Wednesday, 30 November 2016

LABARIN YAJUJ WAMA JUJ

LABARIN YAJUJU DA MAJUJU.
*********

 
Allah (Swt) a Cikin Al-Qur'ani mai Girma Yana Cewa;

ﺣَﺘَّﻰ ﺇِﺫَﺍ ﻓُﺘِﺤَﺖْ ﻳَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻣَﺄْﺟُﻮﺝُ ﻭَﻫُﻢ ﻣِّﻦ ﻛُﻞِّ ﺣَﺪَﺏٍ ﻳَﻨﺴِﻠُﻮﻥ


Ma'ana "Har sa'ad da aka bude Yajuju da Majuju alhali kuwa suna gaggawa daga kowane tudun kasa." (Suratul Anbiya aya ta 96(

Yajuju da Majuju, tsatso ne, na daya daga cikin ‘ya'yan Annabi Nuhu (Alaihis Salam).

A zamanin Annabi Ibrahim (Alaihis Salam) da akwai wani sarki da ake kira da Zulkarnaini, shi wannan sarki, Allah ya bashi iko da kuma Mulki tun daga Bangon Gabas har zuwa yamma.

Shine mutumen da ya zagaye duniya tun daga farkon Inda rana take fitowa har Inda take faduwa.
Wasu ma suna ganin Zurkarnaini Annabine, amma dai maganar gaskiya zurkarnaini Sarki ne kuma mutumin kirki ne da ya shimfida Adalci, shine ya gina wannan Katanga da ta raba wannan duniya da Yajuju da Majuju. Haka kuma, wannan Katanga an gina tane da narkakken karfe da
duwatsu da kwalta da ruwan dalma.

A zamanin Zulkarnain wadannan al’umma (Yajuju da Majuju) sun addabi mutane, shine al’ummar da
Zulkarnaini yake mulka suka rokeshi da ya gina musu katangar da zata rabasu da Yajuju da Majuju.
Yajuju da Majuju sunyi ta kokarin fasa wannan Katanga su fito amma kuma sun kasa.
Sunyi dukkan irin dabarunsu su yi tsalle su fito amma Allah bai basu iko ba, shine tun daga wancan lokaci har kawo yau suna nan suna kwakwule wannan Katanga domin su samu su fito, amma Allah ba zai basu iko ba, sai a karshen duniya.

Ibn Mas’ud (Rta) ya ruwaito daga Manzon Allah (Saww) cewa. A daren da Manzon Allah (Saww) yayi Isra’I ya hadu da Babansa Annabi Ibrahim da Annabi Musa da kuma Annabi Isah, dukkansu sun tattauna akan shin yaushe ne Alkiyama zata tsaya, sun fara tambayar Annabi Ibrahim yace bai
sani ba.

Daga nan Annabi Musa yace shima bai sani ba, daga nan sai Annabi Isah yace babu wanda ya san wannan ranar sai Ubangiji shi kadai.

Sai Annabi Isa (Alaihis Salam) ya cigaba da cewa, abinda Ubangijina ya gayamin shine a karshen duniya, Dajjal zai bayyana, ya zama fitina daga karshe sai a sauko dani, idan ya hadu da ni zai dinga narkewa yana zagwanyewa, Haka nan Allah zai halakar da shi (Dajjal).

Sannan Musulmi zasu yaki kafurai, har sai takai matsayin da Idan kafiri ya buya a bayan wani dutse ko bishiya, zasu yi Magana su kirawo musulmi suce masa zo ga kafiri ka kashi shi.
Daga nan kuma, adalci zai yadu a ban kasa tsakanin Musulmi, can kuma sai Allah ya fito da Yajuju da Majuju. Zasu barko cikin wannan duniya ta gabas da yamma kudu da Arewa, suna shanye ruwa, suna cinye dukkan wani abu da suka yi arba das hi. A lokacin ne al’umma zasu je ga Annabi Isah suna mai rokonsa da ya roki Ubangiji Allah ya kade musu wannan Masifa da Bala’I na Yajuju da Majuju.

Sai Annabi Isah ya daga hannu ya roki Ubangiji, Allah mai girma da daukaka ya amsa, sannan ya dinga saukar musu da tsutsotsi daga sama, suna halakar da su, bayan sun mutu duniya gabaki daya zata cika da warin gawarwakinsu da jinanansu.

Daga nan kuma Sai Allah ya saukar da Ruwan Sama wanda zai wanke duniya gabaki daya ya wanke dukkan dattin gawarwakin Yajuju da Majuju.

Annabi Isah (Alaihis Salam), ya cigaba da cewa, daga zarar Allah ya saukar da wannan ruwa, to babu wani abu da yake gab da zuwa face Alkiyama.

Haka kuma An karbo hadisi daga Abu-Huraira (Rta), Cewa, Manzon Allah (Saww), ya ce “A kowacce rana wasu al’umma (Yajuju da Majuju) suna nan suna hake wata Katanga, da zasu shigo cikin wannan duniya.

