Thursday, 21 April 2016

MUTUWAR AURE A KASAR HAUSA INA MAFITA?

MUTUWAR AURE A KASAR HAUSA INA MAFITA?

Allah (SWT) da kansa ya kira 'ya macce da sunan Nutsuwa a gun mazaje, duk ilmi, kuddi ko Sunan da 'da namiji yayi bazai taba samun nutsuwa ba sai tare da 'ya mace.

Shi yasa Allah da kansa a wani wuri a cikin Alqur'ani ya kirayi 'ya'ya mata da lafazin Sutura a gun maza ba don komai ba domin anuna mana muhimmanci da kimar 'ya'ya mata a gidan duniya. Domin duk kuddinka ko Ilmin ka ba zaka iya tafiya tsirara ba.

To amma wani abin ban haushi a yanzu zaka tarar mazajen yanzu basa kula da wannan qima da martabar da Allah (Swt) Ya baiwa 'ya'ya mata. Wani babban abin haushi da ke faruwa a wannan kasa tamu, musamman a wannan bangaren namu na Hausa Fulani.

Tun ina Qidayawa har na gaji da kirgawa na zubawa sarautar Allah ido tare da addu'ar Allah ya kawo sauki game da wannan matsalar

Ko kunsan me nake kirgawa? Kananan 'Yan mata wayanda ake yawan saki ba tare da sun mayar da shekara da yin aure ba. Wannan abu ba karamin 'daga min hankali yake ba.

Wallahi nasan kusan macce 5 zuwa 6, 7 da suka fito daga gidan mijinsu ba tare da sun mayar da shekara a gidan na aurensu ba. Kuma galibi duk zaka same su yara 'yan kanana wayanda shekarunsu ba zasu haura 23 zuwa da 24 ba.

Duk lokacinda aka sanya muhawara akan me yake kawo sakin aure a kasar Hausa zakayi tajin bayanai daban-daban. Wasu zaka ji sunce rashin ladabin 'ya macce ne, Wasu kuma zaka ji sun ce rashin tsafta da kula da mai gida ne, Wasu kuma zaka ji sun dauki laifin gaba daya sun daura shi akan namiji suce rashin hakuri ne.

A iya bincike da nazarin da nayi game da mace-macen Aure da ke faruwa a yanzu na gano wasu daga cikin wayannan dalilai da ke sanya saurin rabuwa a tsakanin ma'aurata.

Da farko akwai rashin sanin ma'anar aure da kuma raahin sanin darajar da ke cikin aure, galibi maza da matanmu duka muna suna yin aure ne ba don zamansa ibada ba. A'a suna yine saboda dakushe sha'awar da ke damunsu. To da zarar akayi aure wannan sha'awar ta kau ko kuwa sai kowa yaji ya gaji da 'dan uwansa. Domin dama ita sha'awa kamar wutar karace saurin cenyewa take.

Abu na biyu kuma akwai rashin bin ka'idojin da musulunci ya sanya wajen yin aure. Yana daga cikin abinda Manzon Allah (Saww) ya karantar da musulmai Ya ce, Ku zabar wa 'ya'yanku uwa tagari.

Ta yaya zamu zabarwa 'ya'yanmu Uwa ta gari? Anan ma Annabi (Saww) bai barmu a kara zube ba sai da ya gaya mana yanda zamu zabe ta. Yana daga cikin hanyoyin zaben mata tagari yin istihara (addu’a ce manzon Allah (Saww) ya koyar da al’umarsa. Duk  wanda  ya tashi neman aure ya yi istihara.Ita wannan sallar raka’a biyu ake yi sannan a karanta addu’ar).

A addininmu musulunchi ba'a yarda mutum ya fara nemman aure ba, ba tare da ya yi istikara ba. Bayan ya yi istihara sai kuma ya shawarci mutanen kirki da wadanda suka santa.

Domin mace ita ce uwa ta farko ga ‘ya’yanka. Yara suna tasowa ne a kan dabi'unta da halayenta. Haka a addinance ba'a a lura da kyawon mace wajen aure, domin ba shi ne mazon Allah (Saww) ya ce a lura da shi ba.

