Monday, 11 July 2016

GYARAN MOTAR MALAM AUDU



WAJEN NEMAN GIRA AN RASA IDO. GYARAN MOTAR MAL AUDU.
***********************************************************
****
Gidansu malam Audu gidane na talakawa, Gidane da basu mallaki komai ba face tufan sanyawa, gidane da basu da wani abu da zasu nuna su yi bugun gaba da shi.

Gidan na su Malam Audu ya tara mutane maza da mata (kama daga kananan yara matasa, budare da zawarawa).

Ganin irin talaucin da Su malam Audu da yayyansa da kannensa suke ciki ya sa Alh. Musa (wani makwafcinsu malam Audu). Ya sayi sabuwar mota ya ba su malam Audu domin su rika yin jigilar mutane gari-gari domin su samu kuddin da zasu rika ciyarda kansu da tufantarda 'ya'yansu.

Bayan su malam Audu sun karbo motar suka zauna domin a tsara yanda abin zai kasance. A gidan akwai dakuna guda ukku ne.

Dakinsu Mal. Audu sun kasance Su biyar ne macce ukku da kuma yayan Malam Audu wato Idi sai malam Audu din.

Sai daki na biyu mai dauke da Mutane 4 Namiji biyu macce biyu. Daki da ukku kuma duka maza ne.

Bayan an zauna anyi shawarar za'a rika yin karba-karba na tsawon Shekara daya-daya. Idan ta shekara hannun wannan ta shekara hannun wancen.

Duk wanda yake shi zai rika ciyarda yaran da kuma tufatan dasu. Haka kuwa akayi kowa ya rika yana yin nashi kokari amma Mal. AUDU kullum fadin yake yayyen nan nasa basa yin dai-dai.

Akwana a tsahi mota tayi shekara ukku, yanzu lokacine da za'a bawa Malam Audu mota domin shima ya Taimakawa gida da wannan motar.

Mazan gidansu Malam Audu dama sun dade suna son suga wannan ranar domin suga irin kokarin da malam Audu zaiyi ganin yadda ake cewa basu yi abin azo a gabi ba.

Matan Gidan kuwa Sai Murna Suke ganin Cewa, Wanda Ke ta ganin ba'a kyautata musu mota ta kai hannunsa (Alhamdulillahi).

Ashe kai Malam Audu Motar da Ya Iya Automatic Ce ba Manual ba. Kuma gashi motar ta tsufa tana bukatar cenjen Tayoyi da Shokshovers.

Nan take aka bawa Malam Audu Makullin Mota domin ya kai ta Gareji a cenja wayannan abubuwa masu neman Cenji.

Malam Audu na Shiga Mota ya tarar da Ita Manual ba Automatic ba nan take ya rude tare da tunanin mafita. Yayi statar mota ta tashi nana take Qannensa mata Suka Hau sowa da tafi (matsalarsu tazo Qarshe).

Ai kuwa yana saka Giya Sai mota ta mutu (domin bai rike kuloch ba). Nan wasu suka fara tantamar ko dai malam Audu bai iya motar ba.

Da Malam Audu ya fahimci haka sai ya leko ta merrow Yace; "KADA FA KU MANTA SUN RIKA SUN TSUDAR DA MOTAR DUK TA LALACE", Malam Audu ya Sake tayar da Motar tare da Rike kulochi.

Allah ya bada sa'ah mota ta tashi Malam Audu ya fara tafiya da ita, amma fa idan tayi nan mota tayi cen (sai ya tabo karshen titi ya tabo karshen titi).

Yanzu dai mota na hannun Malam Audu ya kama hanyar wajen gyara ko dai yakai lafiya ko kuma motar ta ida lalacewa (Imma bai ture wasu suka mutum ba). Kar wajen neman gira a rasa Ido.

Jamilu Sani Rarah.
Sat 14/05/2016.

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDINI TARE DA BAYANIN SU.
***********************************************************
Wannan Rubutu da Zan Fara gabatarwa ba yana nufin yin Suka ga wata akida ba ko kuma nufin munana matsalar wata akida ba.

A'a rubutune da zai taimaka kwarai da gaske domin fahimtar kowacce akida da kuma tsare-tsaren ta da kuma banbancin ta da saura domin ganin An Samu fahimtar juna.

Yana da kyau mutum ya tsaya da kyau ya karanci wannan rubutun tare da fahimtarsa domin ganin an daina samun sabanin da ake samu a cikin musulmi.

KASHE-KASHEN KUNGIYOYIN ADDININ DA KE AKWAI.

