Saturday, 20 February 2016

SAKO ZUWA GA MATASA

SAKO ZUWA GA MATASAN AREWA.
*********
Dukkan Godiya ta tabbatta ga Allah Ubangijin halittu. Salati da sallama su kara tabbata ga shugaban Manzanni, Muhammadu 'dan Abdullahi tare da iyalanSa da sahabbanSa da duk wayanda suka bi tafarkinsu har ya zuwa ranar Sakamako.

Wannan Sako Nawa ya shafi dukkanin Matasa 'yan Arewa musamman ma masu kishi tare da kaunar Arewa a zukatansu.

Hakika abinda ke faruwa a Facebook, Instagram, Twitter yana daga cikin dubban abubuwan da ke kawo matsala tare da tawayar arzikin da muke fama da su a halin yanzu.

Hakika ina lura tare da kula da cewa, babu wata rana ko wani dare da zan hau social media ba tare da na tarar wani ya aibata Shugaba Buhari ko wani daga cikin 'yan adawa ba.

Hakika zagin juna da cin mutuncin juna na daga cikin abubuwan da ke kawo matsala a wannan rayuwa da muke ciki.

Wani daga ya hau Facebook ba zaka ji ya fadi wata kalma ta alkheri abakinsa ba kawai zaka ji yana kokarin ci mutuncin da zagin 'yan adawarsa ne tare da kirkiro wasu maganganu marar tushe ya saka a bayanan nasa.

Ta 'bangaren Masoya Shugaban kasa Buhari zaka ji suna fadin, Rusashsiyar jam'iyar PDP, ko kuma Jam'iya mai kashin Mutane, ko kai tsaye kaji mutum yace, Jam'iyar kafirai.

To meye amfanin wannan? Ta bangaren 'yan jam'iyar ta PDP kuma zakaji suna Cewa, Tsohon nan ya kawo talauci, Tshohon nan yawonsa yayi yawa, Tsohon nan bazai iya gyara ba. Da dai wasu zan tuka marar amfani.

Shin ko mun Manta Abinda Allah (swt) ke fadi a citkin Alqur'ani mai Girma? Cewa, "SHIN BAKA GANI BA, YADDA ALLAH YA BUGA WANI MISALI; KALMA MAI KYAU, KAMAR BISHIYA CE MAI KYAU; TUSHENTA YANA TABBATACCE, RESSANTA KUMA SUNA CIKIN SAMA* TANA BAYAR DA ABINCINTA, A KOWANI LOKACI DA IZNIN UBANGIJINTA" (Suratul Ibrahim aya ta 24 zuwa 25).

A wani hadisi kuma Manzon Allah (saww) Cewa yayi, Sadaka ta zama wajibi a kan kowani Musulmi, Sai aka ce: To idan bai samu abin sadakar ba fa? Sai ya ce: Yayi aiki da hannayensa; sai ya amfanar da kansa, ya kuma yi sadaka. Sai aka sake tambayarsa: To idan bai samu iko ba fa? Sai ya ce: Ya taimaki ma'abucin buqata; wanda aka zalunta. Sai aka ce masa: To idan bai samu iko ba fa? Sai yace: Ya yi umurni da kyakkyawa, ko da alkhairi. Sai aka tambaye shi: To idan bai aikata ba fa? Sai ya ce: Sai ya kame daga aikata sharri; don yin hakan sadaka ne ".

Shin me yasa muke aibata 'yan uwanmu maimakon muyi shiru ko dan yin hakan ya zama sadaka a garemu?

Kusani ya Matasa Manzon Allah (saww) ya zo ne don ya zama aminci da rahama; kuma don ya tsamar da Mutane daga duhu zuwa ga haske. kamar cika alqawari, hana zalunci tare da qetare iyaka, da tsayar da adalci, da tunkude zalunci.

Ya kai me kiran PDP da Rusasshiyar Jam'iya, Ya kai mai Kiran Shugaba Buhari ya kashe Nigeria muyiwa Allah mu daina ko abubuwa zasu mana sauki.

Allah (Swt) Yana Cewa, "AKWAI TSAMMANIN UBANGIJINKU YA HALAKA MAQIYANKU, SAI YA BAKU MAYEWA A DORON QASA, DON YA GA YAYA ZAKU AIKATAWA (Suratul A'araf aya ta 129).

Hakika dukkan 'yan adawarku su mutu a barku a cikin duniya ba zata karaku da komai ba hasalima babu wani abu da zaku karu da shi sai hasara da tabewa (Allah ya tsare mu).