Sai sun yi haka har sun gaji, sannan zasu fara hango harsken rana, abinda yake nuna hakarsu ta kusa cimma ruwa (ma'ana sun kusa bige ginin), sai kawai shugabansu, ya umarce su da su koma su kwanta su huta gobe zasu dawo su cigaba.

Cikin hukuncin Ubangiji washe gari suna zuwa, sai su tarar Allah (Swt) ya shafe wannan Katanga ta kara karfi da kwari, sama da yadda suka sameta a jiya. Haka zasu sake cigaba da tone wannan Katanga, su sake komawa, washe gari su sake ganinta kamar basu taba haketa ba.

Haka nan zasu yi ta yi, har sai lokacin da Allah ya hukunta fitowarsu. Idan sunyi aiki har sun bula katangar sun fara hango hasken rana, anan ne shugabansu zai umarce su da su koma su
kwanta, gobe idan sun dawo zasu cigaba, amma a wannan Ranat zai ce IN SHAA ALLAHU.
Bisa fadin IN SHAA ALLAHUN da shugabansu ya yi sai Allah ya amsa, washe gari idan sun komo zasu sami wannan Katanga yadda suka barta jiya! Bayan dawowarsu ne, washe gari, zasu ci gaba da yin aikinsu na bugun wannan Katanga.

Kuma cikin nufin Allah, zasu buge wannan gini su shigo cikin duniya daga katangesu da Allah yayi da al’umma, idan suka fito zasu shanye dukkan wani ruwa da sukayi ido hudu dashi, sannan zasu cinye dukkan wani abinci da suka gani, kai kusan dukkan wani abu da suka gani sai sun cinye shi.

kama daga Bishiya tsirrai da dabbobi, sannan zasu shiga kisan mutane babu ji babu gani!
A wannan lokacin Yajuju da Majuju zasu dinga harba kibau sararin samaniya. Suna harba kibiyoyi da masuna, sannan suna fadowa kasa suna masu digar da jini a jikinsu, anan ne Yajuju da Majuju zasu ce, mun gama da al’ummar da take a ban-kasa sannan kuma wadan da suke sama suma mun gama da su!
A lokacin da suka yi wannan ikirari ne kuma, Allah zai yi musu ruwan wasu irin tsutsotsi wadan da zasu dinga makalemusu a wuya suna cizonsu, haka nan, wannan tsutsa zata hakalasu gabaki dayansu a
cikin dare daya!

A duba a Cikin kitaab al-fitan, (hadisi 4080), 2/1364.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tues 30/08/2016

SANARWA MAI MUHIMMANCHI GAME DA MADIGO DA LUWADI

SANARWA MAI MUHIMMANCI
********
Ka karanta tabbas Zai amfaneka idan ma bai amfaneka ba zai amfani 'danka, 'yarka ko kuma qanenka ko 'dan uwanka. Tun kusan Watan January nayi Rubutu akan 'yan Mata masu 'dabi'ar yin Madigo (Lesbian), tun kusan wancen lokaci na samu kira daga wata baiwar Allah Wadda ta bayyanamin Dalilin shigarta harkar madigo da kuma halin da take ciki.

Yarinyar wacce mun dau kusan Mintuna arba'In mun waya ta shaida min dalilin shigarta Harkar madigo, In da ta bayyana min a makarantar gaba da Secondry aka koyar da Ita wannan muguwar 'dabi'ah.
"Bayan kaini makaranta mu hudu ne a dakin da nake, kuma nice karama a duk cikin wayanda muke daki 'daya da su, ranar da nazo na fara fahimtar 'yan Iska ne, domin kuwa a gado 'daya naga suna yin bacci duk da kowace nada nata gado."

"A haka har na fahimci me suke yi domin kuwa wani lokacin a gabana suke sheke ayarsu."
Yarinyar taci gaba da gayamin cewa, a hankali idan suna yi sai taji sha'awa ta taso mata, kwatsam rannan sai suka bukaci ta shiga cikinsu domin jin dadi. Da farko sai ta nuna musu ai ita bata sha'awar wannan mu'amula kuma tana ma son ta chanja 'daki ne domin kada ta takura musu.

Anan ne suka nuna mata ai babu damuwa tayi zamanta a dakin nasu domin halayenta na burgesu.
Kwatsam sai ranan suka nuna mata ai ta shigo cikinsu yafi tunda Allah bai fadi azabar da za'ayiwa mata 'yan madigo ba sai 'yan Luwadi. Sannan kuma tayi wannan shi ya fiye mata da taje tayi zini ko ta aikata Mistabution (ISTIMINA'I).

Ta shaida min da irin wayannan kalamai aka sanya ta a madigo kuma wallahi yanzu bata sha'awar kowane namiji, haka kuma bata sha'awar aure.

Ta kara shaidamin Cewa, Ita kadai ta lalata yara bata san adadiba, kuma yanzu tana son ta tuba amma ba ta san yanda zatayi ba.

Anan na bata wasu shawarwari tare da nuna mata muddin ta mutu bata tuba ba to kuwa akwai matsala domin Allah zai mata Ukuba fiye da yanda take tunani.

