Thursday, 8 December 2016

MATSAFI YA FADA HANNUN 'YAR MADIGO

MATSAFI YA FA'DA HANNUN 'YAR MADIGO
********
Na hadu da wani daga Cikin Abokanai da na dau kusan Shekara 3 zuwa 4 bamu hadu ba, Sai dai a waya ko kuma A kafar sadarwa ta Facebook.

Ya bani Wani Labari da ya Girgizani tare da tunanin Anya kuwa irin wannan labari zan barshi a dunkule ba tare da na 'dan fincina wa mutane na shi ba. Ko ba komai wasu zasu fadaku tare da sanya Ido ga 'ya'yansu da Qannensu da matansu.

Shi Wannan abokin nawa yana da wani aboki wanda kusan baya jin shawararsu duk yanda suka bashi shawara (kuma zama dashi ya zamar musu dole ne.

Ablinda ke faruwa shine wannan abokin nasu ya kasance yana son wata kyakykyawar yarinya Qin wanda ya rasa Son wanda ya samu.

Yayi juyin duniyar nan akan ta so shi amma kuma ba ta ko sauraren shi balle har ya samu ta amince masa (ta yarda da soyayyarsa).

Kwatsam sai Zuciyarsa ta bashi shawara akan cewa, ai yaje ya kai ta wajen Wani wanda duk mai hankali ba zai so a kirashi da malami ba. Saboda yana amfani da malantaka ne yana bokanci.

Ya je ya sami bokan ya gaya masa shakkuwarsa. Nan take wannan bokan Sai ya je yayi tsibbace-tsibbacensa tare da kulle-kullensa da siddabaru akan yarinya ta so wannan yaron.

Ai kuwa cikin kan kanen lokaci sai wannan yarinya ta fada tarkon Aljannun da wannan yaron ya sa aka turo mata domin su rika nuna mata shi a matsayin masoyi.

Kwana tashi Sai ya zamo wannan yarinyar duk duniya bata ganin kowa face, wannan yaron. Shi kuma sai ya fara Jin dadi akan aikin boka yayi kyau.

To meya faru? Kwatsam sai Wata babbar macce ta kirayi wannan abokin nawa mai bani labari tare da gargadarsa akan ya yi maza ya umurci abokinsa ya rabu da wannan yarinyar saboda kayan su ne. Ina fatan wannan hausar ta fito da kyau.

Ma'ana Budurwarsu ce da suke yin madigo da ita (wa'iyazu billahi). Ya amince akan zai bashi shawara akan ya rabu da ita. Haka kuwa akayi ya kira abokinsu ya bashi shawara amma yaqi ji.

Bayan da wannan labari ya zowa saurayin sai kawai ya fara tunani a zuciyarsa cewa, dama wance tana madigo? Ai nan take ya shiga bincike akan ya gano gaskiya.

Ai kuwa sai ya gano Cewa, ashe tana Madigo kuma tafi kusan Shekara biyar tana wannan muguwar 'dabi'a (kenan wannan shibe dalilin da yasa taki amincewa da soyayyarsa tun farko, Sai da yaje wajen boka).

Nan ya fara nadama marar amfani. Eh nadama marar amfani kuwa saobda a duniya ya tsani yar madigo ko 'dan luwadi. Amma kash yau gashi ammasa Baiko da 'yar madigo.

Nan yaje wajen Bokansa akan a raba wannan magani da akayi domin ta soshi. Ai kuwa boka ya aiwatar da abinda ya umurce shi da yi (ya raba wannan magani).

Nan take taji bata sonsa kuma gashi an musu baiko. To meya faru ashe Ita ma tana da nata boka sai taje ta koka masa matsalarta.

Wannan boka yayi na shi tsafi ya gano cewa, tun daga farko magani yaron yayi mata. Ai kuwa da aka gaya mata sai tace ita ma ayi masa magani yaji duk duniya kowa baya so sai ita.

Nan take Wannan bokan ya aiwatar shi kuma wannan yaro sai gashi ya fada tarkon so da kaunar yarinyar baji ba gani.

Ganin irin yanda yake binta take wulaqantashi (kuma aurensu ya kusa), shi ya sanya wannan abokina mai bani labari ya shirya zama da yarinyar don yaji meye matsalar take yiwa abokinsa wulaqanci.

Ai kuwa sai ta fafe masa biri har wutsiya tare da gaya masa cewa, babu shakka ita 'yar madigo ce. Kuma ta lalata yara babu adadi kuma zata ci gaba da lalatawa.