Manzon Allah (Saww) ya ba da
labari yake cewa, Ana auren mata saboda abu hudu (4): Wasu suna auren mace saboda dukiyarta, wasu kuma suna auren mace
saboda kyawonta, wasu kuma suna auren mace saboda danginta, wasu kuma suna auren mace saboda addininta. Sai Annabi (Saww) ya ce na horeka da ka aure ma’abociya addini.

A Wani hadisin da ibn Maajah ya ruwaito Manzon Allah (Saww) ya ce, “Kada ku auri mata saboda kyawon su, kyawonsu yana iya
juyar da ita.( ta kasance mai girman kai.) Sai ya qara da cewa, “Kada ku auri mata saboda dukiyarsu: Ana sa ran dukiyarsu ta sanya su girman kai. Sai dai ku aure su saboda addini.

Wani mutumi ya je majalisin Safiyanu bn Uyaynah ya ce, “Ya Aba Muhammad ina fama da matata tana wulaqanta ni matuqar wukaqantawa. Sai Safiyanu bn Uyaynah ya yi shiru kadan sannan ya ce, “Me yiwuwa ka aure ta ne saboda ka samu daukaka.” Sai mutumin ya ce, “Lallai haka ne. Sai ya ce, “Duk wanda ya auri mace saboda neman daukaka, to Allah zai qasqantar da shi. Wanda kuma ya auri mace saboda dukiya Allah
zai jarabce shi da talauci. Wanda ya auri mace saboda addini to Allah zai hada masa daukaka da dukiya da addini.

Kunga kenan wannan duk yana nuna mana kada muyi aure don sha'awar macce tana fara ko tana da kyawo ko 'yar gidan masu kuddi ce da sauransu. A'a anan ana so ka dauki aure a matsayim ibada kuma ka auri macce ba dan komai ba sai don addininta

Ko kun san muhimmancin auren macce mai addini? Idan baku sani ba ku tsaya kuji. Imamu Shafi’i babansa ya rasu tun yana dan jariri amma da yake uwarsa mai addini ne a wajenta ya haddace Qur’ani mai girma.

Imam Ahmad bn Hambal ya ce shekaransa talatin da matarsa amma bata taba saba masa ba ko jayayya da shi bata taba yi da shi ba, Amfanin mai addini ke ne kenan.

Babu shakka rashin auren macce mai addini yana daga cikin manyan dalilan da suke kawo mutuwar aure a wannan zamani da muke ciki.

Don haka yana da kyau maza a ji tsoron Allah a rika yin Aure don Allah ba don Sha'awa ko daular gidansu yarinya ba yana da kyau a rika daukar aure a matsayin bauta babu shakka wannan zai rage mace-macen auren da ke faruwa a zamanin nan.

In shaa Allahu zan dakata anan a gaba zan kawo siffofin macce mai addini da kuma irin Suma mata mazan da ya kamata su aura da kuma yanda za'a rika walwale husuma da zarar ta faru tun ba'a kai ga saki ba. Dan uwanku a Musulunchi Jamilu Sani Rarah Sokoto Nigeria.

In da nayi dai-dai Allah ka bamu lada mu duka In da nayi Kuskure ba daga ni bane daga Shaidanne Allah ka yafe mana.

Tuesday, 19 April 2016

NIGERIA KASARMU TA GADO

Nigeria Kasarmu Ta Gado.
********
Shuwagabanninmu na Sayen Manyan Motoci domin hawa wasummu Suna Bukatar In da Zasu sami kuddin Sanyen Abinci. Wasunmu ma na kwana da Yunwa.

ShuwagabanninMu na Daukar Shatar Jirgin Sama Su tafi Kasashen Waje. Amma a koda yaushe suna gaya mana Cewa An sace Kuddin Kasa.

ShuwagabanninMu na Biyawa 'Ya'yansu Manyan Makarantu a kasashen waje amma kullum Sai Su ce mana an wargaza mana kasarmu.

Shuwagabanninmu na Cin abinci su koshe su kwana wuri mai kyau amma idan munyi magana ace mana mun cika Gajen Hakuri.