Wannan yarinyar tayi godiya ta kuma bukaci duk ranar da na samu lokaci don Allah Inyi fadakarwa game da Irin Wannan 'yan madigon Masu nunawa mutane madigo bai da wata azaba da aka tanadarwa masu yinsa, haka kuma macce zata ji dadi ba tare da ta rasa budurcin ta ba. Bayan Wannan Jiya14 ga watan October Jaridar Aminiya ta fitarda wani rubutuna game da Maza 'yan Luwadi.

Kusan karfe 10 na dare wani bawan Allah ya kirani, daga daukan wayan na san hankalinsa a tashe yake muryarsa na karkarwa. Ya shaidamin yana 'daya daga cikin masu neman Maza kuma kusan Shekarar sai 15 yana wannan lalata yanzu kuma kusan shekarar sa 10 da aure amma har yanzu ya kasa dainawa.
Yace min hakika babu yanda baiyi ba domin ganin ya bar wannan muguwar 'dabi'ah amma ya kasa.
Bayan gama wayar da shi tare da gama bashi shawarori akan ya tuba ya kuma kauracewa wayanda suke wannan ta'adi.

Cen kusan karfe 12 na dare wani ya kirani ya shaidamin daga wata jami'ah (dake arewa ) yake kira na, ya shaidamin yanda aka sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta luwadi (Wa'Iyazubillah).
Ya gaya min Cewa, wani ne ya sanya shi wannan muguwar 'dabi'ah ta hanyar nuna masa ya zo su rika yin Romace ba tare da sun sadu ba. Wannan yafi yaje yayi zina.

Ya gayamin a hakan ya amince domin a tunaninsa Romac ba komai ba ne, ya gayamin a cikin Romace din ne kawai wata rana ya afka masa yayi masa luwadi.

Ya shaidamin hakika yanzu baya sha'awar macce, Sai dai maza, yace min wani lokaci har kashisa yake dauka ya shafa a al'aurarsa idan wannan sha'awar ta taso masa (Wa'Iyazubillahi).
Yan da kyau 'Yan Uwa mu rika Kula da Suwa Qannenmu da 'ya'yanmu da Abokananmu ke mu'amula domin gudun yin dana sanin a gaba.

Duk wanda yace maka kazo kuyi romace yafi kaje kayi Zina Wallahi karya yake maka Yana so ne kawai ya halaka maka rayuwa.

Sanan yana da kyau 'yan mata su san cewa, da madigo da Luwadi duka daya ne babu banbanci a wajen Azaba a gobe Qiyama. Sannan yana da kyau su san anya mafi sauri ta kamuwa da cutar Infection Itace ta hanyar yin madigo (lesbian). Su kuma samari su sani daga ranar da aka yi maka luwadi daga ranar Kashi ba zai taba tsayama ba. Daga kaji kashi da yazo.

Sannan masu yi yana da kyau su sani daga ranar da kayi sanadiyar wani fadawa cikin Muguwar 'dabi'ah to kuwa duk lokacin da akayi dashi ko yaje yayi sai an rubuta maka zunubi koda kana Cikin kabari ne.
Wannan Muhimmiyar Sanarwa Ce, Idan ka taimaka wajen Yada ta to ka taimaka wajen ya'da Alheri. Idan kuma ka qi yadawa to ka yi hasarar tarin Ladar da Za'a samu.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 15/10/2015

Tuesday, 29 November 2016

NAZARI AKAN YAWAITAR ZAZZABI (MALERIYA)

HUJEWAR OZONE LAYER YA FARA KAWO ANNOBA A CIKIN AL'UMMA.

Tun Kusan Lokacin da Na samu Labari akan k'aruwar Hujewar OZONE LAYER ( Bargon da ke matsayin kariya tsakanin duniya da kuma cutukkan rana), nake ta tunani akan wannan lamari.
A bangare daya kuma Yawaitar Mace-macen hadi da rashin lafiya da Suke Faruwa a Jahar mu ta Sokoto sai na tsaya nayi nazari tare da Bincike mai zurfi game da Wannan Lamari. Sai naga gaba days an dau wannan matsala kacokan an daurata ga zazzabin Cizon Sauro. Wanda kuwa ga dukkan alamu ba haka lamarin yake ba.

Shi dai Wannan OZONE LAYER masana suka ce abu ne tamkar bargo a sararin saman duniya kuma kariya ne ga (Sama) da kuma Mutane.

Suka kara da Cewa, shi wannan Bargon da ake kira ozone layer, yana shinfide ne a Sararin Samaniya domin ya zama kariya ga halittun kasa daga sinadaran da suke zubowa daga zafin rana wanda zasu cutar da 'dan Adam ta hanyar sanyawa mutane cututtuka (masu wuyar Sha'ani). To idan sinadirai masu cutarwa suka zubo sai su makale a jikin wannan Bargon na Ozone layer.