Kuma auren abokinsa babu mahani domin tunda yayi mata magani ita kuma sai ta gwada masa ko wacece. Domin sai ta aure shi kuma bayan auren sai ta mayar da gidansa Kasuwa ta Safarar mata domin yin madigo (Wa'iyazubillahi).

Yanzu dai kam An kusa Aure.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Thus08-12-2016

Wednesday, 7 December 2016

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

"Musulunchi ba Yana Nufin Ka dauki Wuka ko Adda ba kayi kabbara ka kashe wani. A'a musulunchi na nufin zaman lafiya da kyakykyawar mu'amula."___ Cewar, Sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar III.

"Ga Wani gwaji da yakamata muyi domin samun Kyakkyawar dangantaka da mu'amula."

"Mazaje Ku taimaki matayenku a aikace-aikacen gida, Sannan Idan zakuci abinci (misali da dare) ku dauka da hannunku ku ciyar dasu. Idan ka ciyar da ita to ita ma ta sanya hannunta ta ciyar da kai."___Cewa, Mufti Menk.

"Rayuwarka Kamar Photo Ce, Shi kuma Musulunchi Kamar Gidan sanya photo ne. Idan har kai musulmin kirkine, to ka dauko gidan photon nan ka sanya shi ciki. Kayi amfani da ilmin da kaji. Ka tafiyar da maganganu a aikace musulunchi ya zamo a cikin kirjinka. Kayi maganar gaskiya kada ka karkatarda magana. Kuma kada kayi da'awar abinda baka da shi sannan ka aiwatar da musulunchi a dukkanin rayuwarka."

"Babu wata kasa ko Al'umma da zasu ci gaba makawar basu bi dokokin Allah ba Sannan basu girmama Shuwagabanninsu ba, kuma basu bi koyarwar malamansu ba. Ka mu'amulancin malamai tsawon kwanakki bakwai dake cikin sati. Ka roki Allah tsayuwa akan Ibada ba saudaya ba domin ita ke bunkasa kasa" ___ Cewar, Sheik Assim Al-Hakeem.

"Allah yana Son Masu son Junansu ba don komai ba sai domin Allah. Makasudin samun nasara a wannan rayuwa shine dukkannin mu mu zama abu guda saboda Allah"

"Kada mu bari Zuciyoyinmu su jamu zuwaga ganin kyashin juna ko kuma Yawaita ganin laifin juna idan muka hadu wuri daya hakika zamu kai ga dacewa. Mu rika yiwa junanmu godiya. Sannan mu so makwaftan mu kamar yadda muke son kawunan mu. Hakika murmushi abincin ruhine mu zama masu gaskiya game da rubutun mu. Ina rokon Allah ya taimake mu duka. Mu rika rokon hadin kai ba rarrabara kawuna ba."__ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Nawane ake Sayarda Manyan Gidaje a Abuja da Lagos? Hakika farashin da zaka biya ka shiga Aljanna Shine, ka yafewa dan uwanka duk laifin da yayi maka. Hakika hakkine akan kowanen mu akan ya yada zaman lafiya kuma umurnine akan mu rika yafewa juna. Ya ku mutane! Ku yada zaman lafiya tsakanin ku. Sannan ku ciyarda matalauta da masu jin yunwa. Ku sowa dan Uwanka/'yar uwarka abinda kake sowa kanka. Hakika ba zaka zama mai Imani ba har sai ka sowa dan uwanka abinda kake sowa kanka. Allah yana son masu gaskiya."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Idan har da gaske kana Son Manzon Allah (SAW) to kabi Allah sannan ka zama mai yafiya ka zama mai son Juna, Ka ajiye duk wani rudani gefe kada ka nuna kafi kowa iyawa domin yana kai mutum zuwa ga dolanci. Ka zama mai taka tsan-tsan ga lamurranka kada ka bari zuciyarka ta rufe ga gaskiya. Musulunchi ba addini ne kawai ba, A'a musulunchi hanyar Rayuwa ce. Nemi ilmin gaskiya. Allah ya Albarkacemu da kyakkyawar fahimta ka tsare mu da Ilmi mai yawa saboda ilmi mai yawa Wani lokaci cuta ne."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kayi hankali da yawan ganin laifin mutane da yawan ganin Laifin Shuwagabanni. Ka yarda da kanka ka gyara halayenka wannan shi zai cenja gidajenmu, da 'yan uwanmu da Al'ummar mu dama Duniya gaba ki daya ka yarda da kanka ka kauracewa miyagun halaye ka tuna cewa Adanannar dukiyarka na Aljanna. Ka yarda da Allah kada ka taba debe tsammani kayi kaffa kaffa kada ka taba debe tsammani daga rahamar Allah. Allah Yace; "KA GAYAWA BAYINA WAYANDA SUKA CUCI KAWUNANSU KADA SU TABA DEBE TSAMMANI DAGA RAHAMAR ALLAH"..Ya Allah ka hada mu a lambun Aljanna."____ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kada ka shagaltu da ilmin da ka samu na Wannan taro (na wa'azi) na kwana biyu kace ya isheka kawai. Kayi godiya ga malaman kasarku da suka dade suna karantarda ku tare da tarbiyantar da ku."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Allah ya kara mana Imani. Hakika addinin Musulunchi addini ne na Zaman lafiya ba na rikici ko tashin Hankali ba. Mu tashi tsaye kada mu sanya gajiyawa. Mu zama masu Alfahari ba masu girman kai ba."____Cewar, Ustaz Abubakr Sadiq