1. Izala.
2. Wahahiyyah.
3. Salafuyyah.
4. Diyobandiyya.
5. Bareliyya.
6. 'Yan Islama.
7. Kur'aniyyah.
8. Shi'ah.
9. Shi'ah Ashriyyah.
10. Shi'ah Nizariyyah.
11. Shi'ah Musta'aliyyah
12. Shi'ah Shi'ah Alebiyyah.
13. Shaykiyyah.
14. Shi'ah Usuliyyah.
15. Shi'ah Akhbariyyah.
16. Shi'ah Isma'iliyyah.
17. Shi'ah Zaidiyyah.
18. Sufanci.
19. Darika.
20. Darikar Kadiriyyah.
21. Nasiriyyah-Kaduriyyah.
22. Tijjaniyyah.
23. Ibrahimiyyah-Tijjaniyyah.
24. Chishtiyyah
25. Suhrawardiyyah.
26. Bektashiyyah.
27. Nakshibandiyya.
28. Uwaisiyyah.
29. Mu'utazilawa.
30. Kalamanci.
31. Kadiriyyah.
32. Jabariyyah.
33. Ash'Ariyyah.
34. Maturidiyya.
35. Athariyyah.
36. Murjiyyah.
37. Khwarij.
38. Ibadiyya.
39. Surfriyya.

Abin da Zamu lura da shi anan shine, Kowacce kungiyya a cikin wadannan kungiyoyi dana zayyano suna da magoya baya dai-dai nasu, kuma addinin da kowacce cikinsu ke taqama da shi shine musulunci.

Musulunci kuma shine tafarki madaidaici wato addinin da Allah ya ambace shi da addini.

Allah (Swt) a Cikin Suratul Al'imran yana Cewa; "LALLE NE ADDINI A WURIN ALLAH, SHINE MUSULUNCI" (suratul Al'Imaran Aya ta 19).

Kowane daga cikin wayannan kungiyoyin yana ikrari ne akan cewa, shi mabiyin addinin Islama ne. In shaa Allahu kowannensu zan kokarta kawo bayannan su tare da hujjojinsu domin kokarin fadintar sabanin da yake tsakani.

Jamilu Sani Rarah
Fri 13/05/2016.

YA ZAMU KOYAWA 'YA'YAN MU SALLAH?



YA ZAMU KOYAWA 'YA'YAN MU SALLAH?
*************************************

'Ya ta Shekaranta 12 amma sallah ta zamar mata kamar wasu kaya a ka (domin duk yanda nayi da ita bata yin Sallah).

Wata Rana na Umurce ta da taje tayi Sallah. Na tsura mata ido har ta tafi taje ta dau sallaya ta shiga 'daki bata yi wani dogon dadewa ba ta fito a zuwan tayi sallah din amma ni na san bata yi sallar ba.

Na tambayeta ko ta gabatar da Sallar ta kuwa? Ta amsa min da "Eh", amma ni na san bata yi sallar ba. Cikin tsananin fushi na wanke ta da mari har sai da ta kife a kasa.

Daga baya kuma sai tausayin ta ya kamani, amma ba yanda zanyi domin saboda na gaji da halinta (na rashin yin Sallah). Nayi nadamar marinta da nayi na dauki alkawarin ba zan kara marin ta haka ba.Domin na san wannan ba zai amfani 'yata da komai ba.

Wata rana wata Qawata ta gaya min Cewa, takai ziyara wajen wata Qawarta, kuma Qawarta ta ba wata mai kula da addini ba ce sosai, amma a duk lokacin da aka kira sallah takan lura da 'ya'yan Qawartata sukan yi sauri su ta shi suje Sallah ba tare da an tsawatar musu ko tunatar musu ba.

Qawar tawa taci gaba da gayamin cewa, tayi mamaki kwarai a lokacin da ta ga yanda yaran nan ke lura tare da kula da Sallah. Sai ta tabbayi Qawartata Cewa, "Ko me yasa na ga yaranki daga zarar an kirayi sallah suke tashi ba tare da ke tsawatar musu ba?"

"Sirrin abin tun kafin Inyi aure na kasance Ina karanta Wannan addu'ar kowace rana kuma har yau ban daina karantawa ba". Haka ta gayawa Qawata.

Qawar tawa ta bani shawarar ni ma idan ina son 'ya'yana su kasance haka to nima In dukufa wajen karanta wannan addu'ar a koyaushe.

Tun lokacin da na dukufa wajen karanta wannan addu'ar 'yata ita ce ta farko wajen gabatar da sallah a gidan mu ba tare da an tsawatar mata ba.

Takan kuma tashi sallar asuba ba tare da ta saka alam ba. Haka ma duka 'yan uwanta da aka haifa daga baya suna sallah a lokaci.

Har ma dai aka kai itace ke tayar da mu sallar asuba kuma ita ke gaya mana lokacin sallah idan yayi Na san kun Matsu kuji Wace addu'ah ce nake karantawa to aya ta 40 ce a cikin Suratul Ibraheem
ِ
Wato, "Rabbi-Ajal'ni muqeema salaati, wa min Dhurriyyati, rabbana wataqabbal duaa" Hakika duka baya shiryar da 'ya'ya addu'ah ce ke shiryar dasu. Da fatan za'ah rika karanta wannan ayar da niya.