Babu Shakka Wannan Zance na Masana Ilmin Kimiya ba karya bane game da Wannan Bargon.
Domin tun Kusan Shekaru 1400 da suka Gabata Al-qur'ani Mai Girma ya gaya mana labarin wannan Bargon da ke Sama.A Cikin Al-qur'ani Mai Girma Allah (Swt) Yana Cewa, 

ﻭَﺟَﻌَﻠْﻨَﺎ ﺍﻟﺴَّﻤَﺎﺀَ ﺳَﻘْﻔًﺎ ﻣَّﺤْﻔُﻮﻇًﺎ ۖ ﻭَﻫُﻢْ ﻋَﻦْ ﺁﻳَﺎﺗِﻬَﺎ ﻣُﻌْﺮِﺿُﻮﻥَ

MA'ANA, "Kuma Mun sanya sama rufi tsararre, alhali kuwa su daga ayoyinta masu bijirewa ne" (Suratul Anbiya aya ta 31). Sannan a Wata Ayar kuma Allah (Swt) Yana Cewa,

ﻭَﺍﻟﺴَّﻘْﻒِ ﺍﻟْﻤَﺮْﻓُﻮﻉِ


MA'ANA, "Da rufin nan da aka ɗaukaka." (Suratu At-Tur aya ta)
.
A Wani Wuri Kuma Allah (Swt) ya gaya mana Cewa, Wannan bargo kariya ne ga Mazauna kasa.

ﻗَﺪْ ﻣَﻜَﺮَ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻣِﻦ ﻗَﺒْﻠِﻬِﻢْ ﻓَﺄَﺗَﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﺑُﻨْﻴَﺎﻧَﻬُﻢ ﻣِّﻦَ ﺍﻟْﻘَﻮَﺍﻋِﺪِ ﻓَﺨَﺮَّ ﻋَﻠَﻴْﻬِﻢُ ﺍﻟﺴَّﻘْﻒُ ﻣِﻦ ﻓَﻮْﻗِﻬِﻢْ ﻭَﺃَﺗَﺎﻫُﻢُ ﺍﻟْﻌَﺬَﺍﺏُ ﻣِﻦْ ﺣَﻴْﺚُ ﻟَﺎ ﻳَﺸْﻌُﺮُﻭﻥَ

MA'ANA "Lalle ne waɗanda suke a gabaninsu sun yi makirci, sai Allah Ya je wa gininsu daga harsa-shensa, sai rufi ya faɗa a kansu daga bisansu, kuma azaba ta je musu daga inda ba su sani ba." (Suratul An-Nahl aya ta 26).

Friedrich Schonbein Shine mutunen da ya gano Ozone a shekarar 1839, In da a Shekarar 1840 Gordon Miller ya gano amfanin wannan bargo na Ozone layer. Shi dai wannan bargon ya fara hujewa tun kusan shekarun 1980 inda wannan hujewar ta rika fadada tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu, in da a wannan shekarar ta 2016 aka gano wannan bargon yayi qatuwar hujewa.

Masana dai sun riga sun fadi Cewa, Wannan hujewar ta kan iya haifar da kafewar manya da kananan koguna, da kuma karuwar yawan ruwan da ke cikin manyan kogunan
wannan duniya.

Haka Kuma Sun fadi Cewa, Wannan hujewar barazana ce ga lafiyar 'yan Adam din dake rayuwa a wannan duniya musamman sassan duniyar dake fama da yanayin zafin rana. Domin ana samun karin sabbin cututtukan da suke da alaka da fata masu Wuyar magani.

Wannan abu hakika ya fara tabbatuwa domin kuwa a watan juli din wannan shekara ta 2016 (Wato July 2006), a North America an samu mutuwar a kalla mutane 225. Wanda kuma duka bincike ya tabbatar da cewa, dukansu sun samu cutukkane ta dalilin yawan zafin rana.

Haka Wannan Annoba ta mace-mace da rashin lafiya ta yawaita a Wani kauye dake Cikin Erteria In da kusan Sai da 'yan kauyen Suka yanke kauna da rayuwa. Kwatsam kuma Sai gashi Wannan Annoba ta Rashin Lafiya da Mace-mace Sun yawaita a Cikin Tsakiyar Garin Sokoto In da a Rana 'daya zakaji an Rasa fiye da Mutum 50. Babu Shakka Annoba Jarabawa Ce Da Allah Ke yiwa Bayinsa Ko dai don Ya Jarabesu ko Kuma don Gargadesu akan Su tuba daga miyagun laifuka.

....Subhanallah!!!
Jamilu Sani Rarah Sokoto
Wed 26/10/2016

Wednesday, 12 October 2016

ME YA FARU A RANAR 10 GA WATAN AL-MUHARRAM.

ME YA FARU A RANAR 10 GA WATAN AL-MUHARRAM.
*******
A Rana mai kamar ta yau ne, Ranar Goma Ga Watan Al-Muharram aka Kashe Jikan Annabi (Saww) wato Sayyidin Husaini (Rta). Sayyidina Husaini (Rta) An haife shi shekara daya bayan haihuwar wansa wato Sayyidina Hassan (rta), Dukansu suna da kama da Manzon Allah (Saww) daga cibiya har ya zuwa qasa. Annabi (Saww) ne ya sanya masa suna Hussaini.