Ya 'dan uwa matashi kada arude ka da siyasa kaje ka manta dalilin da yasa aka halicce ka a duniya.

Da wannan Nake Rokon Matasa akan mu daina aibata junan mu saboda wani banbanci na siyasa

Haka kuma ina kira ga Shuwagabannin da suyi qoqarin tabbatar da zaman lafiya; ta hanyar tsayar da adalci, tabbatar da gaskiya. Kuma shugabani yakama ta su san wajibi ne  akansu su yi qoqari wajen aikata duk abinda zai amfani talakawa, da tunkude musu abinda zai cutar da su a cikin addininsu da duniyarsu.

Yana da kyau Malamai su san cewa, sune halifofin Manzanni, kuma magada Annabawa. Don haka wajibi ne akan ma'abuta ilimi su kare al'umma daga cutar jahilci, ko rugujewar aqidu da
lalacewansu. Sannan su riqa
haskaka hanyoyi ga Mutane ta
hanyar fada musu duk wasu abubuwan da suka shige musu
duhu.

Wajibine su tashi tsaye wajen ilmantar da Mutane lamuran addininsu da Siyasa; Saboda shi malami yana gyara abinda Mutane suka bata ne, yana! kuma fadakar da su zuwa ga alkhairi, tare da yin umurni da kyawawa, da kuma hani kan munana.

Ina Rokon Allah ya amfanar da mu Tare da Amintar damu aduk inda muke.

Allah (Swt) a cikin Alqur'ani Mai Girma yana Cewa, "Ya ku Mutane lallai ne alkawarin Allah gaskiya ne; kada rayuwar duniya ta rude ku, kuma kada mai rudi (wato Shedan) ya rude ku daga
Allah" (Suratul Luqman ayata 33).

Jamilu Sani RARAH
Sat 20/02/2016.

Friday, 19 February 2016

MAHAIFIYA MAI ABIN MAMAKI

MAHAIFIYA MAI ABIN MAMAKI
**********
Na tsaneta. tsana ta hakika har bana son naganta, aikinta shine dafa abinci ga malamai da dalibbai .domin ta tallafawa karatuna.

Akwai wata rana da ta je har ajin mu (Class) saboda ta ganni ta tabbatar da lafiya ta, "YA ZA'AYI TA MIN HAKA TAZO WAJENA BAYAN TA SAN YANDA NA TSANETA?" haka na fa'da a zuciya ta.

Lokacin da tazo ajin namu ta min magana amma nayi kamar banganta ba. Ta dage da yi min magana anan ne na juyo a fusace, na gaggaya mata ba'kaken maganganu masu zafi, Na fita ajin da gudu raina a 'bace.

Washe gari na shigo makaranta kenan sai na hadu da wani 'dan Class din mu nan take ya bu'da baki yana cemin, "Eeey Mahaifiyarsa ido 'daya ne da ita"

Anan naji kamar in yiwa kaina kabari saboda bakin cikin wannan magana da yayi min, nan take na juya na koma gida wajen Mahaifiyata nace da ita, "IDAN DAI DON KI SAKA ANA YIMIN DARIYA NE ME ZAI HANA MA KI MUTU IN HUTA DA KE"

Mahaifiyata dai bata ce min uffan ba, har na gama gaggaya mata magana na wuce abina.

Allah ya yini mai basira sosai da sosai kuma na dage da karatu babu kama hannun yaro.

Ana haka kawai sai Allah ya kawo wata kungiya a makarantar mu masu bawa yara masu basira scholar ship zuwa kasar waje domin yin karatu.

Aka yi jarabawa Allah ya bani sa'a naci jarabawar, anan ne aka 'dauke ni aka kaini kasar Singapore domin yin karatun nawa.

Da yake ni mutum ne mai basira da hikima Allah ya taimake ni har na samu kammala karatuna ban dawo ba, cikin taimakon Allah na samu aiki a cen Singapore din.

Topa daga nan ne na samu sa'a domin bada dadewa ba na mallaki gida nawa na kaina a kasar ta Singapore daga bisani na nemi mata a cen aka daura mana aure da ita.

Na 'dau shekaru da aure har Allah ya albarkace ni da 'ya'ya ina jin dadin rayuwa cikin iyalin nawa, kwatsam wata rana mahaifiyata tazo ziyarata a Singapore.

Ina zaune a falo 'dana na fari (my fist born) yana wasa, mata ta tana kitchin tare da 'dana na biyu, kawai sai naji mutum a kofar gida ma'ana yana so a bashi umurni ya shigo.