Jamilu Sani Rarah
Thu 19/05/2016


SABODA ME ZAMU KARANTA AL-QUR'ANI ALHALI BAMA JIN LARABCI?



SABODA ME ZAMU KARANTA AL-QUR'ANI ALHALI BAMA JIN LARABCI?
******************************************************************
***
Ina mamakin yadda kakana a koda yaushe yake kokarin Karatul Al-Qur'ani alhali baya jin abinda ake fadi (ma'ana baya jin Larabci).

Kamar kullum safe da rana da dare yake wannan karatu na al-qur'ani, yau dai da rana ne ya zauna yana karanta al-qur'anin sai gani nazo.

Abin nema ya samo dama ina bukatar in ganshi yana karanta wannan al-qur'ani domin in tambayesa dalilinsa na karanta al-qur'ani alhali baya jin larabci.

Na samu wuri na zauna ina jiransa domin ya kai aya muyi magana. Na zauna har tsawon mintuna 2 sannan daga baya ya tsayar da karatun da yake yi.

Nace dashi, Ya kai mahaifin babana akoda yaushe ina so inyi maka wata tambaya ce amma ban samu dama ba sai yau, Allah yasa zaka amsa min wannan tambayar tawa ba tare da kaji haushina ba.

Ya girgiza kai yayi min ishara da hannu da cewa in fadi tambayar yana jina. Nan sai na fara da cewa, "Naga kai ba balarabe ba, kuma kai ba Malami ba, kuma kai ba wanda ya zauna kasashen larabawa ba, hasalima kasashen turawa kayi karatun ka amma me yasa a kullum kake kokarin karanta Al-qur'ani Alhali baka jin yaren Larabci?"

Kakana ya nisa ya danyi tari, uhuk! uhuk! Sannan ya dubeni ya sake dubin gefensa na hagu sai ya dubi wani kwando (ga alama anyi aikin laka) da kwandon domin duka laka ya bata shi.

Sai yace dani, "Dauki wancen kwando je ka debomin ruwa a rijiya" taya yaya kwando zai iya diban ruwa? Nace da kakan nawa.

Kakana Yace dani, In shaa Allahu zai debo je kawai ka debo ruwan a cikin kwando. Ba tare da bata lokaci ba na tashi na dauki kwando na je rijiya na yi ta zuba ruwa a cikin kwandon amma dana zuba da ruwan sun zube a kasa.

Na zuba ruwan yafi a kirga amma da na zuba suke zubewa, nayi nayi har na gaji. Sai na dauki wannan kwandon naje na kaiwa kakana nace da shi, wallahi kwando ba zai iya debo ruwa ba amma idan ruwan kake so da gaske to bani wani abu (wanda ba kwando ba) inje in debo ma ruwan.

Kakana yace, a'a ni a kwando nake so kaje ka debomin ruwan. Anan na nuna masa kwando fa ba zai debo ruwa ba, amma ya matsamin akan sai naje na debo. A hakan na hakura na koma rijiyar domin debo ruwan a karshe dai na dawo ba tare da na debo ruwan ba. Saboda duk sa'adda na zuba ruwa a cikin kwandon zubewa sukeyi a kasa.

Bayan na dawo kakan nawa yace dani, har yanzu ka kasa debo ruwan ne? Nace masa, Eh bazasu debu ba. Sai yace dani, To shikenan amma dubi kwandon ka gani haka kaje dashi wajen debo ruwan?

Na dubi kwandon da kyau sai na ganshi yayi haske duk wannan lakar da ke manne a jikinsa ta debe kuma kwandon ya kara kyau, saboda wannan hasken da yayi.

Sai kakana Yace, TO HAKA AL-QUR'ANI YAKE A DUK LOKACIN DA KA KARANTA SHI KO BAKA JIN ABINDA AKE FADI TO ZUCIYARKA ZATA WANKE FES (Idan kana karantashi zai wanke ma daukar Hassada, Cuta, dasauran abubuwa).

Hakika tun daga ranannan na koma kamar Kakana Wajen Karanta Al-Qur'ani. Hakika naga fa'idar Karanta shi domin na kasance a cikin hassada da Kyashi kuma kullum nine gulma da sa'ido amma Cikin Ikon Allah duk na daina yin Wayannan abubuwan.

Jamilu Sani Rarah
Mon 23/05/2016.

LABARI MAI MA'ANAR GASKE


WANNAN WANI LABARI NE MAI BAN SHA'AWA NA WATA MATA MAI SUNA LAYLA 'YAR KASAR MOROCCO WADDA ALLAH YA JARABA DA CUTAR CANCER.

Likitoci sun taimaka matuka domin samarwa

da Wannan Mata Lafiya, amma Allah bai sa andace ba, hatta ita kanta Layla din ta debe tsammani daga Samun Waraka.