Sayyidina Husain ya yi shada a ranar 10 ga watan Muharram a Karbala. Sakamakon rikici da ya faru a lokacin Mulkin Yazidu dan Sayyidina Mu'awiya. Sayyidina Husaini da Abdullahi bin Zubayr dukansu basu yarda da jagorancin Yazidu dan Mu'awiya ba. Dalilin Kin yardarsu da Mulkin kuwa lokacin da Sayyidina Mu'awiya (rta) yake kan Shugabanci, Sai ya bar Wasiyar Cewa, idan har Allah ya karbi ransa a bawa 'dansa Yazidu mulki.

Wannan dalili shiyasa Sayyidina Husaini Jikan Manzon Allah (saww) da Abdullahi bin Zubayr Jikan Sayyidina Abubakar (rta) suka ki amincewa da mulkin Yazidu. Saboda a ka'idar Mulkin musulunci a wancen zamani ba zaka ce a idan ka mutu a bawa danka ba sai dai su musulmi su zabi mutane masu daraja suyi musu kuri'ah duk wanda Allah ya bawa shikenan.

 Bayan Wannan abu ya faru Sai Sayyidina Husaini (rta) ya bar Madina ya koma makka da zama shi da Abdullahi bin Zubayr. Bayan An kashe Abdullahi bin Zubayr a Makka Sai ‘yan Shia daga kufa suka aiko masa wasika akan ya zo za su yi mashi mubaya’a. Sai Sayyidina Husaini (rta) ya tura 'dan uwansa Muslim ibn Aqeel akan yaje Kufa ya dubo masa shi wayannan wasikun da gaske ne ko kuwa karya ne.

 Daga nan sai Muslim ibn Aqeel yaje Kufa suka yi masa tarba ta arziki suka nuna masa ai da gaske ne su zasu taimaki Sayyidina Husaini (rta), nan take Muslim ibn Aqeel ya turawa da Sayyidina Husaini da Wasika akan yazo babu shakka da gaske suke akan zasu yi masa mubaya'a.

Da ya zo sai ya gane yaudaran sa suka yi, bai ga kowa ba sai rundinar UbaidulLahi ibn Ziyad.
A ranar 9 gawatan Muharram sayyidina Hussaini ya ce wa jama’arsa gobe akwai yaqi tsakani na da gwabnan Kufa duk mai son komawa gida ya bi dare ya tafi.

Rundunar gwabnan Kufa su 4000 shi ko sayyidina Hussaini ‘yan rakiyarsa 72, gari na waye wa sai yaqi ya barke, aka fafata aka fafutuka sahabi Hussaini ya nuna barde ne domin ya kashe jama’a masu yawa kafin yayi shahada. Ana cikin Wannan yakin ne Wani 'dan Shi'a mai suna Zur’atut Tamimi ya fara saransa a kafada daga nan sai Sinanu dan Annas wanda shima 'dan Shi'a ne ya soke shi da mashi a maqogwaronsa ya kuma qara cakansa da mashin a qirginsa.

kafin Sahabi Hussaini ya kai qasa sai Khuli al-Asbahi (La'anannen Allah) ya sa takobi ya sare kan sahabi Hussaini.(Ya Allah kar ka kai rahama ga wadannan mutanan da suka kashe sahabi Hussaini Ya Allah ka tabbatar da la’antarKa ga wadan da suka kashe Hussaini). Kafin a kashe sahabi Hussaini
ya nuna jarunta matuqa. Wannan yaqin ya faru ne bayan mutuwar sahabi Muawiyya da shekara biyu shi kuma Yazidu dan Sayyidina Muawiyya yana Sham. Bayan sun sare kansa sai suka Dauki kan sayyidina Hussaini suka tafi da shi Sham daga baya aka kai kan Sayyidina Hussaini a Madina aka rufe shi bayan kusan sati da faruwan yaqin. Ya Allah ka qara aminci ga jikan Annabinka ya Allah Ka qara daukaka darajansa amin.

'Yan Shi'a sun dauki ranar goma ga watan Muharram rana ce ta baqin ciki saboda a wannan ranar
ce a ka kashe jikan Annabi (Saww) a yaqin Karbala, wato Sayidna Hussaini (rta) wanda kuma Alhali sune suka kashe-shi da kansu. In da zaka kara gano 'yan Shi'a Munafukaine a Ranar ta goma ga watan Al-Muharram din da aka kashe Sayyidina Husaini hakama qannansa Abubakar da Umar da Usaman dukkan su ‘ya ‘ya ne ga sayyidina Aliyu (rta).

Amma abin ban mamaki ‘Yan Shi’a basa baqin ciki sauran yaran, sai Sayyidina Hussaini (rta) kawai
Allah sarki wannan zai ka qara fahitar damu cewa tsakanin sayyidina Aliyu (rta) da sauranan sahabai duk daya ne, tun da ga shi har yasa sunanayen sahabai Abubakar da Umar da Usman kuma tarihi ya tabbatar da cewa su ‘yan Shia da kansu su ka kashe Sayyidina Hussain A duba a littafin Shi’a Muntahal A’amal1 Shafi na 450 da I’ilamul wara na dabaris Shafi na 203 da Maqtalu Hussain shafi na 147 da Ma’alimi Madaratina shafi na 62 da kitabul Raudha dukkanin wadannan littafan na masu bi addini Shia ne da kansu su ka fada cewa 'Yan Shia ne su kashe Hussain bayan sun aika ma sa da wasiqu ya zo suyi masa mubaya’a, amma kuma suke baqin ciki na yaudara.

