala, amma suka qi yarda da cenja min magungunan.

Na koma morocco in da likitana, Likitan nawa Ya bani Shawarar inje kasashen Yamma (Europe).

A Belgium akwai wani bala'i da suka tono min, domin kuwa likitocin sun gayawa mijina cewa, wannan Cutar ta shafi dukan Jikina Domin gaba daya wannan cutar ta mallake huhuna suka gayawa mijina babu wani abu da zasu iya akai don haka ya dauke ni ya mayar da ni Gida domin in mutu ko Allah yasa in mutu a cen.

A lokacin Mijina Ya Tsorata kwarai da gaske Amma mai makon mu koma gida morocco, Sai Muka Wuce faransa, a tunanin mu zamu samu mafita a cen (faransan).

Mu kaje Faransa amma babu wata mafita face irin Bayanin da muka samu a Belgium.

Daga Karshe sai muka yanke shawarar kawai a cire min Nonuwan in huta kamar yadda likitocin Belgium suka fada.

Muna cikin wannan tunanin ne kawai sai tunani ya fadowa Mijina "Hakika mun manta wanu abu guda wanda bamu damu da shi ba"

Na tambaye shi, "Menene?" "Bamu gaya wa Allah wannan Matsala taki ba" ya bani amsa.

Nan take mijina Ya Biya mana kuddin Visa da Taketi na jirgi na zuwa Saudiya (domin mukai kukan mu a dakin Allah).

Mu ka bar Paris "Allaho Akbar, La Ilaha Illa Allah" (Allah mai girma hakika babu sarki sai Allahh).

Nayi matukar farin ciki domin wannan shine farkon lokacin da zan yi tozali kuma in ziyarci dakin Allah.

Tun a paris na sayi Alqur'ani mai Girma abinda ban taba mallakarsa ba (na wa) a rayuwa ta.

Da shigar mu makka.. a lokacin da muka shiga masallachi tsarki, ai kuwa daga shiga ta ciki na fashe da kuka (kuka ba kadan ba).

Irin yanda naga an tsara wurin an qawata shi kuma na tuna da wurin da Annabi yayi Ibada kenan wuri mai falala da rahama shi yasan ya ni kuka.

Sannan a gefe daya ina kukan ne saboda ban taba fuskanta ko tunanin wannan wuri ba a rayuwa ta kuma ban taba rokon Allah ko tuna shi ba a shekarun baya.

Anan Nace, "Ya Allah! Kaine likitan likitocin da suka kasa warkar dani, duka kofofin samun waraka sun rufe min, banda wata mafita baya fa In rokeka, Ya Allah! Ya Allah! Kada ka rufe min kofar waraka".

Na ci gaba da kewayar dakin ka'aba ina rokon Allah akan Ka barni in koma hannu sake ba tare da na samu waraka daga gare shi ba.

Kamar yadda na fada a baya cewa, ni macce ce da bata da mu da harkokin musulunci ba, hasalima duk wani abu da ya jibanci musulunci kauyanci nake ganinsa.

Amma yau da kaina naje wajen wasu manyan malamai dake kasa mai tsarki ina neman taimako a garesu.

Suka bani shawara akan In je in rika karanta Alqur'ani Mai Girma, Sannan kuma suka bani shawarar in rika amfani da ruwan Zamzam.

Su Umurceni da In rika yin "Tadhalloo" kamar yadda suka kiransa da larabci ( Tadhalloo shine ka sha ruwan Zamzam Masu yawan gaske har sai ka ji ka koshi).

Sannan suka bani shawarar akan a duk lokacin da zan sha wannan ruwan in fadi sunan Allah tare da yin Salatin Annabi (Saww)

Suka bani tabbacin In shaa Allahu Idan har na Rika yin haka Allah zai bani Lafiya in dawo kamar kowa.

Anan na roki Mijina akan ya barni I zauna a Haram ba sai na koma Hotel ba l, mijina ya amince min akan in zauna a masallacin Haram shi ya koma a Hotel yaci gaba da zama.

A masallacin ne na hadu da wasu matan da suka zo daga Egypt da turkiya wayanda suka tausayamin a lokacin da nake yin kuka mai tsanani.

Suka tambayeni dalilin da yasa nake kuka, anan na sanar dasu duka labari na da kuma ciwon da ke tare da ni.

Allah Sarki basu gujeni ba suka zauna tare dani haka suma suka tambayi Izni daga mazansu akan su barsu domin su zauna a tare dani a masallaci.

