Friday, 15 April 2016

BAYYANAR MADIGO A KASAR HAUSA LAIFINWA? KUMA INA MAFITA?

BAYYANAR MADIGO A KASAR HAUSA LAIFIN WA? INA MAFITA?
************
Sau da dama Idan na tuna halin da wasu daga cikin 'yan matan arewa suka fada na neman Jinsin Su, hakika na kan kasa samun Natsuwa a zuciya ta.

Daga cikin Kashi 100% na 'yan matan Arewa zaka iya samun Kashi 30 Suna wannan mummunar 'dabi'a ta Madigo (Wa'iyazu Billah).

Babban Abin tashin hankali a Yanzu har matan Aure ake samu suna aikata wannan mummunar 'dabi'a ta neman Jinsinsu.

Babban Abin tashin hankali a yanzu wai har aure suke daurawa tsakaninsu (domin biyan bukatar junansu).

Kwanan baya na samu wani labari wanda ya tadarmin da hankali ainun, wannan labari duk mai imanin da ya saurare shi ko ya ji shi to hankalinsa zai tashi matuka.

Wata matace Wacce Shekarunta Sun haura 45 zuwa sama, ta koyar da 'yar cikin ta wannan lalata ta Madigo bayan koyar da ita wai sai kuma ta sanya ta tana nemo mata kananan yara (sa'an 'yar tata) tana koyar da su wannan muguwar dabi'a (Wa'iyazubillah).

Dalilin da yasa asirinsu ya tonu shine, ita yarinyar ta nemo wata wacce take mutuwarso sai mahaifiyar ta ce ta bar mata ita to fa anan ne asiri ya tonu taje ta sanar da mahaifinsu duka sirrinsu da yanda akayi har ta koya mata wannan mummunar 'dabi'a.

Haka kuma Jaridar Leadership Hausa ta Ruwaito wani labari a shekarar 2015 wani magidanci ne matarsa ta tursasa masa kara auren wata aminiyarta.

Bayan ya auri aminiyar tata da 'yan watanni sai Allah ya tona musu asiri in da mijin ya kamasu suna wannan 'dabi'ar ta madigo.

Haka kuma wani magidanci ya kama 'ya'yansa biyu (Ya da Kanwa) sun auri juna. Suma suna biyawa kansu wannan bukatar.

To wannan da me yayi kama? Idan har Mahaifiya zata koyar da 'yarta wannan lalata? Haka Ya ta koyarda Kanwarta wannan lalatar?

Ina mafita Idan har kishiya da Kishiya zasu auri juna su rinka biyawa kansu bukata su manta da Mijinsu?

Babu shakka wannan Ba karamar Masifa bace ta kunno muna ai a Arewacin Nigeria, wanda idan bamu tashi tsaye ba to kuwa akwai babbar matsala wacce zata yi sanadiyar wargajewar wannan nahiya tamu.

Daga cikin Masu wannan laifi akwai iyaye maza domin Kabar 'yarka 'yar shekara 24 ko 25, 26, wani har 30 bata yi aure ba kuma ba tare da tana tattare da wata lalura ba babu shakka wannan na sanadiyar faruwar wanan abu.

Hakika akwai lalura domin akwai matan da Aljannune ke hana su aure wasu kuma kawai ganin duk abinda take nema tana samu yakan sanya takiyin auren.

Babu shakka wayannan Wayoyi da muke amfani dasu sune manyan musabbabin Wannan lalacewar da wasummu sukayi.

Hakika ya zama dole ga dukkaninMu mu rika kula da matanmu da Qannenmu shin da wa suke Hulda? Kuma wace Hulda suke yi a tsakaninsu? Kuma ya halayen Qawayensu da suke?

Babu shakka wannan ba karamar taimakwa zaiyi ba wajen magance wannan matsalar. Mu tuna a cikin Alqur'ani Allah yana Ce Mana; YA! KU WAYANDA KUKAYI IMAMI KU TSARE KANKU DA IYALANKU DAGA WUTA.