 Haka kuma Za'a iya Dubawa a Cikin Littafen Imamu Zahabi Mai Suna Siyar A'alamun Nubla. Sai mutum ya duba tarihin Sayyidina Aliyu, Dana Mu'awiya dana Sayyidina Husaini In shaa Allahu zaka fahimci makircin Shi'ah.

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Wed 12/10/2016

Tuesday, 2 August 2016

TARIHIN DAULAR MUSLINCHI TA ANDALUS 2

TARIHIN DAULAR MUSLUNCI TA ANDALUS (Spain) Fitowa ta 2
*******************************************************


Ga wayanda Basu samu damar karanta Fitowa ta Farko ba Su latsa nan domin karantawa; jamilrara.blogspot.com/…/…/tarihin-kasar-andalus-spain.html…

Ci Gaban Tarihin;

Kasar Andalus Sai da ta Shekara 800 a cikin musulunci kuma daular musulunci. Amma a Ranar da Yahudawa sunka saka Andalus a gaba sai da wannnan kasa ta fita daga hannun Musulmi (ta tashi daga daular musulunci).

kasan cewa duka ka'idodin musulunci da ake bi a kasar da kewaye har sai da ta kai kafirai basa sha'awan shiga kasar, amma randa yahudawa suka bulla a kasar ba'a dauki shekaru 50 ba saida suka juyar da musuluncin. sunka rushe duk wani abu na musulunci akasar suka cenja Sunayen garin (daga na musulunci zuwa nasu na kafirci).

Har sai da ta kai ta kawo Gaba daya kasar ba'a yarda ayi addinin musulunci ba.
Babban abinda ya kawo haka a kasar kuwa rashin hadin kan da yahudawa suka sanya a tsakanin 'yan kasar. Wato babu hadin kai tsakanin kiristoci na asali da musulman da aka tilasta masu shiga adinin kirista. Haka ma tsakanin musulmin su kansu babu hadin kai.

To daga nan Sai tattalin arzikin kasar ya rika fadawa cikin nakaso da samun matsala tare da tabarbarewa.
Sakamakon ganin Tattalin Arzikin na tabarbarewa sai aka yi wani zaman tattaunawa (Metting) a Ingila don idan har aka bari tattalin arzikin kasar yana rushewa to mutanan kasar zasu watsar da kiristiyaniti zasu koma musulmai.

A zaman tattaunawar ne sunka yanke shawarar cewa za'a kirkiro da wani abu wanda zai hada kan 'yan kasar. A cikin tattaunawar akayi ta kawo abubuwan da ake ganin zasu karbu ga musulmi da kafirai amma duk wanda aka kawo aga bayayi. Anan ne wani ya bada shawara akan a kirkiro da gasar kwallon kafa a kasar domin zata karbu (musamman ga matasa musulmi da Kirista).

To anan ne aka kirkiro da kwallon kafa akasar ta spain. Wannan ne yasa aka debi dalibai akaje dasu kasar Ingila aka karantar dasu kwallon kafa da dabarunta tare da yanda zasu sanyawa mutane Sha'awarta.
Bayan sun kware sai aka turosu kasar ta spain don su karantar da matasan kasar kwallon ta kafa.
Anan ne aka kirkiro da wani kulob na kwallon kafa mai suna sevilla (Wanda asalin sunan wani garine na musulunci da ke cikin kasar ta Spain mai suna Ishbiliya).

Sevilla shine kulob na farko da aka kirkiro akasar ta Spain. (Wannan yafaru ne a shekarar 1890 zuwa 1899). daga baya aka kirkiro da spanish king cup. Wato copa del ray, Shi wannan kofin an kirkiroshi ne wajan bikin bada sanda ga sarkin kasar.

Haka a Shekarar 1905 aka samar da kulob din real madrid. sai kum kulob din Barcalona Sai Espenyol da ganan sai visaya. Wayannan kulob kulob din su sunka maye madadin musulunci a kasar. har sai da ya kasance musulmi yafi son kirista dan kulob dinsu da musulmi wanda ba dan kulob dinsu ba.

Haka sarkin spain mai suna king alfanso yace suna da wata kalma ta kiristoci wadda su sunka san sirrin dake cikinta (Wannan kalmar).kalmar tana da wani sirri.wanda sai dan kungiyar yahudawa yasan sirrinta.
Wannan kalmar itace real. wannan kalmar sarkin ya bada ita a shekarar 1927 yace duk kulob din dake son kalmar ya dauki wannan kalmar yabashi aronta.

Nan take kulob fiye da 10 sunka dauketa anan ne anka samu real zaragoza wanda ainihin sunan garin musulunci ne wanda ake kira saraqusda.