Shuwagabanni Ku sani Manzon Allah (Saww) yana cewa:

ﻣﻦ ﺍﺳﺘﻌﻤﻠﻨﺎﻩ ﻣﻨﻜﻢ ﻋﻠﻰ ﻋﻤﻞ ﻓﻜﺘﻤَﻨﺎ ﻣﺨﻴﻄًﺎ ﻓﻤﺎ ﻓﻮﻗﻪ, ﻛﺎﻥ ﻏُﻠﻮﻻً ﻳﺄﺗﻲ ﺑﻪ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ.

Ma'ana: Duk wanda muka bashi wani aiki daga cikinku sai ya boye mana koda gwargwadon allura ko abinda ke sama da shi to wannan gululi ne da zai zo dashi a ranar tashin kiyama.

Imamu Abu dawud Ya Ruwaito Hadisin a Hadisi Mai lamba 2943.

MU DAI AIKIN MU GAYA MUKU KO KU DAUKA KO KUYI DARIYA, DARIYARKU TA ZAN KUKA GABA DA NADAMAR MAI QIN GASKIYA.

Da Muka Ce Kar Talakawa Suyi Sak wasu sun Kiramu da Maqiya. Yanzun ma idan mun hango mun fadi wasu na mana izgilanci.

A cikin Alqur'ani Mai Girma Suratu Yunus aya ta 58 Allah Yana Cewa;

ﻗﻞ ﺑﻔﻀﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺑﺮﺣﻤﺘﻪ ﻓﺒﺬﻟﻚ ﻓﻠﻴﻔﺮﺣﻮﺍ ﻫﻮ ﺧﻴﺮ ﻣﻤﺎﻳﺠﻤﻌﻮﻥ.

Ma’ana: Ka ce: Ku yi farin ciki da falalar Allah da rahamarSa shi ne mafi alheri daga abin da suke tarawa.

Hakika mu bama bakin ciki da abinda wasu suka samu ko kuma suka tara. Mu ni'Imar da Allah ya mana ta Musulunchi ta Ishemu.

Alhamdul Lahi Ala Nee'Imatul Islam.

Jamilu Sani Rarah
Tue 19/04/2016.

Friday, 15 April 2016

BAYYANAR MADIGO A KASAR HAUSA LAIFINWA? KUMA INA MAFITA?

BAYYANAR MADIGO A KASAR HAUSA LAIFIN WA? INA MAFITA?
************
Sau da dama Idan na tuna halin da wasu daga cikin 'yan matan arewa suka fada na neman Jinsin Su, hakika na kan kasa samun Natsuwa a zuciya ta.

Daga cikin Kashi 100% na 'yan matan Arewa zaka iya samun Kashi 30 Suna wannan mummunar 'dabi'a ta Madigo (Wa'iyazu Billah).

Babban Abin tashin hankali a Yanzu har matan Aure ake samu suna aikata wannan mummunar 'dabi'a ta neman Jinsinsu.

Babban Abin tashin hankali a yanzu wai har aure suke daurawa tsakaninsu (domin biyan bukatar junansu).

Kwanan baya na samu wani labari wanda ya tadarmin da hankali ainun, wannan labari duk mai imanin da ya saurare shi ko ya ji shi to hankalinsa zai tashi matuka.

Wata matace Wacce Shekarunta Sun haura 45 zuwa sama, ta koyar da 'yar cikin ta wannan lalata ta Madigo bayan koyar da ita wai sai kuma ta sanya ta tana nemo mata kananan yara (sa'an 'yar tata) tana koyar da su wannan muguwar dabi'a (Wa'iyazubillah).

Dalilin da yasa asirinsu ya tonu shine, ita yarinyar ta nemo wata wacce take mutuwarso sai mahaifiyar ta ce ta bar mata ita to fa anan ne asiri ya tonu taje ta sanar da mahaifinsu duka sirrinsu da yanda akayi har ta koya mata wannan mummunar 'dabi'a.

Haka kuma Jaridar Leadership Hausa ta Ruwaito wani labari a shekarar 2015 wani magidanci ne matarsa ta tursasa masa kara auren wata aminiyarta.

Bayan ya auri aminiyar tata da 'yan watanni sai Allah ya tona musu asiri in da mijin ya kamasu suna wannan 'dabi'ar ta madigo.