Ga abinda LAYLA ke cewa; Shekara tara Ina fama da Cutar Cancer duk wanda ya sanni ya san ina fama da wannan matsalar, kai hatta sunana aka fada Sai mutane sun tausaya min kasancewa Ina cikin wani hali na rai kwai-kwai mutu kwai-kwai.

Nayi tunanin in je in Kashe Kaina amma kuma tunanin irin hukuncin da zan tarar a Wajen Allah da kuma son da nake yiwa Mijina da 'ya'yana ya sanya dole na daina wannan tunani.

A lokacin da muka ziyarci Belgium, muje mun samu wasu likitoci game da matsala ta.

Shine suka gayawa Mijina Dole za'a debe nono na daya, sannan kuma zasu hadani da wasu maganguna.

Lokacin da suka bayyana mana sunan magungunan, sai naga ai da dadewa na taba amfani dasu.

Sukan sanya gashin kai na Zuba, sukan kuma sanya idona Fitar da kwantsa. Haka kuma sukan sanya Akaifun hannayena Kakkaryewa tare da sanya hakorana karyewa.

Kasan cewa, na san wannan maganungunan muka ki yarda da hakan. Na fiso in mutu da in koma amfani da wayannan magunguna.

Na buka ci likitocin da su cenja min magungunan saboda wayannan suna bani matsala, amma suka qi yarda da cenja min magungunan.

Na koma morocco in da likitana, Likitan nawa Ya bani Shawarar inje kasashen Yamma (Europe).

A Belgium akwai wani bala'i da suka tono min, domin kuwa likitocin sun gayawa mijina cewa, wannan Cutar ta shafi dukan Jikina Domin gaba daya wannan cutar ta mallake huhuna suka gayawa mijina babu wani abu da zasu iya akai don haka ya dauke ni ya mayar da ni Gida domin in mutu ko Allah yasa in mutu a cen.

A lokacin Mijina Ya Tsorata kwarai da gaske Amma mai makon mu koma gida morocco, Sai Muka Wuce faransa, a tunanin mu zamu samu mafita a cen (faransan).

Mu kaje Faransa amma babu wata mafita face irin Bayanin da muka samu a Belgium.

Daga Karshe sai muka yanke shawarar kawai a cire min Nonuwan in huta kamar yadda likitocin Belgium suka fada.

Muna cikin wannan tunanin ne kawai sai tunani ya fadowa Mijina "Hakika mun manta wanu abu guda wanda bamu damu da shi ba"

Na tambaye shi, "Menene?" "Bamu gaya wa Allah wannan Matsala taki ba" ya bani amsa.

Nan take mijina Ya Biya mana kuddin Visa da Taketi na jirgi na zuwa Saudiya (domin mukai kukan mu a dakin Allah).

Mu ka bar Paris "Allaho Akbar, La Ilaha Illa Allah" (Allah mai girma hakika babu sarki sai Allahh).

Nayi matukar farin ciki domin wannan shine farkon lokacin da zan yi tozali kuma in ziyarci dakin Allah.

Tun a paris na sayi Alqur'ani mai Girma abinda ban taba mallakarsa ba (na wa) a rayuwa ta.

Da shigar mu makka.. a lokacin da muka shiga masallachi tsarki, ai kuwa daga shiga ta ciki na fashe da kuka (kuka ba kadan ba).

Irin yanda naga an tsara wurin an qawata shi kuma na tuna da wurin da Annabi yayi Ibada kenan wuri mai falala da rahama shi yasan ya ni kuka.

Sannan a gefe daya ina kukan ne saboda ban taba fuskanta ko tunanin wannan wuri ba a rayuwa ta kuma ban taba rokon Allah ko tuna shi ba a shekarun baya.

Anan Nace, "Ya Allah! Kaine likitan likitocin da suka kasa warkar dani, duka kofofin samun waraka sun rufe min, banda wata mafita baya fa In rokeka, Ya Allah! Ya Allah! Kada ka rufe min kofar waraka".

Na ci gaba da kewayar dakin ka'aba ina rokon Allah akan Ka barni in koma hannu sake ba tare da na samu waraka daga gare shi ba.

Kamar yadda na fada a baya cewa, ni macce ce da bata da mu da harkokin musulunci ba, hasalima duk wani abu da ya jibanci musulunci kauyanci nake ganinsa.

Amma yau da kaina naje wajen wasu manyan malamai dake kasa mai tsarki ina neman taimako a garesu.

Suka bani shawara akan In je in rika karanta Alqur'ani Mai Girma, Sannan kuma suka bani shawarar in rika amfani da ruwan Zamzam.

Su Umurceni da In rika yin "Tadhalloo" kamar yadda suka kiransa da larabci ( Tadhalloo shine ka sha ruwan Zamzam Masu yawan gaske har sai ka ji ka koshi).