Ni da na fassara Ina fatan Wayannan Gwala-gwalan Kalamai zasu samu wurin zama a cikin Zukatan mu.

Anyi Wannan Wa'azin ne a  dakin taro da ke Abuja a Ranar 3 da Ranar 4  ga watan 12. 2016.

Fassarawa, Jamilu Sani Rarah Sakwkwato.

Monday, 5 December 2016

MEYE LAIFIN SHUGABAN KASA BUHARI GA SADAKIN ZARAH?

MEYE LAIFIN SHUGABA BUHARI A CIKIN SADAKIN ZARAH?
*******
Tunkusan Lokacin da Akayi Sadakin Zarah 'yar Gidan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na ke samun Sak'onni akan ba'aji nayi sharhi ba game da wannan Sadakin.

Alhamduli Lahi bayan 'yan Uzurukka da suka sha gabada Sai yau Allah ya kaddare ni da Cewa wani abu game da wannan Sadaki.

Har yau har gobe Ina Kara kira ga 'yan Arewar mu akan Don Allah su daina Sanya Kansu cikin Kwano ko k'ok'o suna tunani su rika bude kawunansu suna tunani.

Da farko ina son mutane su san Wanene Ahmad Indimi sannan suyi tunani mai kyau game da shi Kafin Su rika yanke Hukunci game da duk wannan Sadaki na shi.

Kafin Nayi bayani akan Ahmad Indimi bari na fara bayani akan Jahar Borno (In da Cen ne Garin Su Ahmad da Mahaifansa).

Wani daga cikin Masu son jin ra'ayina game da wannan Sadakin ya min tambaya game da wannan sadaki na Zarah Buhari.

Amma mai makon In bashi amsa sai na kyale shi Na kira wata baiwar Allah Wacce 'yar asalin maiduguri ce.

Bayan na kira ta dauka sai na saka Speaker domin yaji me zamu tattauna ana akai. Bayan mun gaisa sai na tambayeta Cewa, "Shin har yanzu A maiduguri Miliyan daya ake Sadaki?"

Sai tayi dariya tace dani, "Humm yanzu wannan Recession da ake ciki wa zaiyi wani sadaki milion 1"

Sai nace, "To nawa ake yin Sadaki Maiduguri a yanzu?" Sai tace dani, "Dubu d'ari bakwai, d'ari biyar Ida kuma mutum bai da shi sosai Cikin Anyi hankuri an matse sai ya biya Naira dubu dari biyu da hamsin ko kuma dubu d'ari da Ashirin."

Bayan mun gama magana mukayi Sallama na kashe waya ta. Tare da tambayar wannan mai tambaya ta ko kaji wayar da nayi? Sai yace da Ni "Eh yaji ashe haka maiduguri suke."

Sai nace dashi to Wanda yayi wa Zarah Buhari Sadaki 'dan Maiduguri ne, kuma a maidugurin ma su ne manyan masu kuddi.

Baban Ahmad Wato Muhammad Indimi Surukine ga Tsohon Shugaban Kasa Ibrahim Badamasi Babangida IBB.

Sannan Muhammad Indinmi Shike da kamfanin nan na Oriental Energy Resources Limited, kamfanin da ke da rijiyoyin mai har guda uku da suka hada da: OML 115 da ta Oldwok da kuma ta Ebok.

Sannan Shi Ahmad Indimi yana daga Cikin Manyan Daretoci na Kamfanin domin Shine daracta na Ukku a kamfanin.

Sannan Ahmad Indimi din da kake ji yana daga Cikin Matasan Samari da ke da taimako domin IDPs INTERNAL DISPLACE PERSONS (Wato mutanen da rikici yasa suka bar mazauninsu) ya taimakesu kusan da Naira Miliyan d'ari biyu har da wani abu.