Haka kuma wani magidanci ya kama 'ya'yansa biyu (Ya da Kanwa) sun auri juna. Suma suna biyawa kansu wannan bukatar.

To wannan da me yayi kama? Idan har Mahaifiya zata koyar da 'yarta wannan lalata? Haka Ya ta koyarda Kanwarta wannan lalatar?

Ina mafita Idan har kishiya da Kishiya zasu auri juna su rinka biyawa kansu bukata su manta da Mijinsu?

Babu shakka wannan Ba karamar Masifa bace ta kunno muna ai a Arewacin Nigeria, wanda idan bamu tashi tsaye ba to kuwa akwai babbar matsala wacce zata yi sanadiyar wargajewar wannan nahiya tamu.

Daga cikin Masu wannan laifi akwai iyaye maza domin Kabar 'yarka 'yar shekara 24 ko 25, 26, wani har 30 bata yi aure ba kuma ba tare da tana tattare da wata lalura ba babu shakka wannan na sanadiyar faruwar wanan abu.

Hakika akwai lalura domin akwai matan da Aljannune ke hana su aure wasu kuma kawai ganin duk abinda take nema tana samu yakan sanya takiyin auren.

Babu shakka wayannan Wayoyi da muke amfani dasu sune manyan musabbabin Wannan lalacewar da wasummu sukayi.

Hakika ya zama dole ga dukkaninMu mu rika kula da matanmu da Qannenmu shin da wa suke Hulda? Kuma wace Hulda suke yi a tsakaninsu? Kuma ya halayen Qawayensu da suke?

Babu shakka wannan ba karamar taimakwa zaiyi ba wajen magance wannan matsalar. Mu tuna a cikin Alqur'ani Allah yana Ce Mana; YA! KU WAYANDA KUKAYI IMAMI KU TSARE KANKU DA IYALANKU DAGA WUTA.

Hakika Duk masuyin wannan mummunar 'dabi'a suji tsoron Allah su tuba kuma su san cewa, Wallahi Duk mai yin Wannan 'dabi'ah kuma ta mutu tana aikatata wallahi Allah zai azabartarda ita sosai da sosai kuma zata hadu da mummunar makoma a cikin Qabarinta.

Jamilu Sani RARAH.
Fri 15/04/2016

Saturday, 12 March 2016

LADUBBAN CIN ABINCI A MUSULUNCI

 LADUBBAN CIN ABINCI YA KAMATA KOWA YA SANSU
**********
Addinin musulunci addini ne mai girma da tsari, addini ne da bai bar wani abu aboye ba face yayi bayani akansa domin musulmai ya ribantu da abin, lura da wannan, addinin Musulunci ya zo da ladduba masu yawa da kuma tarin amfani dangane da shiga makewayi da kuma fita daga makewayin. Haka ya sake bayani kan ladduban cin abinci, da sauran abubuwa da suka kama daga saduwa, sanya sutura, kwanciya da sauransu. Ga dai kadan daga cikin ladduban cin abinci, kamar haka:

1.  Fadin BISMILLAH a lokacin fara cin abinci: Babu ko shakkah fadin bisimillah shine ladabi na farko wajen cin abinci saboda an karbo hadisi daga Umar bin Abiy-salamah (RA) yace: Na kasance yaro qarqashin kulawar Manzon Allah (saww) kuma hanuna ya kasance yana yawo a cikin akwashin abinci, sai yace dani: Ya kai yaro! Ka ambaci sunan Allah (ma’ana kayi Bisimillah) , ka ci da hanunka na dama, ka kuma ci daga abinda ke gabanka.
Jabir yace:- Daga wannan lokacin ban gushe ba; wannan ne irin cin abincina.
(Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5376, da Imamu Muslim hadisi mai lamba: 2022).

2.   Cin abinci da hannun dama: Hakika cin abinci da hannun dama shine ladabi na biyu daga ladubban cin abinci, Wannan kuma sunna ne saboda hadisin da ya gabata.