Sannan suka bani shawarar akan a duk lokacin da zan sha wannan ruwan in fadi sunan Allah tare da yin Salatin Annabi (Saww)

Suka bani tabbacin In shaa Allahu Idan har na Rika yin haka Allah zai bani Lafiya in dawo kamar kowa.

Anan na roki Mijina akan ya barni I zauna a Haram ba sai na koma Hotel ba l, mijina ya amince min akan in zauna a masallacin Haram shi ya koma a Hotel yaci gaba da zama.

A masallacin ne na hadu da wasu matan da suka zo daga Egypt da turkiya wayanda suka tausayamin a lokacin da nake yin kuka mai tsanani.

Suka tambayeni dalilin da yasa nake kuka, anan na sanar dasu duka labari na da kuma ciwon da ke tare da ni.

Allah Sarki basu gujeni ba suka zauna tare dani haka suma suka tambayi Izni daga mazansu akan su barsu domin su zauna a tare dani a masallaci.

A wannan zaman bama wani bacci kuma bama wani cin abinci mai yawa ko mai gina jiki, amma fa su ruwan zamzam mukan sha su da yawa har sai sun cika cikin mu.

Dama kuma Annabi (Saww) yace, duk wanda ya sha Ruwan Zamzam Allah zai warkar da shi idan har ya sha da niyar hakan.

A haka muka ci gaba da shan wannan ruwan muna rokon Allah kuma muna Dawafi tare da karatun Alqur'ani Mai girma. Wannan shine aikin mu safe da dare.

A lokacin da muka zo Dakin Allah babu shakka duka sassan Jikina yayi rauni sosai da sosai, domin Nonuwa na har fitar da Wasu ruwa masu wari hade da jini suke yi.

Saboda wannan kansar ta gama Illata min sassan Jiki na Duka.

To a lokacin cin Sai Wayannan Qawayen nawa suka Bani shawarar in rika wanke duka sassan jikin nawa da ruwan Zamzam. Ni kuma naki saboda ina tsoron Abinda zai iya biyowa baya domin ina gudun taba wannan Jikin nawa musamman Nonuwana.

Da ga farko na ki yarda da in rika wanke duka Jikina amma suka matsamin tare da takurani akan lalle sai na rika wanke jikina da ko wanka da wayannan Ruwan. A haka dole na bi shawarar su.

Na fara wanke Jikin nawa da wayannan Ruwa da farko na fara jin ciwo amma sai na daure na rika wanka da wayannan ruwan.

Cikin kwana Goma Sha Biyar da nayi Ina Wannan Wankan Na tarar da wani abu wanda sam nayi tunanin ba zai taba yiwuwa ba.

Domin ina taba Nonuwana na tarar babu jini babu Ciwo, nan da nan na bude duka sassan Jikin Nawa, domin ganin abin da ke faruwa da jikina.

Na tsarata kwarai da gaske ainun domin babu alama guda da zata tabbatar ma cewa nayi fama da Ciwo a Jikin nawa.

Nan na bude wa daya daga cikin Qawayen nawa jikina na Umurce ta da ta taba jikin nawa taji ai kuwa tana tabawa Dukan su Suka Dauki kabbara.

Allahu Akbar.. Allahu Akbar!! Na take na Arce da gudu na koma Hotel wajen Mijina.

Na Cira Rigata sama na Ce da shi, "Ka dubi taimakon Allah!" Anan na gaya masa duk abubuwan da suka faru da abinda kawayena suka sani in rika yi.

Nan take ya fashe da Kuka yace dani, "Shin ko ke san Likitoci sun Rantse da Allah akan nan da sati 3 zaki mutu akan wannan cutar?"

...Na Ce da shi; "Duka kaddara tana hannun Allah (Swt) babu wanda ya san abinda zai faru da wani face Allah Shi kadai.

Anan muka zauna har tsawon Sati daya, Na yiwa Mijina Godiya sosai da sosai abisa kokari da hakurin da yayi dani, su kuma wayannan kawayen nawa muka zama kamar Juna Ni da su.

Baya ga haka muka koma masallacin Annabi (Saww) da ke Madina. Daga nan muka wuce France.

A cen Lokacin da muka ziyarci Likitocin cen, duka wayannan likitocin suka Shiga mamaki tare da tambaya ta akan, 'Anya kuwa ke ce mai dauke da wannan Cuta?'

Cikin Izzan Na Ce da Su, YESS!! ..and this is my husband..we have
returned to God.. and I now fear nothing but Allah SWT.. (Ma'ana, Eh sannan kuma wannan Mijina ne mun koma nema ga Allah ne, Sannan yanzu babu wani abu da nake tsoro face Allah (SWT)).

Suka Ce Cuta ta babba Ce sosai da Sosai, Sannan Suka Sake Bukatar su sake yimin Gwaji.