Hakika Duk masuyin wannan mummunar 'dabi'a suji tsoron Allah su tuba kuma su san cewa, Wallahi Duk mai yin Wannan 'dabi'ah kuma ta mutu tana aikatata wallahi Allah zai azabartarda ita sosai da sosai kuma zata hadu da mummunar makoma a cikin Qabarinta.

Jamilu Sani RARAH.
Fri 15/04/2016

Saturday, 12 March 2016

LADUBBAN CIN ABINCI A MUSULUNCI

 LADUBBAN CIN ABINCI YA KAMATA KOWA YA SANSU
**********
Addinin musulunci addini ne mai girma da tsari, addini ne da bai bar wani abu aboye ba face yayi bayani akansa domin musulmai ya ribantu da abin, lura da wannan, addinin Musulunci ya zo da ladduba masu yawa da kuma tarin amfani dangane da shiga makewayi da kuma fita daga makewayin. Haka ya sake bayani kan ladduban cin abinci, da sauran abubuwa da suka kama daga saduwa, sanya sutura, kwanciya da sauransu. Ga dai kadan daga cikin ladduban cin abinci, kamar haka:

1.  Fadin BISMILLAH a lokacin fara cin abinci: Babu ko shakkah fadin bisimillah shine ladabi na farko wajen cin abinci saboda an karbo hadisi daga Umar bin Abiy-salamah (RA) yace: Na kasance yaro qarqashin kulawar Manzon Allah (saww) kuma hanuna ya kasance yana yawo a cikin akwashin abinci, sai yace dani: Ya kai yaro! Ka ambaci sunan Allah (ma’ana kayi Bisimillah) , ka ci da hanunka na dama, ka kuma ci daga abinda ke gabanka.
Jabir yace:- Daga wannan lokacin ban gushe ba; wannan ne irin cin abincina.
(Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5376, da Imamu Muslim hadisi mai lamba: 2022).

2.   Cin abinci da hannun dama: Hakika cin abinci da hannun dama shine ladabi na biyu daga ladubban cin abinci, Wannan kuma sunna ne saboda hadisin da ya gabata.

3.   Mutum ya ci gabansa: Shima wannan sunna ne saboda hadisin da ya gabata. Sai dai idan mutum ya san cewa mutumin da suke cin abinci tare da shi ba zai cutu ko kyamaci yawo da hannu a cikin kwaryar abinci ba, to a nan babu laifi kan ya ci daga ko-ina na kwano; saboda hadisin Sayyidina Anas bin Malik (RA)  a qissar  wani tela da ya gayyaci Manzon Allah (Saww) zuwa cin abinci Anas yace: Sai na ganshi –yana nufin: Annabi (saww) yana bibiyan kabewa daga geffen kwano. Ko kuma idan mutum ya kasance yana cin abincin ne shi kadai; babu wani a tare da shi, ko kuma abincin akwai launukan abun ci da dama; a irin wannan halin ya halatta ya ci abincin da ke gaban waninsa; matuqar dai bai cutar da wani da hakan ba.

4.     Fadin "Alhamdu Lillah" a qarshen abinci: Yana daga cikin ladubban cin abinci Saboda hadisin Abu-umamah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) ya kasance idan aka dauke akwashin abinci bayan kammala cinsa- daga gaba-gare shi sai yace:

Ma'ana: Yabo mai yawa daddada mai albarka sun tabbata ga Allah, Allah Ubangijinmu ba a barin yi masa da'a, ko kuma ace an wadata ga barinsa. (Imam Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5459).

Da kuma wani hadisi da Annabi (saww) ke cewa, Lallai Allah yana rubuta yardarsa ga bawa, idan ya ci abinci ya gode masa akanta, ko ya sha abun sha ya gode masa akansa. (Imamu Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 2734).