3.   Mutum ya ci gabansa: Shima wannan sunna ne saboda hadisin da ya gabata. Sai dai idan mutum ya san cewa mutumin da suke cin abinci tare da shi ba zai cutu ko kyamaci yawo da hannu a cikin kwaryar abinci ba, to a nan babu laifi kan ya ci daga ko-ina na kwano; saboda hadisin Sayyidina Anas bin Malik (RA)  a qissar  wani tela da ya gayyaci Manzon Allah (Saww) zuwa cin abinci Anas yace: Sai na ganshi –yana nufin: Annabi (saww) yana bibiyan kabewa daga geffen kwano. Ko kuma idan mutum ya kasance yana cin abincin ne shi kadai; babu wani a tare da shi, ko kuma abincin akwai launukan abun ci da dama; a irin wannan halin ya halatta ya ci abincin da ke gaban waninsa; matuqar dai bai cutar da wani da hakan ba.

4.     Fadin "Alhamdu Lillah" a qarshen abinci: Yana daga cikin ladubban cin abinci Saboda hadisin Abu-umamah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) ya kasance idan aka dauke akwashin abinci bayan kammala cinsa- daga gaba-gare shi sai yace:

Ma'ana: Yabo mai yawa daddada mai albarka sun tabbata ga Allah, Allah Ubangijinmu ba a barin yi masa da'a, ko kuma ace an wadata ga barinsa. (Imam Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5459).

Da kuma wani hadisi da Annabi (saww) ke cewa, Lallai Allah yana rubuta yardarsa ga bawa, idan ya ci abinci ya gode masa akanta, ko ya sha abun sha ya gode masa akansa. (Imamu Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 2734).

5.    Makruhi ne cin abinci a kishingide: Cin abinci a kishingide makaruhine (ma’ana ba lad aba zunubi) Wannan kuma saboda hadisin uwar muminnai A'ishah (RA) tace, Nace: Ya ma'aikin Allah! Ka ci abinci Allah ya sanya ni na zamo fansarka a halin kishingida; saboda zai fiye maka sauqi, Sai manzon Allah (saww) ya karkata kansa har sai da goshinsa ya yi kusan taba qasa, sai yace: A'a! zan ci abinci ne kamar yadda bawa ke cin abinci, zan kuma zauna kamar yadda bawa ke zaunawa. (Albagawiy a cikin littafin "Sharhus sunnah" ya rawaito shi (11/286-287), da Ahmad a "Zuhdu" (5-6) kuma Shu'aibul Arna'ud ya inganta shi da "wani hadisi mursal da ya ke masa shaida", a cikin (Hashiyar sharhus sunnah)
Da kuma saboda hadisin Abu-juhaifah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) yace: Lallai ni bana cin abinci a kishingide. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba 5398).

6.    Mustahabbi ne hanuwa daga aibata abincin da mutum baya son cinsa: Hakika aibata abinci mustahabbine saboda hadisin Abu-hurairah (RA) yace: Manzon Allah (saww) bai taba aibanta abinci ba; idan ya yi sha'awarsa sai ya ci, in kuma bai yi ba, sai ya bari. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5409, da Imamu Muslim a hadisi mai lamba: 2064).

7.    Cin abinci daga geffan masaki, da kuma kasancewar cinsa daga tsakiyar kwarya makruhi ne: saboda hadisin Ibnu-abbas (RA), daga Annabi (Saww) lallai shi an zo masa da masaki da aka sanya kwababben alkubuz da nama mai suna (Sarid), Sai yace: Ku ci daga geffan masakin, kada ku ci daga tsakiyansa, saboda albarka tana sauka ne a tsakiyarsa.

8.     Cin abinci da yatsu guda uku, da kuma sude su bayan kammalawa, shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda hadisin Ka'ab dan Malik (RA) yace: Annabi (Saww) ya kasance yana cin abinci da 'yan yatsunsa guda uku, baya kuma wanke hannunsa har sai ya sude su.  (Imamu Ahmad ya rawaito shi (1/270), da At-tirmiziy (lamba: 1805), ya kuma ce: hadisi ne hasan ingantacce. Da Abu-dawud (lamba: 3772), da Ibnu-majah, (lamba: 3277), Albaniy ya inganta shi (Sahihu sunan Ibni-majah, lamba: 2650)).