Suka gwada amma basu tarar da wata matsala ba ko da ta Matsalar ciwon Kai Ce.

Bayan 'yan watanni na Samu "seerah" (tarihin Annabi (Saww) na rika karantawa da na shi da na sahabbansa (RA).

Hakika nayi Kuka kuma nayi da na sanin lokacin da na bata ba tare da kulawa da Wayannan Tarihin ba.

Hakika Na Yarda Cewa, Ruwan ZamZam Magani ne Makawar Ka sha da Niya kamar Yadda Hadisan Annabi (Saww) Suka Bayyana.

Jamilu Sani Rarah
Mon 13/06/2016.

GAJERUN KALAMAN DR. BILAL PHILIPS GUDA 20



GAJERUN KALAMAN DR. BILAL PHILIPS GUDA 20 AKAN MANUFAR KARATUN ALQUR'ANI.


1. A cikin Watan Azumi Allah (SWT) ya saukarwa da Annabi Muhammad (SAWW) da Al-qur'ani mai Girma.

2. Hakika Allah (Swt) ya saukar da Alqur'ani ne don Ya zama rahama a gare mu (kamar yadda bayanin hakan yazo a cikin Suratul Al-Baqara).

3. Yawaita Karanta (Al-Qur'ani) a cikin Wannan wata (na Azumi) ba Karamar lada ake samu ba.

4. Daga cikin ladubban karatun Alqur'ani akwai buqatar tunani a kan ma’anoninsa yayin karatun
sa. Wannan kusan shi ne mafi muhimmancin ladaban karatun Alqur’ani gaba daya.

5. Al-Qur'ani gaba dayansa waraka ne, idan kana dauke da Cutukkan zamani kamarsu HIV, Cancer to ka dukufa wajen karanta shi Zaka samu waraka da Iznin Allah.

6. Allah (Swt) a cikin Alqur'ani Yana Gaya mana Cewa, "Al-Qur'ani Waraka ne amma ga muminnai". Don haka makawar mumini ya yawaita karanta (Al-Qur'ani) to Allah zai bashi lafiya.

7. Idan kana son ka samu labarai da sakonni daga Ubangijinka to ka nemi al-Qur'ani ka karanta.

8. Dukkan Wani Sako da yazo a Cikin Al-Qur'ani to zaka same shi a cikin Suratul-Al-bakara.

9. Ka tsaya ka Karanci suratul Bakara tare da Sanin sakonnin da take dauke da shi, shiya fiye ma da ka karance duka Al-Qur'ani amma baka san ma'anarsa ba.

10. Ko mu karanta Al-Qur'ani ko kada mu karanta, babu abinda zai rage ko kara Allah (SWT) da shi. Don haka 'dan Adam ya karanta (Al-qur'ani) domin ya samu albarkar da ke ciki.

11. Matan da ke dauke da Jinin Al'ada zasu iya karanta Al-Qur'ani da ka. Ba tare da sun dauki (Shi Al-Qur'anin) ba, domin su samu albarka da kariyar da ke cikin karanta shi.

12. Makawar Al'umma basu chanja halayensu ba to Allah ba zai fitar dasu daga kangin da suke ciki ba. Don haka mu cenja Rayuwar mu ta hanyar karanta Al-qur'ani.

13. Zaka samu musulmi masu kallon Kwallo (ball) Idan anyi abu mai kyau a cikin wasan zasu tafa da nuna jinjina amma basu cika damuwa da yin sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah) ba.

14. Idan har kana cikin tsanani to kafin ka koka kafara yin sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah).

15. Idan har ka tsinci kanka da samun wani alheri to ka gaggauta yin Sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah) domin nuna godiya akan wannan Ni'Imar.

16. Sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah) ana yin ta ba tare da Alwala ba.

17. Sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah) Mata zasu iya yin ta koda suna a cikin Jinin Al'ada. Don haka a kowane lokaci farin ciki ko bakin ciki ya same ka ka gaggauta yin ta.

18. Yaren larabci Shine yare na biyu ga kowane dan adam (musulmi da ma wanda ba musulmi ba), domin idan bahaushe yaje kasar chana ya tarar ana kiran sallah da yaren Chananci ba zai fahimci me suke yi ba, amma makawar akayi da larabci to, kowa ma yasan kiran Sallah ne.

19. Idan har ka samu damar karanta Al-Qur'ani ka qi kayi to babu makawa wahalhalu da matsaloli zasu dabai-baye ka.

20. Kada mu bari mu koma ga Allah (Swt) ba tare da Munyi Sujood al-shukur (Sujudar godiya ga Allah) ko sau daya ne a rayuwar mu ba.

Wayannan kalamai zamu iya kiran Su da gajerun Kalamai a baki ko a karance amma ta fuskar fahimta tarin tulin Ilmi ne a dunkule tattare a wuri daya.