Sannan Idan ka koma B'angaren Ita kanta Zarah Duk kusan Cikin 'ya'yan Manyan Kasarnan Kaf (ban cire ma kowa ba daga cikinsu), ta fisu taimako tare da Neman Dukiya. Domin har Ophanage (gidan marayu) take da shi.

To mene A Ciki don Shi Wannan matashin Mai kuddi ya bi Al'adar Garinsu ta yin Sadaki da Tsada? Tun da dai ba'a kaiyade kuddin Sadakin ba a musulunce.

A musulunce Kuddin Sadakin Bana yanda malamai suka yi kiyasi shine naira 8400, Shin don Allah akwai wanda yaga In da akayi Sadaki 10,000 a bana? In kuwa babu inda akayi to me yasa don shi yayi al'adar garinsu (na yin sadaki da tsada) abu zai zama abin Ganin Laifi.

Ni banga laifin Wannan Ba Gaskiya sai dai abinda muke cewa da Su Wayannan Samarin Sunyi kwaikwayo da Sunnar Manzon Allah (Saww) na Takaita Sadaki da Sun kyauta. Domin Manzon Allah (saww) yake cewa, Aure Mafi albarka shine wanda sadakinsa ya zamo mafi sauki".Kuma da Sun bar tarihi a kasarnan.

Da kuma sun kwaikwayi auren Nana Fatima da Sayyidina Aliyu da Sun burge duk wani ma'abocin Sunnah.

Lokacin da Sayyidina Aliyu (Rta) ya nemi Auren Nana Fatima (rta) bayan Annabi (Saww) ya tambayeta kuma ta amince sai Manzon Allah (Saww) ya cewa Sayyidina Aliyu (RA): "Ya Aliyu, shin kana da wani abu da zan daura maka aure da shi (sadaki)?".

Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya ce: "Sai takobina da garkuwata, sai kuma rakumina na ban ruwa ", (a wata ruwayar an ce doki ne maimakon rakumin)

Sai Manzon Allah (Saww) ya ce: "Amma takobinka kana da bukatarsa, za ka yi yaki da shi a tafarkin Allah kuma ka kashe makiya Allah da shi.

Rakuminka kuma kana shayar da (gonar) dabinonka da shi, haka kana daukar kaya da shi, kuma yana daukarka a tafiye-tafiyenka.

Don haka je ka yi yadda za ka yi da
garkuwarka". Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya je ya sayarwa Sayyidina Usman bin Affan (RA) da garkuwarsa a kan farashin dirhami 480, sai ya kawo wa Manzon Allah (saww).

Daga nan Manzon Allah (Saww) ya sanar da Musulmi zancen auren.

Haka kuma na So ace Zarah Buhari ta kwaikwayi Ummu Sulman An Ruwaito Cewa Sahabbai (RA) suna
Cewa, "FIYAYYEN AURE SHINE AUREN UMMU SULMAN (RA), DOMIN ITA SADAKINTA MUSULUNCI NE."

Ummu Sulman Itace Mahaifiyar Anas Bin Malik (Hadimin Manzon Allah (Saww)), lokacin da mahaifinsa ya rasu, taqi yin aure har Saida Abu Talha ya fito yana Sonta sannan ta amince zata aure shi amma da sharadi zaya Musulunta (Musuluntarsa Shine Sadakinta).

Bayan manyan attajirai da Masu mulki da Sadaukai sunyi ta fito mata amma taki amincewa dasu. To da ace Zarah Buhari ta Bukaci kada sadakinta Yayi tsada haka to babu shakka da ta kyauta.

Kuma ba zanga Laifinta ba ko na wanda zata aura ko mahaifanta don anyi mata sadaki naira miliyan 44, sai dai muna cewa a kamanta Sunnah ga dukkanin Abubuwa yafi.

Subhanallah...!

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Mon 5/12/2016

Wednesday, 30 November 2016

LABARIN YAJUJ WAMA JUJ

LABARIN YAJUJU DA MAJUJU.
*********

 
Allah (Swt) a Cikin Al-Qur'ani mai Girma Yana Cewa;

ﺣَﺘَّﻰ ﺇِﺫَﺍ ﻓُﺘِﺤَﺖْ ﻳَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻣَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻫُﻢ ﻣِّﻦ ﻛُﻞِّ ﺣَﺪَﺏٍ ﻳَﻨﺴِﻠُﻮﻥ


Ma'ana "Har sa'ad da aka bude Yajuju da Majuju alhali kuwa suna gaggawa daga kowane tudun kasa." (Suratul Anbiya aya ta 96(

Yajuju da Majuju, tsatso ne, na daya daga cikin ‘ya'yan Annabi Nuhu (Alaihis Salam).