Sai Real betis, Real soceida, Real valadolid wanda shima asalin sunan garin musulunci ne mai suna valadu walid, Sai Real murcia, Real union, Real sporting gijon sai Real madrid. (In shaa Allahu zan kawo bayanin ma'anar Real anan gaba).

Haka ma a can baya akwai wani bayahude makiyin musulunci na gaske wanda yana cikin wayanda sunka yaki musulunci akasar ta Spain sunan sa santiago to shine aka sakama stadium din Real Madrid domin Girmamawa gareshi da girmama kwazonsa.

To ta hakane akaci musulunci da yaki akasar. yanzu yawan musulmai akasar ta spain akalla akwai musulmai dubu 500 kacal. Yayin da mutanan kasar kuma yawansu ya kai miliyan 36. wanda tarihi ya nuna kasar ta spain tayi zama kashi 95 cikin 100 musulmai ne kamar yadda na fada a baya
Kuma a cikin yawan musulmin a kasar dubu 500 to dubu 400 ba ainahin 'yan kasar bane bakine (wato ba yan asalin kasar bane).

Daga cikin Musulmi Mutum Dubu 100 kacal sune 'yan kasa. cikin dubu 100 din mutum dubu 20 sabbin musulmai ne dubu 80 ne kawai tsofaffin musulmai. Hakika da kwallo aka Shiga Kasar Spain aka Karya Kashin gadon bayan Musulunci a kasar ta Spain. Kuma dama yahudawa sunce kwallo addini ne mai zaman kanshi. kuma duk wanda ya shiga cikinta yau da gobe sai ya aje addininshi ya rungumeta don zai samu tarin kudin da ba zai iya samun kwatan-kwacinsu a addininsa ba. Haka kuma zai kashe mata kuddin da ba zai iya kashewa a addininsa ba. Kuma Zai bada lokacinsa lokacin da bazai iya ba addininsa ba.
Akwai wata waka da akayi a 2008 mai suna "Football is religion". haka ma shugaban fifa a lokacin Sep Blater yace Football is more than sport is a religing.

Kuma Wannan Gadkiya ne Saboda kiyasin da akayi a akwai masu sha'awar kwallon kafa sama da mutum biliyan 5. Yayin da yawan mutanan duniya gaba daya biliyan 7 ne. yayin da musulmai yawan mu be kai biliyan 2 ba. kunga masu kwallo da sha'awarta sun lunka yawan musulmai aduniya. Haka yanzu yan kwallo sune masu kudi a duniya.

Dan wasan Real madrid duk minti yana amsar sama da naira dubu 9 koda yana baccine. A duniya Bayan Bill gate 'dan Kasar America da yafi kowa Kuddi a duniya Sai Mutumen Spain mai suna Amancio Ortega shine na Biyu da kuddi a duniya wannan mutumen a talaka ya tashi amma ta dalilin yin tufafe wa 'yan kallo yanzu ya zama shine yafi kowa kuddi a kasar ta Spain kuma shine mai kuddi na biyu a duniya. (Shima zuwa gaba zan kawo tarihinsa da kuma yanda ya samu kuddinsa In shaa Allahu).

Mutane da yawa suna tambayar wai ina kulob kulob din nan ke samun wayannan makuddan kudade ne?
Watakila in na samu dama nan gaba zan kawo bayanai game da haka tare da kawo mutu wasu abubuwan da suka Shafi Daular musulunci ta kasar Andalus (Spain a yanzu In shaa Allahu).

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Mon 25/07/2016.

SOYAYYAH DA DADI

SOYAYYA DA DADI GA MA IYANTA
********************************

Wata Mata Ce ta yanke Shawarar tsokanar mijinta akan ta gwada shi ta gani ko yanda yake sonta
Wata Rana ya fita aiki, Cen kusan lokacin da zai dawo sai ta Janyo Biro da takarda ta fara rubutu kamar haka; "BA ZAN IYA YI MAKA SALLAMA BA A CIKIN WANNAN RUBUTUN, SABODA RAINA A BACE, KAI TSAYE INA SON IN GAYA MA NE CEWA, NI NA GAJI DA ZAMA DA KAI KUMA DAGA YAU BA ZAKA SAKE GANI NA BA, INA FATAN ZAKA CIRE NI DAGA RANKA"

Bayan ta gama Sai ta nemi Wuri ta zauna tana jiran Isowarsa, Cen Sai taji Sallamar Sa ya Shigo gidan.
Ta ajiye takardar a kan gado, Tayi maza ta buya a bayan dirowa a cikin dakin domin taga yanda zai yi idan ya karanta wannan takarda.

Ya shigo falo yayi Sallama amma shiru ba kowa (ba'a amsa ba), kai tsaye ya shiga cikin daki.
Anan ma yayi Sallama amma shiru ba'a amsa ba, Sai takarda da Biron da ya hanga saman Gado.
Ya dauki takardar ya karanta tsaf. Cikin farin cikin ya dauko wayarsa daga Aljihu ya latsa kiran wata number. Cen sai yace; "Hello my Sweet heart. Albishirinki matata ta tafiyarta yanzu ke ga mun huta da boyo don haka yanzu ma ki shirya gani nan zuwa in dauki ki." Bayan ya gama wayar ya ajiye wayar. Sai yace, kai Yau gaskiya ina cikin farin ciki da annashuwa, bari ma in dan taka rawa. Anan yayi rawa bayan ya gama sai ya juya takardar yayi wani rubutu akai.