9.  Cinye abin da ya zuba ana tsakiyar cin abinci, ko wanda ya warwatsu: Shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda fadinnsa (Saww): Idan lomar dayanku ta fadi to sai ya kade mata kura, sannan ya cinye ta, kada ya barta ga shedan.

10. Sude kwaryar da aka ci abinci a cikinta da lashe yatsu: Shima wannan na daga cikin manyan ladubban cikin abinci saboda fadin Sayyidina Anas (RA) a cikin hadisin da ya gabata, da yake cewa Kuma ya umurce mu yana nufin Annabi (saww) da mu katse kwaryar abinci. Ma'ana: mu sude ta, mu kuma bibiyi abinda ya rage a cikinta na abinci. A wata riwayar kuma aka ce: Annabi (saww) ya umurce mu da mu sude 'yan yatsu da kuma akwashi, yace: Saboda lallai ku ba ku san a ina ne daga cikin abincinku albarkar ta ke ba!.

Jamilu Sani RARAH

Sat 11/03/2016.

LADUBBAN CIN ABINCI

 LADUBBAN CIN ABINCI YA KAMATA KOWA YA SANSU
**********
Addinin musulunci addini ne mai girma da tsari, addini ne da bai bar wani abu aboye ba face yayi bayani akansa domin musulmai ya ribantu da abin, lura da wannan, addinin Musulunci ya zo da ladduba masu yawa da kuma tarin amfani dangane da shiga makewayi da kuma fita daga makewayin. Haka ya sake bayani kan ladduban cin abinci, da sauran abubuwa da suka kama daga saduwa, sanya sutura, kwanciya da sauransu. Ga dai kadan daga cikin ladduban cin abinci, kamar haka:

1.  Fadin BISMILLAH a lokacin fara cin abinci: Babu ko shakkah fadin bisimillah shine ladabi na farko wajen cin abinci saboda an karbo hadisi daga Umar bin Abiy-salamah (RA) yace: Na kasance yaro qarqashin kulawar Manzon Allah (saww) kuma hanuna ya kasance yana yawo a cikin akwashin abinci, sai yace dani: Ya kai yaro! Ka ambaci sunan Allah (ma’ana kayi Bisimillah) , ka ci da hanunka na dama, ka kuma ci daga abinda ke gabanka.
Jabir yace:- Daga wannan lokacin ban gushe ba; wannan ne irin cin abincina.
(Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5376, da Imamu Muslim hadisi mai lamba: 2022).

2.   Cin abinci da hannun dama: Hakika cin abinci da hannun dama shine ladabi na biyu daga ladubban cin abinci, Wannan kuma sunna ne saboda hadisin da ya gabata.

3.   Mutum ya ci gabansa: Shima wannan sunna ne saboda hadisin da ya gabata. Sai dai idan mutum ya san cewa mutumin da suke cin abinci tare da shi ba zai cutu ko kyamaci yawo da hannu a cikin kwaryar abinci ba, to a nan babu laifi kan ya ci daga ko-ina na kwano; saboda hadisin Sayyidina Anas bin Malik (RA)  a qissar  wani tela da ya gayyaci Manzon Allah (Saww) zuwa cin abinci Anas yace: Sai na ganshi –yana nufin: Annabi (saww) yana bibiyan kabewa daga geffen kwano. Ko kuma idan mutum ya kasance yana cin abincin ne shi kadai; babu wani a tare da shi, ko kuma abincin akwai launukan abun ci da dama; a irin wannan halin ya halatta ya ci abincin da ke gaban waninsa; matuqar dai bai cutar da wani da hakan ba.

4.     Fadin "Alhamdu Lillah" a qarshen abinci: Yana daga cikin ladubban cin abinci Saboda hadisin Abu-umamah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) ya kasance idan aka dauke akwashin abinci bayan kammala cinsa- daga gaba-gare shi sai yace:

Ma'ana: Yabo mai yawa daddada mai albarka sun tabbata ga Allah, Allah Ubangijinmu ba a barin yi masa da'a, ko kuma ace an wadata ga barinsa. (Imam Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5459).