Nan take 'dana na fari ya ruga da gudu yaje ya bude kofar ai kuwa yana budewa sai ya fara kuka, nan da nan na iso kofar bada shiri ba (domin) in gani meke faruwa yake kuka.

Me zan gani kawai sai naga mahaifiyata a tsaye (ashe abinda ya saka 'dan nawa kuka ganinta da yayi da ido dayane).

Anan na fara yi mata kururuwa tare da ce mata, "YA ZA'AYI KIZO GIDANA KI TSORATA MIN 'DANA? MAZA KI 'BACE MIN DA GANI".

Mahaifiyar tawa cikin sanyin hali tace dani, "YI HAKURI A SHE NAYI KUSKUREN GIDA NE. ( MA'ANA, BA NAN NE NAKE NEMA BA)". ta fita ta yi waje. Ban san ya akayi tazo Singapore ba, ban kuma tambaye ta ya akayi ba bare har in bata ruwa da abinci.

Wata rana an shirya taro a makarantar da na fara karatu, sai aka gayyaceni.

Na tashi na shirya tsaf na yanki tacket din jirgi na sauka kasar mu, bayan sauka ta a kasar sai na yanke shawarar bari in tafi tsohuwar unguwar tamu.

Bayan naje unguwar sai na samu gidan namu a rufe, ba tare da bata lokaci ba na tambayi makwaftanmu labarin mahaifiyar tawa.

Sai suka gaya min cewa ai ta mutu tun kusan wata 2 da suka wuce. Banji wani ciwo ba lokacin da suka gayamin bare inyi hawaye.

Na juya haka sai suka ce min, ga wata takarda da tasa a rubuta mata a lokacin da take cikin rashin lafiya.

Na karbi takardar na fara warware wa a hankali, nan take na fara karanta rubutun da ke cikin takardar.

YA 'DANA!

A KO DA YAUSHE TUNANINKA NAKE, INA MAI BAKA HAKURI DA NAJE GIDAN KA A Singapore KUMA NA BAWA 'YA'YANKA TSORO, NAJI DADI KWARAI DA GASKE LOKACIN DA SHUGABAN MAKARANTARKU YA GAYA MIN ZAKA ZO TARO, SAI DAI KUMA KASH! BANDA LAFIYAR DA ZAN IYA ZUWA DOMIN IN GANKA.

INA BAKA HAKURI AKAN DARIYAR DA ABOKANANKA SUKE MA SABODA NI. HAKIKA ZAN GAYA MAKA WANI SIRRI WANDA BAKA SANI BA.

A LOKACIN DA KANA YARO KARAMI BAKA MALLAKI HANKALINKA BA KA SAMU HATSARI WANDA YA KAI HAR KA RASA IDO DAYA.

KASAN CEWA LIKITAN YACE ANA IYA SAKA MA WATA TAYI LAFIYA QALAU, NI KUMA A MATSAYINA NA MAHAIFIYA SHINE NA BAKA TAWA NI NA ZAUNA DA IDON 'DAYA.

INA FATAN ZAKA KULA DA JIKOKINA, ALLAH YA YIMA ALBARKA.

NOTE:-
﹏﹏﹏
Wannan Labarin ya faru da gaske a Kasar Nepal, Ina fatan Zamu kula da irin Soyayyar da iyayen mu suke mana.

Jamilu Sani RARAH
TUE 16/02/2016.

Sunday, 14 February 2016

RANAR MASOYA TA DUNIYA

VALENTINE DAY BA DANI BA.
*********
Kasan Cewa Ruwayoyi sun banbanta game da ainahin dalilin da yasa ake wannan Biki na Ranar Masoya wasu suka ce;

Valentine sunan wani shahararren malamin kiristoci ne wanda ya rayu a shekaru masu yawa, zamanin Claudius II Sarkin Rome.

Wata Rana Sarkin Rome, Claudius II ya sanya dokar hana sojoji yin aure wai a ganinsa aure zai shagaltar da su, kuma ya kau da tunaninsu daga yaki.

Shi kuma Valentine ya bijire wa wannan doka ta Sarki, kuma ya ci gaba da daura wa sojoji aure a boye ba tare da an sani ba.

Da sarkin ya gano, sai ya jefa shi cikin kurkuku, kuma ya yanke masa hukuncin kisa.

Yana cikin kurkuku ne ya kamu da ciwon son `yar sarkin, amma a boye, duk da cewa haramun ne ya so wata mace ko kuma ya yi aure, a matsayinsa na babban malamin kirista, kasancewar dokokin kiristanci sun hana.