A zamanin Annabi Ibrahim (Alaihis Salam) da akwai wani sarki da ake kira da Zulkarnaini, shi wannan sarki, Allah ya bashi iko da kuma Mulki tun daga Bangon Gabas har zuwa yamma.

Shine mutumen da ya zagaye duniya tun daga farkon Inda rana take fitowa har Inda take faduwa.
Wasu ma suna ganin Zurkarnaini Annabine, amma dai maganar gaskiya zurkarnaini Sarki ne kuma mutumin kirki ne da ya shimfida Adalci, shine ya gina wannan Katanga da ta raba wannan duniya da Yajuju da Majuju. Haka kuma, wannan Katanga an gina tane da narkakken karfe da
duwatsu da kwalta da ruwan dalma.

A zamanin Zulkarnain wadannan al’umma (Yajuju da Majuju) sun addabi mutane, shine al’ummar da
Zulkarnaini yake mulka suka rokeshi da ya gina musu katangar da zata rabasu da Yajuju da Majuju.
Yajuju da Majuju sunyi ta kokarin fasa wannan Katanga su fito amma kuma sun kasa.
Sunyi dukkan irin dabarunsu su yi tsalle su fito amma Allah bai basu iko ba, shine tun daga wancan lokaci har kawo yau suna nan suna kwakwule wannan Katanga domin su samu su fito, amma Allah ba zai basu iko ba, sai a karshen duniya.

Ibn Mas’ud (Rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (Saww) cewa. A daren da Manzon Allah (Saww) yayi Isra’I ya hadu da Babansa Annabi Ibrahim da Annabi Musa da kuma Annabi Isah, dukkansu sun tattauna akan shin yaushe ne Alkiyama zata tsaya, sun fara tambayar Annabi Ibrahim yace bai
sani ba.

Daga nan Annabi Musa yace shima bai sani ba, daga nan sai Annabi Isah yace babu wanda ya san wannan ranar sai Ubangiji shi kadai.

Sai Annabi Isa (Alaihis Salam) ya cigaba da cewa, abinda Ubangijina ya gayamin shine a karshen duniya, Dajjal zai bayyana, ya zama fitina daga karshe sai a sauko dani, idan ya hadu da ni zai dinga narkewa yana zagwanyewa, Haka nan Allah zai halakar da shi (Dajjal).

Sannan Musulmi zasu yaki kafurai, har sai takai matsayin da Idan kafiri ya buya a bayan wani dutse ko bishiya, zasu yi Magana su kirawo musulmi suce masa zo ga kafiri ka kashi shi.
Daga nan kuma, adalci zai yadu a ban kasa tsakanin Musulmi, can kuma sai Allah ya fito da Yajuju da Majuju. Zasu barko cikin wannan duniya ta gabas da yamma kudu da Arewa, suna shanye ruwa, suna cinye dukkan wani abu da suka yi arba das hi. A lokacin ne al’umma zasu je ga Annabi Isah suna mai rokonsa da ya roki Ubangiji Allah ya kade musu wannan Masifa da Bala’I na Yajuju da Majuju.

Sai Annabi Isah ya daga hannu ya roki Ubangiji, Allah mai girma da daukaka ya amsa, sannan ya dinga saukar musu da tsutsotsi daga sama, suna halakar da su, bayan sun mutu duniya gabaki daya zata cika da warin gawarwakinsu da jinanansu.

Daga nan kuma Sai Allah ya saukar da Ruwan Sama wanda zai wanke duniya gabaki daya ya wanke dukkan dattin gawarwakin Yajuju da Majuju.

Annabi Isah (Alaihis Salam), ya cigaba da cewa, daga zarar Allah ya saukar da wannan ruwa, to babu wani abu da yake gab da zuwa face Alkiyama.

Haka kuma An karbo hadisi daga Abu-Huraira (Rta), Cewa, Manzon Allah (Saww), ya ce “A kowacce rana wasu al’umma (Yajuju da Majuju) suna nan suna hake wata Katanga, da zasu shigo cikin wannan duniya.

Sai sun yi haka har sun gaji, sannan zasu fara hango harsken rana, abinda yake nuna hakarsu ta kusa cimma ruwa (ma'ana sun kusa bige ginin), sai kawai shugabansu, ya umarce su da su koma su kwanta su huta gobe zasu dawo su cigaba.

Cikin hukuncin Ubangiji washe gari suna zuwa, sai su tarar Allah (Swt) ya shafe wannan Katanga ta kara karfi da kwari, sama da yadda suka sameta a jiya. Haka zasu sake cigaba da tone wannan Katanga, su sake komawa, washe gari su sake ganinta kamar basu taba haketa ba.

