Monday, 11 July 2016

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI TARE DA BAYANIN SU.
***********************************************************
Wannan Rubutu da Zan Fara gabatarwa ba yana nufin yin Suka ga wata akida ba ko kuma nufin munana matsalar wata akida ba.

A'a rubutune da zai taimaka kwarai da gaske domin fahimtar kowacce akida da kuma tsare-tsaren ta da kuma banbancin ta da saura domin ganin An Samu fahimtar juna.

Yana da kyau mutum ya tsaya da kyau ya karanci wannan rubutun tare da fahimtarsa domin ganin an daina samun sabanin da ake samu a cikin musulmi.

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDININ DA KE AKWAI.

1. Izala.
2. Wahahiyyah.
3. Salafuyyah.
4. Diyobandiyya.
5. Bareliyya.
6. 'Yan Islama.
7. Kur'aniyyah.
8. Shi'ah.
9. Shi'ah Ashriyyah.
10. Shi'ah Nizariyyah.
11. Shi'ah Musta'aliyyah
12. Shi'ah Shi'ah Alebiyyah.
13. Shaykiyyah.
14. Shi'ah Usuliyyah.
15. Shi'ah Akhbariyyah.
16. Shi'ah Isma'iliyyah.
17. Shi'ah Zaidiyyah.
18. Sufanci.
19. Darika.
20. Darikar Kadiriyyah.
21. Nasiriyyah-Kaduriyyah.
22. Tijjaniyyah.
23. Ibrahimiyyah-Tijjaniyyah.
24. Chishtiyyah
25. Suhrawardiyyah.
26. Bektashiyyah.
27. Nakshibandiyya.
28. Uwaisiyyah.
29. Mu'utazilawa.
30. Kalamanci.
31. Kadiriyyah.
32. Jabariyyah.
33. Ash'Ariyyah.
34. Maturidiyya.
35. Athariyyah.
36. Murjiyyah.
37. Khwarij.
38. Ibadiyya.
39. Surfriyya.

Abin da Zamu lura da shi anan shine, Kowacce kungiyya a cikin wadannan kungiyoyi dana zayyano suna da magoya baya dai-dai nasu, kuma addinin da kowacce cikinsu ke taqama da shi shine musulunci.

Musulunci kuma shine tafarki madaidaici wato addinin da Allah ya ambace shi da addini.

Allah (Swt) a Cikin Suratul Al'imran yana Cewa; "LALLE NE ADDINI A WURIN ALLAH, SHINE MUSULUNCI" (suratul Al'Imaran Aya ta 19).

Kowane daga cikin wayannan kungiyoyin yana ikrari ne akan cewa, shi mabiyin addinin Islama ne. In shaa Allahu kowannensu zan kokarta kawo bayannan su tare da hujjojinsu domin kokarin fadintar sabanin da yake tsakani.

Jamilu Sani Rarah
Fri 13/05/2016.

No comments:

Post a Comment