Daga nan sai ya kama hanya ya fita ya bar dakin. Wannan mata cikin tsananin kishi da jin haushi ta fito daga in da ta buya. Tayi Sauri don ta same shi amma ina ya riga yayi nisa har ya bar gidan. Sai tace; "Ai kuwa yau ana yin ta domin sai nayi maganin wannan shegiyar karuwa."

Nan take ta dauko karamar tukunya ta zuba ruwa ta daura ruwan zafi. Tazo daki ta zauna tana cika da batsewa. Cen Sai ta tuna da ai taga yayi rubutu a takardar cen ta janyo takardar ta fara karanta rubutun da yayi akan takardar. "NI BARI IN FARA DA YI MIKI SALLAMA ASSALAMU ALAIKUM, AI NA GANKI KIN BUYA A BAYAN DIROWA KUMA KO BAN GANKI BA NA SAN KINA NAN A BOYE DOMIN KAMSHIN TURARENKI MA BA ZAI BARKI KI BUYA BA."
"DON HAKA NI DAI NA TAFI NA SAYO BURODI DA FATAN KAFIN IN DAWO KI DAURA RUWAN ZAFI DOMIN YUNWA NAKE JI. NA BARKA LAFIYA SAI NA DAWO MATATA ABIN ALFHARINA."

Jamilu Sani Rarah Yace; Kenan Ruwan da aka daura domin antayawa wacce zata shigo, Buredi Za'a antayawa su. Hahahah.

Jamilu Sani Rarah Sokoto.
Sun 17/07/2016

ME YASA AKE SON AYI JUYIN MULKI A TURKIYA?

ME YASA AKE SON AYI JUYIN MULKI A TURKIYA?
**********************************************

Tayyip Erdogan Shine Prime Ministan Kasar ta Turkiya tun Shekarar 2002 ko kuma 2003, Tayyip ya kasance Musulmi mai son Ci gaban musulunci da Musulmi a kasar ta Turkiya.
Babu Shakka kasar turkiya kasace ta Musulunci, amma a gaskiya wasu musulmin kasar a yanzu basa kula da hakkokin musulunci.

Idan nace basa kula da hakkokin Musulunci Ina nufin, wasunsu basa bin koyarwar ta addinin musulunci.
Domin wani marubucin Kafiri 'dan kasar ta turkiya ya taba rubuta wa a cikin Littafensa Cewa, "Da ace yanda musulmin Turkiya suke haka Sauran Al-ummar musulmin duniya suke da an zauna lafiya a Duniya."
Dalilin da yasa ya fadi haka kuwa shine, Musulmin Turkiya zai iya jan Kafiri su je cikin masallachi suyi fira har da kyakkewa, wanda ni a ganina sam ba koyarwar addinin musulunchi bace.

Wannan shiyasa ma wasu daga cikin kafirrai basa daukar wasu daga cikin musulmin turkiya na yanzu a matsayin musulmi. Amma zaman Tayyip Shugaban kasa a Shekarar 2013 sai ya fara sauya halin musulmin kasar izuwa turbar Addinin musulunchi.

Daga cikin wannan juyarwa akwai lokacin Majalisar Dinkin duniya suka bada umurnin fara yin tsarin hana haihuwa a kasar. Daga jin haka nan take Tayyip ya fito a kafafen watsa labarai yake cewa; "Daga yau daga Rana mai kamar ta yau kada gidan musulmin da naji ance suna amfani da tsarin kayyade Iyali."
"Hakika addinin musulunci yana bukatar al'umma masu yawan gaske don haka kada wata macce ta kuskura ta ajiye haihuwa ba tare da dalilin musulunci ba". "Musulmi dole ne mu bi Allah da Manzonsa domin Annabin mu Mai girma yace, Mu haifafa domin yayi alfhari damu."

Baya ga wannan Shugaba Tayyip na daga cikin Shugabanin da basa tsoron Isra'il hasalima adawarsa a garesu tafi ta sauran shuwagaanni tsanani. Ko wane taro ake yi ko mai muhimmancin taron idan lokacin Sallah yayi Tayyip yakan Fita yaje yayi Sallah. Haka ma akwai wani 'dan majalisarsa mai suna Huseyin Sahin yake Cewa, "Mu musulmi hakika Shugaba Tayyip ya zamar mana wani babban Jigo domin duk zaman da muke idan lokacin Sallah yayi yakan tashi tare da umurtarmu mu je muma muyi sallah."

Tayyip Erdogan shugaba ne adili mai son Ci gaban kasarsa da addinin musulunchi don haka yana da kyau taya shi addu'ah ta samun cikakken samun kariya daga makiya masu son hanbarar da Mulkinsa.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 16/07/2016