Dr. Bilal phillips (Abu Ameena) ya gabatar da Wayannan Kalamai ne a muhadarar da ya gabatar a Usman Danfodio University Sokoto akan manufar dake cikin karanta Al-Qur'ani a jiya Laraba 15/6/06.

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Thu 16/06/2016

KARAMAR TAMBAYA TA HANASHI SAMUN MATA



KARAMAR TAMBAYA TA HANA SHI SAMUN MATAR DA YAKE SO.
***********************************************************
Wani Yaro dake Mutuwar So da kaunar wata Yariya ya Rasata saboda kasa amsa wata karamar tambaya da akayi masa. Yaron ya kasance dan masu fada aji a garine bayan haka kuma ya kammala karatunsa a matsayi na mastas kuma ya samu aiki wata babbar ma'aikata a kasashen larabawa.

Yazo wajen mahaifin yariyar da yake so aure, ya ce da mahaifin yarinyar,"Baba na kammala karatuna, Na mallaki mota biyu da gida daya sannan Ina da filaye guda 4 wayanda zanyi gini in sanya 'yan haya, domin bana son in dogara ga aikin gwamnati".

"Nazo ina son 'yarka da aure hakika zanyi farin ciki idan ka bani aurenta, kuma zan kula da ita. Kuma koda ace wani ya kashe mata kuddi hakika zan iya biyansa ko nawane domin ina sonta".

Mahaifin yarinyar yayi murmushi sannan ya dubi yaron daga bisani yace da shi, "Hakika babu wanda ya kawo kuddi balle ka biya, sai dai zan yima tambaya guda daya".

"Idan ka bani amsar tambayata zan yarde ma ka auri 'ya ta, ba ina bukatar kuddinka ko gida ko wani abu ba, a'a ina bukatar amsar wannan tambaya daya ce kawai".

Yaron yayi farin cikin da jin hakan tare da sonjin wacce irin tambya ce za'ayi masa.

Mahaifin yarinyar ya kalli Idanuwan yaron Sannan yace dashi, "Ka amsa min sau daya kawai, A karfe nawa Ladanin Unguwarku yake kiran Sallar Subahin?".

Nan da nan jikin yaron ya fara rawa, ya juya nan ya juya cen, bayan yayi dan tunani kadan sai yace, "Ina ganin Karfe 4 ake kira...a'a karfe 3:30...a gaskiya Baba ban sani ba".

Mahaifin yarinyar cikin Murmushi yace da yaron, ”I don’t care of your high status or your bank account! My daughter is so precious, she is like a princess to me with her Hijab and purity so she needs someone who treats her like a queen!

No one would make her happy more than a man who fears Allah and obeys Him. Only a righteous husband would give her an unlimited happiness by helping her to get closer to Allah”.

Nan take yaron yayi godiya ya tashi. a hanyarsa ta komawa gida ya rika tunanin a zuciyarsa cewa, ashe mahaifinta ma 'dan bokone? Wato a tunaninsa tunda yana riko da addini Shi ba d'an boko bane
 
Jamilu Sani Rarah Sokoto.

KYAKYKYAWAR MU'AMULA NA SA A KAUNACI MUSULUNCI


KYAKYKYWAR MU'AMULA NA SANYA A KAUNACI MUSULUNCI
************************************************************
A lokacin da aka fara yin sufuri da jirgin European Airline, da akwai wani musulmi mai tsoron Allah a zuciyar shi a cikin Jirgin. Shi Wannn bawan Allah yana zaune ne a wurin da masu fada aji suke zama (Wato first class section a turance).

A daidai lokacin da Jirgi ya fara tafiya sai ma'aikaciyar Jirgi (wato air hostes) ta gabatar masa da kyautar kofin giya wadda kamfanin Jirgin ya dauki nauyin bayarwa ga fasinjojin jirgin.

Cikin ladabi da girmamawa ya kalle ta yace, "Nagode aini bana shan Giya" ta kalle shi cikin natsuwa ta gyangyada kai (alamar mamaki).

Wannan matar ta damu ainun da Qin shan Wannan giya da yayi, nan take taje ta sanarda Manajan akan akwai wani da yaki karba "..Wai baya shan Giya".

Manaja yayi tattaki har wajen wannan bawan Allah, Shima dai dauke yake da Giyar Yace da wannan mutumen; "Shin ko akwai abinda kake tunani game da mune? Hakika ka karba kasha wannan kyauta ce ta musamamman daga kamfanin mu".

Bawan Allah Cikin Ladabi Ya kalli Manajan Yace da shi, "Ni Musulmi ne kuma musulmi basa shan Giya".

Manaja yace yaji amma yana son ya karba ya shan ko da sau daya ko biyu ne domin wannan rana ta yau ranar farin ciki ce.

Wannan bawan Allah yayi murmushi ya dubi manajan Yace da shi, yaji zai sha amma suje ya fara bawa direban Jirgin ya fara sha sannan shi ma yasha.