Haka nan zasu yi ta yi, har sai lokacin da Allah ya hukunta fitowarsu. Idan sunyi aiki har sun bula katangar sun fara hango hasken rana, anan ne shugabansu zai umarce su da su koma su
kwanta, gobe idan sun dawo zasu cigaba, amma a wannan Ranat zai ce IN SHAA ALLAHU.
Bisa fadin IN SHAA ALLAHUN da shugabansu ya yi sai Allah ya amsa, washe gari idan sun komo zasu sami wannan Katanga yadda suka barta jiya! Bayan dawowarsu ne, washe gari, zasu ci gaba da yin aikinsu na bugun wannan Katanga.

Kuma cikin nufin Allah, zasu buge wannan gini su shigo cikin duniya daga katangesu da Allah yayi da al’umma, idan suka fito zasu shanye dukkan wani ruwa da sukayi ido hudu dashi, sannan zasu cinye dukkan wani abinci da suka gani, kai kusan dukkan wani abu da suka gani sai sun cinye shi.

kama daga Bishiya tsirrai da dabbobi, sannan zasu shiga kisan mutane babu ji babu gani!
A wannan lokacin Yajuju da Majuju zasu dinga harba kibau sararin samaniya. Suna harba kibiyoyi da masuna, sannan suna fadowa kasa suna masu digar da jini a jikinsu, anan ne Yajuju da Majuju zasu ce, mun gama da al’ummar da take a ban-kasa sannan kuma wadan da suke sama suma mun gama da su!
A lokacin da suka yi wannan ikirari ne kuma, Allah zai yi musu ruwan wasu irin tsutsotsi wadan da zasu dinga makalemusu a wuya suna cizonsu, haka nan, wannan tsutsa zata hakalasu gabaki dayansu a
cikin dare daya!

A duba a Cikin kitaab al-fitan, (hadisi 4080), 2/1364.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tues 30/08/2016

SANARWA MAI MUHIMMANCHI GAME DA MADIGO DA LUWADI

SANARWA MAI MUHIMMANCI
********
Ka karanta tabbas Zai amfaneka idan ma bai amfaneka ba zai amfani 'danka, 'yarka ko kuma qanenka ko 'dan uwanka. Tun kusan Watan January nayi Rubutu akan 'yan Mata masu 'dabi'ar yin Madigo (Lesbian), tun kusan wancen lokaci na samu kira daga wata baiwar Allah Wadda ta bayyanamin Dalilin shigarta harkar madigo da kuma halin da take ciki.

Yarinyar wacce mun dau kusan Mintuna arba'In mun waya ta shaida min dalilin shigarta Harkar madigo, In da ta bayyana min a makarantar gaba da Secondry aka koyar da Ita wannan muguwar 'dabi'ah.
"Bayan kaini makaranta mu hudu ne a dakin da nake, kuma nice karama a duk cikin wayanda muke daki 'daya da su, ranar da nazo na fara fahimtar 'yan Iska ne, domin kuwa a gado 'daya naga suna yin bacci duk da kowace nada nata gado."

"A haka har na fahimci me suke yi domin kuwa wani lokacin a gabana suke sheke ayarsu."
Yarinyar taci gaba da gayamin cewa, a hankali idan suna yi sai taji sha'awa ta taso mata, kwatsam rannan sai suka bukaci ta shiga cikinsu domin jin dadi. Da farko sai ta nuna musu ai ita bata sha'awar wannan mu'amula kuma tana ma son ta chanja 'daki ne domin kada ta takura musu.

Anan ne suka nuna mata ai babu damuwa tayi zamanta a dakin nasu domin halayenta na burgesu.
Kwatsam sai ranan suka nuna mata ai ta shigo cikinsu yafi tunda Allah bai fadi azabar da za'ayiwa mata 'yan madigo ba sai 'yan Luwadi. Sannan kuma tayi wannan shi ya fiye mata da taje tayi zini ko ta aikata Mistabution (ISTIMINA'I).

Ta shaida min da irin wayannan kalamai aka sanya ta a madigo kuma wallahi yanzu bata sha'awar kowane namiji, haka kuma bata sha'awar aure.

Ta kara shaidamin Cewa, Ita kadai ta lalata yara bata san adadiba, kuma yanzu tana son ta tuba amma ba ta san yanda zatayi ba.

Anan na bata wasu shawarwari tare da nuna mata muddin ta mutu bata tuba ba to kuwa akwai matsala domin Allah zai mata Ukuba fiye da yanda take tunani.