Kasancewar Sa Babban Malamin Kiristoci sarkin Romawa ya nemi Valentine ya bar kiristanci, ya bauta wa gunkin Romawa, shi kuma zai mai da shi daya daga cikin makusantansa kuma ya aurar masa da 'yarsa.

Shi kuma Valentine ya ki yarda da haka, Sai sarkin yasa aka kashe shi a ranar 14 ga Febreru 270 CE, a daren 15 ga watan Febrerun da aka saba yin wani bikin wai Lupercalis.

Daga nan aka canza sunan bikin ya koma ranar tunawa da Malam Valentine, wai saboda dagewar da ya yi a kan kiristanci, wasu kuma suka ce a'a saboda goyon bayan da ya nuna wa sojojin da suka fada cikin soyayya, har hakan ya kai shi ga rasa ransa.

Daga nan, sai Pope, shugaban kiristocin da ya gaji Saint Peter, ya mai da ranar 14 ga Febreru 270 CE a matsayin ranar bikin soyayya, kuma ya shar’anta wa duk kan kiristoci murnar zagayowar wannan rana a kowace shekara.

To In dai Haka ne Ni Jamilu 'dan Sani Jikan Adamu Jikan Isah me zai saka ni murnar wannan Rana?

Shin ko 'yan uwa zasu tuna da wani hadisin Annabi (Saww) wanda yake Cewa, KUYI SALLA DA TAKALMI KO SAU DAYA NE A RAYUWARKU DOMIN KU SA'BAWA YAHUDAWA?

A wani hadisi kuma yace, KADA KU ASKE GEMU KU BAR GASHIN BAKI DOMIN YAHUDAWA NE KE YIN HAKA.

A wani hadisin kuma, umurtar mu yayi da cenja kalar farin gemen mu domin mu sa'bawa yahudawa.

Bikin valantine biki ne da ya kunshi kamanceceniya da mushrikan Romawa da kuma tarayya da kiristoci.

Sanin kan ku ne Yin kamanceceniya da kafirai ko tarayya da su a cikin addininsu ko akidarsu ko ibadarsu ko wata al’ada da ta kebanta da su, haramun ne Ina Rokon Matasa da kauracewa wannan Bikin.

#NoForValanTineIamMuslim.

Jamilu Sani RARAH
14/02/2016.

Saturday, 13 February 2016

ME YASA HAKA 'YAN AREWA?

ME YASA HAKA 'YAN AREWA?
********
Malamai masana suka ce, "IDAN HAR A LOKACIN DA KAKE CIKIN FARA'A DA ANNASHUWA BAKA TUNA ALLAH BA ME YASA A LOKACIN DA WANI ABU MARAR DADI YA SAMEKA ZAKA TUNA ALLAH?"

So da yawa nake mamakin 'yan arewa a lokacin da Allah ya azzurtasu ya kuma wadata musu aljihunsu bazakaji sunyi godia tare da neman mai neman taimako ba don su taimake shi, amma daga ranar da baida kuddi zaka ji shi yana ta ganin laifin mutane tare da yin tsinuwa ga wasu.

Babu shakka wannan mulki na Shugaban Kasa Buhari wasu daga cikin talakawa dama wasu wayanda ba talakawa ba na cikin wani hali na rashi.

Shin tsinuwa ce zata fitar da mu daga wannan halin? Sam tsinuwa da munanan kalamai ba sune mafita ba.

Wata Rana Annabi (saww) yana tafiya tare da Sahabbansa (RA), wani daga cikin sahabban Rakuminsa yaqi tafiya sai wannan mutumen ya tsinewa rakumin nasa tare da la'antarsa.

Nan take Annabi (saww) yace a dakata. Bayan an dakata sai Annabi (saww) ya dubi sahabin yace, to tunda ka tsine masa ka sake shi ya shiga daji hakika mu ba zamuyi tafiya da tsinanne ba.

Wannan ta sa dole wannan mutumen ya saki wannan rakumi ya shiga daji, suka ci gaba da tafiya.

Da yawa daga cikin mu 'yan Arewa mu ke janyowa kan mu matsala, tun mulkin Goodluck Jonathan har zuwa yanzu Mulkin Buhari 'yan Arewa sune kan gaba wajen 'bata lamarin mulkin kasar nan.

Hakika cenja halittar shugabanni ta hanyar mai dasu siffar mata ko wata kaskantacciyar siffa na daga cikin abinda ke 'bata mulkin kasarnan.