A wannan zaman bama wani bacci kuma bama wani cin abinci mai yawa ko mai gina jiki, amma fa su ruwan zamzam mukan sha su da yawa har sai sun cika cikin mu.

Dama kuma Annabi (Saww) yace, duk wanda ya sha Ruwan Zamzam Allah zai warkar da shi idan har ya sha da niyar hakan.

A haka muka ci gaba da shan wannan ruwan muna rokon Allah kuma muna Dawafi tare da karatun Alqur'ani Mai girma. Wannan shine aikin mu safe da dare.

A lokacin da muka zo Dakin Allah babu shakka duka sassan Jikina yayi rauni sosai da sosai, domin Nonuwa na har fitar da Wasu ruwa masu wari hade da jini suke yi.

Saboda wannan kansar ta gama Illata min sassan Jiki na Duka.

To a lokacin cin Sai Wayannan Qawayen nawa suka Bani shawarar in rika wanke duka sassan jikin nawa da ruwan Zamzam. Ni kuma naki saboda ina tsoron Abinda zai iya biyowa baya domin ina gudun taba wannan Jikin nawa musamman Nonuwana.

Da ga farko na ki yarda da in rika wanke duka Jikina amma suka matsamin tare da takurani akan lalle sai na rika wanke jikina da ko wanka da wayannan Ruwan. A haka dole na bi shawarar su.

Na fara wanke Jikin nawa da wayannan Ruwa da farko na fara jin ciwo amma sai na daure na rika wanka da wayannan ruwan.

Cikin kwana Goma Sha Biyar da nayi Ina Wannan Wankan Na tarar da wani abu wanda sam nayi tunanin ba zai taba yiwuwa ba.

Domin ina taba Nonuwana na tarar babu jini babu Ciwo, nan da nan na bude duka sassan Jikin Nawa, domin ganin abin da ke faruwa da jikina.

Na tsarata kwarai da gaske ainun domin babu alama guda da zata tabbatar ma cewa nayi fama da Ciwo a Jikin nawa.

Nan na bude wa daya daga cikin Qawayen nawa jikina na Umurce ta da ta taba jikin nawa taji ai kuwa tana tabawa Dukan su Suka Dauki kabbara.

Allahu Akbar.. Allahu Akbar!! Na take na Arce da gudu na koma Hotel wajen Mijina.

Na Cira Rigata sama na Ce da shi, "Ka dubi taimakon Allah!" Anan na gaya masa duk abubuwan da suka faru da abinda kawayena suka sani in rika yi.

Nan take ya fashe da Kuka yace dani, "Shin ko ke san Likitoci sun Rantse da Allah akan nan da sati 3 zaki mutu akan wannan cutar?"

...Na Ce da shi; "Duka kaddara tana hannun Allah (Swt) babu wanda ya san abinda zai faru da wani face Allah Shi kadai.

Anan muka zauna har tsawon Sati daya, Na yiwa Mijina Godiya sosai da sosai abisa kokari da hakurin da yayi dani, su kuma wayannan kawayen nawa muka zama kamar Juna Ni da su.

Baya ga haka muka koma masallacin Annabi (Saww) da ke Madina. Daga nan muka wuce France.

A cen Lokacin da muka ziyarci Likitocin cen, duka wayannan likitocin suka Shiga mamaki tare da tambaya ta akan, 'Anya kuwa ke ce mai dauke da wannan Cuta?'

Cikin Izzan Na Ce da Su, YESS!! ..and this is my husband..we have
returned to God.. and I now fear nothing but Allah SWT.. (Ma'ana, Eh sannan kuma wannan Mijina ne mun koma nema ga Allah ne, Sannan yanzu babu wani abu da nake tsoro face Allah (SWT)).

Suka Ce Cuta ta babba Ce sosai da Sosai, Sannan Suka Sake Bukatar su sake yimin Gwaji.

Suka gwada amma basu tarar da wata matsala ba ko da ta Matsalar ciwon Kai Ce.

Bayan 'yan watanni na Samu "seerah" (tarihin Annabi (Saww) na rika karantawa da na shi da na sahabbansa (RA).

Hakika nayi Kuka kuma nayi da na sanin lokacin da na bata ba tare da kulawa da Wayannan Tarihin ba.

Hakika Na Yarda Cewa, Ruwan ZamZam Magani ne Makawar Ka sha da Niya kamar Yadda Hadisan Annabi (Saww) Suka Bayyana.

Jamilu Sani Rarah
Mon 13/06/2016.