Wannan yarinyar tayi godiya ta kuma bukaci duk ranar da na samu lokaci don Allah Inyi fadakarwa game da Irin Wannan 'yan madigon Masu nunawa mutane madigo bai da wata azaba da aka tanadarwa masu yinsa, haka kuma macce zata ji dadi ba tare da ta rasa budurcin ta ba. Bayan Wannan Jiya14 ga watan October Jaridar Aminiya ta fitarda wani rubutuna game da Maza 'yan Luwadi.

Kusan karfe 10 na dare wani bawan Allah ya kirani, daga daukan wayan na san hankalinsa a tashe yake muryarsa na karkarwa. Ya shaidamin yana 'daya daga cikin masu neman Maza kuma kusan Shekarar sai 15 yana wannan lalata yanzu kuma kusan shekarar sa 10 da aure amma har yanzu ya kasa dainawa.
Yace min hakika babu yanda baiyi ba domin ganin ya bar wannan muguwar 'dabi'ah amma ya kasa.
Bayan gama wayar da shi tare da gama bashi shawarori akan ya tuba ya kuma kauracewa wayanda suke wannan ta'adi.

Cen kusan karfe 12 na dare wani ya kirani ya shaidamin daga wata jami'ah (dake arewa ) yake kira na, ya shaidamin yanda aka sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta luwadi (Wa'Iyazubillah).
Ya gaya min Cewa, wani ne ya sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta hanyar nuna masa ya zo su rika yin Romace ba tare da sun sadu ba. Wannan yafi yaje yayi zina.

Ya gayamin a hakan ya amince domin a tunaninsa Romac ba komai ba ne, ya gayamin a cikin Romace din ne kawai wata rana ya afka masa yayi masa luwadi.

Ya shaidamin hakika yanzu baya sha'awar macce, Sai dai maza, yace min wani lokaci har kashisa yake dauka ya shafa a al'aurarsa idan wannan sha'awar ta taso masa (Wa'Iyazubillahi).
Yan da kyau 'Yan Uwa mu rika Kula da Suwa Qannenmu da 'ya'yanmu da Abokananmu ke mu'amula domin gudun yin dana sanin a gaba.

Duk wanda yace maka kazo kuyi romace yafi kaje kayi Zina Wallahi karya yake maka Yana so ne kawai ya halaka maka rayuwa.

Sanan yana da kyau 'yan mata su san cewa, da madigo da Luwadi duka daya ne babu banbanci a wajen Azaba a gobe Qiyama. Sannan yana da kyau su san anya mafi sauri ta kamuwa da cutar Infection Itace ta hanyar yin madigo (lesbian). Su kuma samari su sani daga ranar da aka yi maka luwadi daga ranar Kashi ba zai taba tsayama ba. Daga kaji kashi da yazo.

Sannan masu yi yana da kyau su sani daga ranar da kayi sanadiyar wani fadawa cikin Muguwar 'dabi'ah to kuwa duk lokacin da akayi dashi ko yaje yayi sai an rubuta maka zunubi koda kana Cikin kabari ne.
Wannan Muhimmiyar Sanarwa Ce, Idan ka taimaka wajen Yada ta to ka taimaka wajen ya'da Alheri. Idan kuma ka qi yadawa to ka yi hasarar tarin Ladar da Za'a samu.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 15/10/2015

Tuesday, 29 November 2016

NAZARI AKAN YAWAITAR ZAZZABI (MALERIYA)

HUJEWAR OZONE LAYER YA FARA KAWO ANNOBA A CIKIN AL'UMMA.

Tun Kusan Lokacin da Na samu Labari akan k'aruwar Hujewar OZONE LAYER ( Bargon da ke matsayin kariya tsakanin duniya da kuma cutukkan rana), nake ta tunani akan wannan lamari.
A bangare daya kuma Yawaitar Mace-macen hadi da rashin lafiya da Suke Faruwa a Jahar mu ta Sokoto sai na tsaya nayi nazari tare da Bincike mai zurfi game da Wannan Lamari. Sai naga gaba days an dau wannan matsala kacokan an daurata ga zazzabin Cizon Sauro. Wanda kuwa ga dukkan alamu ba haka lamarin yake ba.

Shi dai Wannan OZONE LAYER masana suka ce abu ne tamkar bargo a sararin saman duniya kuma kariya ne ga (Sama) da kuma Mutane.

Suka kara da Cewa, shi wannan Bargon da ake kira ozone layer, yana shinfide ne a Sararin Samaniya domin ya zama kariya ga halittun kasa daga sinadaran da suke zubowa daga zafin rana wanda zasu cutar da 'dan Adam ta hanyar sanyawa mutane cututtuka (masu wuyar Sha'ani). To idan sinadirai masu cutarwa suka zubo sai su makale a jikin wannan Bargon na Ozone layer.