Hakika ina bakin ciki yanda wasu ke cenja siffofin shuwagabannin Kasarnan, da wannan nake son tunatar da mu hadisin Annabi (saww) da ke cewa, Allah ya tsinewa ya koma ya tsinewa namiji mai cenja siffansa zuwa siffar mata, haka kuma ya tsinewa duk maccen da ta siffantu da siffofin maza.

Ka sani ya kai 'dan uwa a lokacin da ka dauki photon wani ko wata ka cenja masa fasali zuwa macce ko namiji to wannan tsinuwar zata hau kanka ne.

Jamilu Sani RARAH
Sat 13/02/2016.

TAIMAKO MAI DADI

WANNAN LABARIN YA FARU DA GASKE
*********
An yi wani mutum a Egypt, wannan mutumen ya kasance yana da matsalar ciwon zuciya. Ya kama hanya yaje asibito domin a duba shi.

Bayan gama yi masa dukkanin gwaje-gwaje (medical cheak up), sai likitan ya ce da shi, "HAKIKA DUKKAN JIJIYOYIN DA KE KAI JINI A ZUCIYARKA BASA KAI JININ YANDA YAKAMATA."

Mutumen ya dubi likita yace da shi, To me zai hana ayi min tiyata ko zan samu lafiya? Likitan ya shaida masa cewa, akwai wani likita gwani a wannan fanni dake zaune a kasar Germany don haka kaje wajensa zai yima wannan tiyata.

Bayan 'yan kwanakki wannan mutumen ya tashi daga Egypt zuwa Germany, bayan ya sauka yaje masaukinsa ya kwata.

Da wayewar Safiya wannan mutumen yaje ya samu likitan, likitan ya shaida masa cewa, Hakika na dau shekaru ina wannan aikin wasu ana samun nasara wasu kuwa ba'a samun nasara, don haka idan ka amince kaje jibi ka dawo in yima aiki.

Bayan kwana biyu wannan mutumen ya koma wajen likita tare da neman uzuri akan ya bari ya koma gida domin ya biya bashin da ake binsa kuma yayi ban kwana da matarsa da 'ya'yansa da iyayensa da sauran 'yan uwa.

Likita yace, ba damuwa, wannan mutumen ya koma gida (Egypt), bayan komawarsa gida da kwana biyu yana tafiya a dai-dai wata tashar mota kawai sai ya ga wata tsohuwa tana tsintar kashin da aka ci aka raga wajen wani mai sayarda nama.

Wannan mutumen yaje ya tambayeta dalilin da yasa take tsintar wayannan kasusuwan, sai matar ta buda baki tace da shi, "YAU KUSAN SHEKARA BIYU HAKA MUKE CIN NAMA NI DA 'YATA (MARAINIYA), SABODA BAMU DA KUDDIN DA ZAMU SAYI NAMAN."

Daga jin hakan wannan mutumen ya cewa mai sayarda naman, Zan biyaka kuddi ka rika ba wannan mata nama kullum har tsawon shekara daya.

Nan take wannan matar ta fara yi masa addu'ah, "Ya! Allah ka baka lafiya da kai da iyalinka, ya Allah ka biya maka bukatunka duniya da Lahira" Wannan mutumen ya wuce zuwa inda zashi.

Bayan ya koma gida sai 'yarsa tace, Baba wallahi naga komai naka ya cenja, hakika yau na ganka cikin fara'a, meke faruwa?

Ya bata amsa akan babu abinda ke faruwa, bayan ya gama abubuwan da yake kwana biyu yayi sallama da gida ya koma zuwa kasar Germany domin aiki.

Bayan yaje wajen likita sai likitan ya kara yi masa wasu gwaje-gwaje wanda daga sune za'a shiga yi masa wannan tiyatar.

Lokacin da likitan ya gama gwaje-gwajen da yake sai ya tambayi mutumen, Wace Asibiti kaje? Mutumen yace, Babu asibitin da naje.

Likitan yace, A'a kada muyi haka da kai hakika kaje wata asibiti sun baka wani magani domin duka jijiyoyin da suka rufe yanzu sun bude don haka baka bukatar aiki (operation).

Mutumen yayi murmushi yace, "HAKIKA NA SAN WANDA YA WARKAR DA NI, SHINE ALLAH. SABODA NA TAIMAKI WATA MATALAUCIYAR MATA LOKACIN DA NA KOMA".

Allahu akbar, Shin 'dan uwa Sau nawa ka bada sadaqa a rayuwar nan ta duniya?