Da kuma wani hadisi da Annabi (saww) ke cewa, Lallai Allah yana rubuta yardarsa ga bawa, idan ya ci abinci ya gode masa akanta, ko ya sha abun sha ya gode masa akansa. (Imamu Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 2734).

5.    Makruhi ne cin abinci a kishingide: Cin abinci a kishingide makaruhine (ma’ana ba lad aba zunubi) Wannan kuma saboda hadisin uwar muminnai A'ishah (RA) tace, Nace: Ya ma'aikin Allah! Ka ci abinci Allah ya sanya ni na zamo fansarka a halin kishingida; saboda zai fiye maka sauqi, Sai manzon Allah (saww) ya karkata kansa har sai da goshinsa ya yi kusan taba qasa, sai yace: A'a! zan ci abinci ne kamar yadda bawa ke cin abinci, zan kuma zauna kamar yadda bawa ke zaunawa. (Albagawiy a cikin littafin "Sharhus sunnah" ya rawaito shi (11/286-287), da Ahmad a "Zuhdu" (5-6) kuma Shu'aibul Arna'ud ya inganta shi da "wani hadisi mursal da ya ke masa shaida", a cikin (Hashiyar sharhus sunnah)
Da kuma saboda hadisin Abu-juhaifah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) yace: Lallai ni bana cin abinci a kishingide. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba 5398).

6.    Mustahabbi ne hanuwa daga aibata abincin da mutum baya son cinsa: Hakika aibata abinci mustahabbine saboda hadisin Abu-hurairah (RA) yace: Manzon Allah (saww) bai taba aibanta abinci ba; idan ya yi sha'awarsa sai ya ci, in kuma bai yi ba, sai ya bari. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5409, da Imamu Muslim a hadisi mai lamba: 2064).

7.    Cin abinci daga geffan masaki, da kuma kasancewar cinsa daga tsakiyar kwarya makruhi ne: saboda hadisin Ibnu-abbas (RA), daga Annabi (Saww) lallai shi an zo masa da masaki da aka sanya kwababben alkubuz da nama mai suna (Sarid), Sai yace: Ku ci daga geffan masakin, kada ku ci daga tsakiyansa, saboda albarka tana sauka ne a tsakiyarsa.

8.     Cin abinci da yatsu guda uku, da kuma sude su bayan kammalawa, shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda hadisin Ka'ab dan Malik (RA) yace: Annabi (Saww) ya kasance yana cin abinci da 'yan yatsunsa guda uku, baya kuma wanke hannunsa har sai ya sude su.  (Imamu Ahmad ya rawaito shi (1/270), da At-tirmiziy (lamba: 1805), ya kuma ce: hadisi ne hasan ingantacce. Da Abu-dawud (lamba: 3772), da Ibnu-majah, (lamba: 3277), Albaniy ya inganta shi (Sahihu sunan Ibni-majah, lamba: 2650)).

9.  Cinye abin da ya zuba ana tsakiyar cin abinci, ko wanda ya warwatsu: Shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda fadinnsa (Saww): Idan lomar dayanku ta fadi to sai ya kade mata kura, sannan ya cinye ta, kada ya barta ga shedan.

10. Sude kwaryar da aka ci abinci a cikinta da lashe yatsu: Shima wannan na daga cikin manyan ladubban cikin abinci saboda fadin Sayyidina Anas (RA) a cikin hadisin da ya gabata, da yake cewa Kuma ya umurce mu yana nufin Annabi (saww) da mu katse kwaryar abinci. Ma'ana: mu sude ta, mu kuma bibiyi abinda ya rage a cikinta na abinci. A wata riwayar kuma aka ce: Annabi (saww) ya umurce mu da mu sude 'yan yatsu da kuma akwashi, yace: Saboda lallai ku ba ku san a ina ne daga cikin abincinku albarkar ta ke ba!.

Jamilu Sani RARAH

Sat 11/03/2016.