Babu Shakka Wannan Zance na Masana Ilmin Kimiya ba karya bane game da Wannan Bargon.
Domin tun Kusan Shekaru 1400 da suka Gabata Al-qur'ani Mai Girma ya gaya mana labarin wannan Bargon da ke Sama.A Cikin Al-qur'ani Mai Girma Allah (Swt) Yana Cewa, 

ﻭَﺟَﻌَﻠْﻨَﺎ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﺀَ ﺳَﻘْﻔًﺎ ﻣَّﺤْﻔُﻮﻇًﺎ ۖ ﻭَﻫُﻢْ ﻋَﻦْ ﺁﻳَﺎﺗِﻬَﺎ ﻣُﻌْﺮِﺿُﻮﻥَ

MA'ANA, "Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhali kuwa su daga ayoyinta masu bijirewa ne" (Suratul Anbiya aya ta 31). Sannan a Wata Ayar kuma Allah (Swt) Yana Cewa,

ﻭَﺍﻟﺴَّﻘْﻒِ ﺍﻟْﻤَﺮْﻓُﻮﻉِ


MA'ANA, "Da rufin nan da aka ɗaukaka." (Suratu At-Tur aya ta)
.
A Wani Wuri Kuma Allah (Swt) ya gaya mana Cewa, Wannan bargo kariya ne ga Mazauna kasa.

ﻗَﺪْ ﻣَﻜَﺮَ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻣِﻦ ﻗَﺒْﻠِﻬِﻢْ ﻓَﺄَﺗَﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑُﻨْﻴَﺎﻧَﻬُﻢ ﻣِّﻦَ ﺍﻟْﻘَﻮَﺍﻋِﺪِ ﻓَﺨَﺮَّ ﻋَﻠَﻴْﻬِﻢُ ﺍﻟﺴَّﻘْﻒُ ﻣِﻦ ﻓَﻮْﻗِﻬِﻢْ ﻭَﺃَﺗَﺎﻫُﻢُ ﺍﻟْﻌَﺬَﺍﺏُ ﻣِﻦْ ﺣَﻴْﺚُ ﻟَﺎ ﻳَﺸْﻌُﺮُﻭﻥَ

MA'ANA "Lalle ne waɗanda suke a gabaninsu sun yi makirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsa-shensa, sai rufi ya faɗa a kansu daga bisansu, kuma azaba ta je musu daga inda ba su sani ba." (Suratul An-Nahl aya ta 26).

Friedrich Schonbein Shine mutunen da ya gano Ozone a shekarar 1839, In da a Shekarar 1840 Gordon Miller ya gano amfanin wannan bargo na Ozone layer. Shi dai wannan bargon ya fara hujewa tun kusan shekarun 1980 inda wannan hujewar ta rika fadada tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu, in da a wannan shekarar ta 2016 aka gano wannan bargon yayi qatuwar hujewa.

Masana dai sun riga sun fadi Cewa, Wannan hujewar ta kan iya haifar da kafewar manya da kananan koguna, da kuma karuwar yawan ruwan da ke cikin manyan kogunan
wannan duniya.

Haka Kuma Sun fadi Cewa, Wannan hujewar barazana ce ga lafiyar 'yan Adam din dake rayuwa a wannan duniya musamman sassan duniyar dake fama da yanayin zafin rana. Domin ana samun karin sabbin cututtukan da suke da alaka da fata masu Wuyar magani.

Wannan abu hakika ya fara tabbatuwa domin kuwa a watan juli din wannan shekara ta 2016 (Wato July 2006), a North America an samu mutuwar a kalla mutane 225. Wanda kuma duka bincike ya tabbatar da cewa, dukansu sun samu cutukkane ta dalilin yawan zafin rana.

Haka Wannan Annoba ta mace-mace da rashin lafiya ta yawaita a Wani kauye dake Cikin Erteria In da kusan Sai da 'yan kauyen Suka yanke kauna da rayuwa. Kwatsam kuma Sai gashi Wannan Annoba ta Rashin Lafiya da Mace-mace Sun yawaita a Cikin Tsakiyar Garin Sokoto In da a Rana 'daya zakaji an Rasa fiye da Mutum 50. Babu Shakka Annoba Jarabawa Ce Da Allah Ke yiwa Bayinsa Ko dai don Ya Jarabesu ko Kuma don Gargadesu akan Su tuba daga miyagun laifuka.

....Subhanallah!!!
Jamilu Sani Rarah Sokoto
Wed 26/10/2016