Hakika An karbo Hadisi daga Abu Huraira (rta) yana Cewa, Manzon Allah (Saww) Yace, Sadaqa bata rage yawan dukiya, babu wani daga cikinku wanda zai yafewa 'dan uwansa face shima Allah ya masa gafara, sannan ba wanda zaiyi tawali'u (gaskantar da kai ga Allah) face Sai Allah ya daukaka darajarsa.

Don Girman Allah mu rika lura da Almajira da mabukata, kai kana zamanka hankali kwance kaci mai kyau ka sha mai kyau wallah daga cikin mabukatan nan akwai wanda bai ta'ba cin abinci mai dadi ko 'dan'dano ba.

A kula da mabukata ko za'a samu biyan bukata.

Jamilu Sani Rarah
Sat 13/02/2016

Sunday, 7 February 2016

YARE NA YA FIYE MIN WANI YARE CEN

YARENA YA FIYE MIN YAREN WASU CEN DABAN
*********
Mala Ahja Ta ta'ba tambaya ta akan cewa Me yasa na ke son yin rubutu da Yare na, maimakon in rika yi da turanci kowa ma ya fahimta har wayanda ba 'yan yare na ba.

Ban bata amsa ba kawai cewa nayi "HUMMM". Kawai yare na na burgenine.

Nusaiba  'yar yaya ta ce shekarun ta 7 da haihuwa. Wata rana mamarsu ta gargade Nusaiba da yayyenta kada taji wani daga cikinsu yayi yaren Hausa duk wanda yayi zai bada tara.

Haka kuwa akayi saboda Biyayyar yaran dukkansu suka daina hausa suka rika yin turanci.

Ana haka kawai sai ga almajiri ya shigo gidan yana rokon a taimake shi da abinci duk yanda yake yunwa yake ji.

Mahaifiyar Nusaiba ta ce, Nusaiba je kice wa almajiri yayi hakuri yanzu muka dawo daga cikin gari. Wannan maganar da harshen turanci mahaifiyar Nusaiba ta yi mata ita.

Nusaiba cikin ladabi taje har gurin almajiri tace, "PLEASE MY MOTHER SAY I SHOULL TALL YOU WE DO'NT HAVE FOOD...." kafin Nusaiba ta gama bayanin ta nan take wannan Almajirin ya mika mata kwanonsa (a tunaninsa abincin zata bashi).

Babu shakkah wannan abin ya fahimtar dani dalilin da yasa nake rubutu da Hausa.

Babban dalilina shine ina cikin hausawa kuma ina son in habaka yaren nawa ina kuma bukatar wani yare yaji sha'awar yarena.

Hakika da ace da hausa Nusaiba ta fada wa wannan almajirin zai fahimta, amma da yake bada yarensa ta yi masa bayani ba sai ya kasa fahimta.

A cen da Kusan duk wani ilimi na kimiyya ko fasaha ko kuma na ci gaban al’umm a Larabce yake, kuma dole ta sa Turawa
suka yi amfani da nakaltar Larabci don cin moriyar ilimin da ke kumshe a cikin littattafan Larabawa da ke mulkin duniya a wancan lokaci.

Daga baya ne Turawa suka fahimci cewa ai yawancin ilimin da Larabawa ke takama da shi su ma sun kwaso wasu ne daga littattafan Girkawa, don haka suka yi watsi da na Larabawa suka koma wa na ainihin, ta haka ne mallakar da Larabawa suka yi wa duniya ta subuce ta koma ga Turawa, musamman na Ingila.

Ni dai na kasance ina yin rubutu na badan kowa ba sai dan mutanen mu Hausawa kuma ina so su fahimta da kyau.

Rokona gareku yan uwa kai ma in dai har da malam Bahaushe kake magana ko kuma rubutu, to ya dace rubutun nan naka ya kasance a cikin hasrshen da mutanenka za su gane, za su fahimta, za su kuma yi aiki da shi.

Ina Rokon Allah ya daukaka Musulunci da Yaren Hausa.

Jamilu Sani RARAH

Saturday, 6 February 2016

SAN WANI ABU GAME DA MUFTI MENK

SAN WANI ABU GAME DA MUFTI MENK
*********
A musulunce idan aka kira mutum da suna mufti to ana nufin shahararren mai bada fatawa game da hukunce-hukuncen da suka shafi addinin musulunci.

Ba za'a bawa mutum mufti ba face sai ya kasance sananne a kowane fanni na musulunci. Hakika idan za'a bada wannan kujera ta mufti sai an tara dukkanin malaman kasar daga kowace akida. Idan har sun yarda to sai a bawa mutum wannan kujerar ta mufti. Idan kuma basu yarda ba sai mutum yayi zamansa a matsayin Shiekh.