Monday, 7 March 2016

NASIRU ZARUMMAI YAYI BAN KWANA

Nasiru Zarummai Ya yi ban kwana da Gidan karya izuwa Gidan Gaskiya. Yanzu ya rage daga shi sai ayukkansa da ya gabatar a Gidan duniya.Sai da me kuma? Hakkinsa da ya rage a gareku abokansa da yaransa da matansa shine, Ku boye sharrinsa, ku yawaita fadin Alkherinsa a zamansa da ku.
Ku yawaita yi masa addu'ah a duk lokacin da kuka tuna shi (akan Allah ya gafarta masa kura kuransa ya kuma yi masa rahama). Abokanansa ku yawaita Ziyarar 'ya'yansa da ya bari da matasa domin jin abubuwanda suke ciki, idan na neman taimako ne ku taimakesu idan na shawara ne ku basu shawara.
Hakika muna kyautata zato na alkheri tare da samun Rahama ga Nasiru Zarummai domin Imamu Ahmad ya ruwaito cewa, Manzon Allah (saww) ya ce, “Babu wani mutum musulmi da zai mutu ranar juma'a ko yini Juma'a face Allah ya kare shi daga fitinar qabari. (Imamu Ahmad 6582-6646).
Marigayi Nasiru ya rasu a ranar Jumu'ah kafin rasuwar Marigayin Shine kwamisinan kimiya da Fasaha a wannan gwamnati mai ci yanzu ta Aminu Waziri Tambuwal. Manazarta suka ce, Tunda ake Mutuwa mutum biyu ne ke mutuwa, daga wanda ya mutu ya huta sai wanda ya mutu aka huta.

Ina rokon Allah jallah wa'Azzah da ya sanya Nasiru Zarummai da sauran mamatan Musulmi cikin wayanda Suka huta.

Jamilu Sani RARAH
Sat 05/03/2016.

Wednesday, 2 March 2016

MASOYAN BUHARI NA GASKIYA KU GAYA MASA

MASOYAN BUHARI NA GASKIYA KU GAYA MASA
*************


Ku Gayawa Buhari kada ya gwada kama duk wani wanda yayi sata a cikin Gwamnatinsa a halin yanzu idan har ya kasance mai gaskiya ne.

 Domin A lokacin khalifancin Sayyidina Umar (RA) ya taba tura Amru bin Aass kasar Misra (Egypt) don ya zama gwamna a cen.Lokacin tafiyar Amru bin Aass yayi Sai Sayyidina Umar (RA) ya tambaye shi, Idan aka zo maka da barawo da laifin sata wane irin hukunci zaka yi masa?

Sai Amru bin Aass (RA) yace: zan yanke masa hannunsa kamar yanda shari'a ta tanada wa masu irin wannan laifin. Sai Sayyidina Umar (RA) ya ce, masa haka ne amma kai ma idan aka sami wani daga masar ya zo min da kukan yunwa kaima zan yanke hannunka.Hakika Shugaba Buhari 'yan Nigeria Musamman talakawa na cikin garari da matsi da yunwa, yana da kyau a duba lamarin talakawa idan akwai abinda za'ayi.

Nayi imani akan cewa, tun ranar da ka shiga Villah bada aljihunka kake sayen Abincin da 'ya'yanka da matanka ke ci ba, haka kuma bada albashin ka suke ci suke sha ba. Duk da kuddin jama'ah suke yi.
Shugaba Buhari ka sani Yahudawa suna ganin cewa, Muddin aka Sanya jama'ah a cikin talauci to kuwa ko mai zasu iya aikatawa.

Wasu da dama suna cikin gararin yunwa da rashin abinci. Hakika bama cewa kai ka kawo talauci amma muna tunatar da kai akan cewa duk wanda ya mutu da yunwa kamar kisan kai ne kuma Sai Allah ya tambayi shuwagabanni a Gobe Qiyama.

A gwamnatin da ta gabata anyi fama da tashe-tashen Bom Babu shakkah dukkan wanda ya mutu a sanadiyar tashin Bom sai Allah (swt) ya isar masa tare da biye masa hakkinsa akan duk wani mai hannu a ciki. Haka kuma duk wanda ya mutu ta dalilin Yunwa ko matsi ko wahala sai Allah ya tambaye ku shuwagabannin mu.

Gyara kayanka.....
 
Jamilu Sani RARAH
Tue 23/02/2016
.