Cikin mamaki manajan Jirgin Yace; "taya Direba zai sha Giya Alhali yana aiki (na jan jirgi?) Ai da zarar ya sha giya wannan jirgin zai samu Hatsari".

Wannan bawan Allah ya kalli wannan Manajan Yace da shi, "Ni musulmi ne sannan akoda yaushe ina kan aikina na tsare Imani na Idan har na sha wannan barasar to kuwa zan sanya rayuwa ta cikin hatsari domin zan rasa Imani na".

Allahu Akbar, Wannan ta sa Wannan manaja da wannan matar duka suka girgiza suka shiga tunanin karbar Musulunci daga hannun Wannan Bawan Allah.

Hakika haka Ake Son Musulmi ya siffantu da kyawawan dabi'u da kuna iya zance kada ya mayarwa da musulmi da wanda ba musulmi ba magana cikin zafi ko jin haushi.


Jamilu Sani Rarah Sokoto
Fri 24/06/2016

SABON SALO MUSULMI DA BAUTAR SHAIDAN (LA)

SABON SALO MUSULMI DA BAUTAR IBLESS (L.A).
***********************************************



Masu Bautar Shaidan (LA) wato Illuminiti Sun rubuta a Cikin Coustitution dinsu cewa, "Mallakar Media kamar Mallakar Public ne" ma'ana Idan Suka Mallaki Hanyoyin Sadarwa (Kamarsu, TV, Facebook, Istagram, youtube) to kamar Sun mallaki gama garin al'umma ne.

Babu shakka Zancensu Yana so ya zama gaskiya koma In ce ya zama gaskiya muddin bamu tashi tsaye ba.
Akwai wata Sabuwar Rawa ko Kuma daukan Photo da ya fito Sabo Wanda ake Kira da DAB STYLE ko kuma DAB DANCE. Babu shakka wannan salo ne na bautar Ibless (LA) da masu bautarsa (LA) suka fito dashi a kokarinsu na jan ra'ayin jama'a game da wannan bauta.

Dab Dance ko kuma Dab Style ta samo asaline daga Wani mawaki da ake kira da Migos wanda shine Mawakin da ya fara yin wannan rawar har ya yi mata waka.
Ana haka sai dan wasan kwallon karfin nan wato Cam Newton ya watsa wannan rawa a duk lokacin da ya ci wasan sa na kwallon karfi.

Daga nan kuma sai wani mawaki mai suna Jay Z (Wanda kusan kowa yasan Cewa, Shine Shugaba na masu bautar Shaidan) yayi wannan rawa a cikin Wata Wakarsa mai suna “Fuck With Me You Know I Got It”.
Babu shakka daga nan Sai Sauran mawaka da 'yan Kwallon kafa suka dauki wannan dab dance din suka juyar da shi a zuwa dab Picture.

Ma'anar Dab dai shine, Rufe Fuska da hannun hagu ko dama sai hannu dayan a mikar dashi. Masu shan tabar Iblis wato Wiwi sun kasance Suna amfani da wannnan kalma ne a lokacin da suka zuqi taba wiwi din suka sha. Ma'ana idan ka zuqi tabar ta wiwi sai ka noke fuskarka a cikin hannunka daya shi kuma dayan ka rike tabar ta wiwi da shi.

Migos wanda ainahin Shine ya kawo wannan rawar ta Dab Dance Abinda yake Nufi da Dab Shine "Dimands are bright". Dimands kalmace da aka dauko daga yaren Greek adámas, wacce take nufin abinda baya karyewa ko kuma baya samun wani nakkaso ko baya samu wata tangarda.

"Dimands are bright". Ma'ana Lu'ulu'u Mai haske ne (a yanda suke nufi shine Shaidan Kenan) ku lura Dimands aka ce ba Diamonds ba, duk da Shima Lu'u'lu'u yake dauka amma wannan Shaidan Iblees Suke nufi. Don haka don Allah Mu guji Yin wannan Photo da Sunan Wayewa ko da Sunan Burgewa, ko kuma da sunan mun ga wani babban 'dan film ko mawaki ko dan kwallo yayi. Hakika da yawa daga Cikin Wayannan 'yan Film din Da 'yan Kwallo da Mawaka yaran Shaidan Ne masu bautarsa ke nema masa passenger.
Duk wani mawaki ko dan film ko dan kwallo da kuka ga yayi Dab to babu Shakka yana mika Bautarsa ne ga Mai Gardama Shaidan (LA).

 Zaku Iya Kallon Wata Wakarsu a nan https://m.youtube.com/watch?v=oet8spdBCtA Ina Fatan Duk Bawan Allah da Yaci Karo da Wannan Sako nawa Don Allah Ya sanarwa da 'yan Uwa domin Mu kula.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Mon 11/07/2016