Mufti menk cikakken sunansa Ismail sunan mahaifinsa musa Menk an haifeshi a garin Harare dake kasar Zimbabwe.

Ya fara hardar alqur'ani mai girma a gaban mahaifinsa tun yana da shekara tara a duniya ya samu nasarar hardace shi yanada shekara goma sha biyu (9 to 12 years).

Mufti menk ya samu ilmin addini sosai a wajen mahaifinsa shiek Musa wanda shima shahararen mai bada fatawa ne a kasar ta zambabuwie kuma mabiyin mazhabar Hanafi.

Daga nan mufti menk ya samu tafiya jami'ar musulunci ta dake saudia in da ya karanci fannin sharia wanda kuma dama shi ya karanta a wajen mahaifinsa.

Daga nan kuma ya koma kasar india ya karanci ilmi fiqhu (Jurisprudence), mufti isma'il ya kasance mai sauqin kaine da kuma girmama mutane ko wayanni iri (ma'abota musulunci da ma wayanda ba musulmai ba).

Dama ance 'daukaka bata zowa mutum a banza ba tare da anjarabeshi ba

A watan augusdin shekarar 2014 wasu gungun marasa imani suka kai gagarumin hari da mufti da niyar hallaka shi amma Allah cikin ikonsa ya tsare mufti daga kai dinsu.

Yanda abin ya faru, wata rana ne da yamma mufti menk yaje domin ya saye wani abu kamar yanda ya saba. Bayan ya kare sayayyar ya shiga motarsa direbansa ya ja mota sun fara tafiya kenan sai suka tarar da gungun wasu mutane suna jiran isowarsa domin su gaisar da shi.

Suna isa gun mutane sai Mufti ya saukarda glass din motarsa tare da yi musu sallama, hadi da mika musu hannu domin suyi musabuha.

Mufti na tsakiyar gaisawa da mutane sai wani mutum daga cikin mutanen ya fara zagensa yana Cewa, "KAI MAQIYI ANNABI NE KAFIRI KAWAI."

Mufti baice masa uffan ba a na haka sai kawai 'yan uwansa sukazo dauke da bindigogi da niyar su harbi mufti nan take mufti ya taka su mufti suka fice da gudu su kuma wayannan mutane suka rinka harbin motar, cikin tsarin Allah mufti ya tsira daga kaidinsu.

Babu shakka irin haka tayi ta faruwa ga mufti amma bai ta'ba nuna damuwarsa ko jin tsoro ba, haka kuma hakan bai hana shi ya'da da'awa ba.

Duk lokacin azumi mufti yakan ha'da kayansa yaje 'kauye me nisa daga birnin domin ya gabatar musu da tafsiri domin su san yana kaunarsu.

Wani abin mamaki ga mufti kuma idan aka gayyace shi ako wane gari yakanje kuma baya bukatar ace sai an tara masa kudade kafin yazo a gari komai nisan garin.

Abin mamaki kowa da inda yake karar da lokacinsa, wani a wajen alkheri wani kuma awajen sharholiya to shi mufti gaba daya lokacinsa da dukiyarsa ya sadaukar da sune akan 'daukaka kalmar Allah.

Kusan sati 3 ko ma fiye da haka mufti ya kasance a hanyar ya'da da'awa, daga kasar philipps ya taso yazo senghpor daga cen ya taso sai nigeria.

A wannan zuwa da yayi a nigeria ya so ya ziyarci wasu jahohi domin sada zumunci da kuma gabatar da lecture kamar yadda ya gabatar a kano, amma wasu abubuwa sun hana shi ciki wannan gurbi.

Ranar jumu'ah (jiya kenan. 05/02/2016) na bukaci ina son mu hadu da shi a zahirance nan take mufti ya bukaci in bashi number wayata domi munyi waya misalin karfe daya na rana a daidai lokacin da yake shirin tafiya gabatar da sallar jumu'ah a B.U.K da ke kano ya kirani muka dauki kusan mintuna 04 muna waya da shi.

Kwarjinin mufti ya sakani kasa sakin jikina inyi magana da shi yanda ya kamata, da ya fahimci haka sai ya gayamin cewa, idan har ina da wata bukata kada in damu zan iya tuntubarsa a koda yaushe da wannan layin da ya kirani da shi.

Daga baya na tura masa tex akan cewa muna gayyatarsa zuwa sokoto, sai bai min replay ba sai jiya assabar karfe takwas na dare mufti sai ga kiran mufti.

Bayan na 'dauka na masa gaisuwa cikin girmamawa ya gayamin cewa yaga tex messege dina amma kuma yana bani hakuri da sauran 'yan sokoto akan cewa ba zai samu zuwa ba amma ya min alkawari akan cewa nan da sati biyu zai sake tuntubata ya gani ko akwai yiwuwar ya zo sokoton.

In shaa Allahu mufti zai bar nigeria a yau lahadi tare da kewar kanawa, hakika mufti ya ji dadin zuwa kano tare da alfahari da matasan kano akan yanda ya ga suna so da kaunar addini.

Hakika na samu karantar wasu daga halayen mufti sosai da sosai. Na farko shahararren malamine, mai kuddine, ya shahara a wajen wa'azi ya shahara a wajen sarrafa yaren larabci da kuma turanci.

Mufti komai talaucinka koya shekarunka suke zaiyi mu'amula da kai ta kamala kamar yadda yake yi da kowa.

Wani abin sha'awa game da Mufti lokacin da zai fara gabatar da lecture sai da ya yi hausa.

Ina Rokon Allah ya albarka ce mu da ire-iren mufti a nigeria. Kuma Allah ya saka masa da mu kanmu da alkhairi duniya da lahira.

Jamilu Sani RARAH
Sun 07/02/2016.

Wednesday, 3 February 2016

ZUWA GA 'YAN GANI KASHENI BUHARI

ZUWA GA 'YAN GANI KASHENI BUHARI
*******
Da yawa daga Cikin Mu 'yan Nigeria Mun Jahilci Menene SO? mun Kuma Jahilci Menene Gaskiya.

Wataran masoyinka sai yayi kuskure, kuma ka sani sai soyayya ta rufe maka ido ka kasa ganin wannan Kuskuren  Nashi.

Kamar yanda Watarana makiyinka sai yayi daidai, amma kiyayya ta rufe maka ido sai ka Nuna Kuskure yayi.

Abinda zamu duba a nan shine duk kiyyayar da Allah yake yiwa
yahudawa amma da aka sami masu rike amanar kudi a cikinsu sai da Allah ya fada.

Haka kuma mu duba irin soyyayar da Allah yake yiwa Annabi (saww), amma da makaho yazo wajensa ya daure fuska sai da Allah ya fada.

Mu tuna yadda Annnabi (Saww) yake son Nana Aishah (Ra), har an taba tambayars Cewa, Wakafi So ya Rasulillahi? Ya bada amsa cewa, "AISHA, A CIKIN MAZA KUMA MAHAIFINTA (Sayyidina Abubakar (Ra))", amma Annabi (saww) yace, da zata fasa kwanon Nana Safiyya (RA) da sai ta biya.

Nana Aisha (RA) da kanta take Cewa, Wata rana Manzon Allah (saww) zai fita daga gida, sai ya tuna da Khadijah, ya fadi wasu
kalmomi na girmamawa gare ta. To amma sai na gagara rike kai na sai na ce masa; 'Ita dai ba wani abu ba ne face tsohuwar mace, kuma a halin yanzu Allah ya musanya maka wadanda suka fi ta'.

Nan take Manzon Allah (saww) ya maya min da martani, cikin fushi yana cewa: "Lallai ba haka ba ne...lalle ban samu wadanda suka fi ta ba. Don kuwa ita ce ta yarda da Annabcina a lokacin da kowa ya kyale ni. Ta ba ni dukkan dukiyarta a lokaci mafi tsanani (na bukatuwa da su).

Kuma Allah Ya ba ni zuriya ta hannunta, alhali kuwa ya haramta min daga wasunta".

Lalle Wannan Kadai Zai saka mu fahimci Cewa, Fadin Gaskia ga Masoyi Shine Cikakken So, ba boye Gaskia ba.

Sannan Allah (swt) yana umurce mu da fadin Gaskia ko da akan kan mune.

Manzon Allah (saww) yace: "ku
lamunce min abu shida (6) zan lamunce muku shiga Aljanna:

(1) Ku rinka fadar gaskiya. (2) ku rinka cika alkawari. (3) Ku rike amana. (4) ku kame kanku. (5) Ku kame hannuwanku daga abubuwan da ba naku ba".
(Ahmad 5/233/323).

Don haka mu rika Fadan Gaskia akan kowa komai ma tsayin mu, Idan kuma muna tunanin sai mun qi fadin gaskia zamu samu abinci to mu Muji tsoron Allah, FATTABU INDALLAH, Munema A wajen Allah, domin shine me bayarwa da hanawa.

Allah yasa Mu dace.

Jamilu Sani RARAH
Fri, 01/01/2016.