5.    Makruhi ne cin abinci a kishingide: Cin abinci a kishingide makaruhine (ma’ana ba lad aba zunubi) Wannan kuma saboda hadisin uwar muminnai A'ishah (RA) tace, Nace: Ya ma'aikin Allah! Ka ci abinci Allah ya sanya ni na zamo fansarka a halin kishingida; saboda zai fiye maka sauqi, Sai manzon Allah (saww) ya karkata kansa har sai da goshinsa ya yi kusan taba qasa, sai yace: A'a! zan ci abinci ne kamar yadda bawa ke cin abinci, zan kuma zauna kamar yadda bawa ke zaunawa. (Albagawiy a cikin littafin "Sharhus sunnah" ya rawaito shi (11/286-287), da Ahmad a "Zuhdu" (5-6) kuma Shu'aibul Arna'ud ya inganta shi da "wani hadisi mursal da ya ke masa shaida", a cikin (Hashiyar sharhus sunnah)
Da kuma saboda hadisin Abu-juhaifah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) yace: Lallai ni bana cin abinci a kishingide. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba 5398).

6.    Mustahabbi ne hanuwa daga aibata abincin da mutum baya son cinsa: Hakika aibata abinci mustahabbine saboda hadisin Abu-hurairah (RA) yace: Manzon Allah (saww) bai taba aibanta abinci ba; idan ya yi sha'awarsa sai ya ci, in kuma bai yi ba, sai ya bari. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5409, da Imamu Muslim a hadisi mai lamba: 2064).

7.    Cin abinci daga geffan masaki, da kuma kasancewar cinsa daga tsakiyar kwarya makruhi ne: saboda hadisin Ibnu-abbas (RA), daga Annabi (Saww) lallai shi an zo masa da masaki da aka sanya kwababben alkubuz da nama mai suna (Sarid), Sai yace: Ku ci daga geffan masakin, kada ku ci daga tsakiyansa, saboda albarka tana sauka ne a tsakiyarsa.

8.     Cin abinci da yatsu guda uku, da kuma sude su bayan kammalawa, shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda hadisin Ka'ab dan Malik (RA) yace: Annabi (Saww) ya kasance yana cin abinci da 'yan yatsunsa guda uku, baya kuma wanke hannunsa har sai ya sude su.  (Imamu Ahmad ya rawaito shi (1/270), da At-tirmiziy (lamba: 1805), ya kuma ce: hadisi ne hasan ingantacce. Da Abu-dawud (lamba: 3772), da Ibnu-majah, (lamba: 3277), Albaniy ya inganta shi (Sahihu sunan Ibni-majah, lamba: 2650)).

9.  Cinye abin da ya zuba ana tsakiyar cin abinci, ko wanda ya warwatsu: Shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda fadinnsa (Saww): Idan lomar dayanku ta fadi to sai ya kade mata kura, sannan ya cinye ta, kada ya barta ga shedan.

10. Sude kwaryar da aka ci abinci a cikinta da lashe yatsu: Shima wannan na daga cikin manyan ladubban cikin abinci saboda fadin Sayyidina Anas (RA) a cikin hadisin da ya gabata, da yake cewa Kuma ya umurce mu yana nufin Annabi (saww) da mu katse kwaryar abinci. Ma'ana: mu sude ta, mu kuma bibiyi abinda ya rage a cikinta na abinci. A wata riwayar kuma aka ce: Annabi (saww) ya umurce mu da mu sude 'yan yatsu da kuma akwashi, yace: Saboda lallai ku ba ku san a ina ne daga cikin abincinku albarkar ta ke ba!.

Jamilu Sani RARAH

Sat 11/03/2016.

LADUBBAN CIN ABINCI

 LADUBBAN CIN ABINCI YA KAMATA KOWA YA SANSU
**********
Addinin musulunci addini ne mai girma da tsari, addini ne da bai bar wani abu aboye ba face yayi bayani akansa domin musulmai ya ribantu da abin, lura da wannan, addinin Musulunci ya zo da ladduba masu yawa da kuma tarin amfani dangane da shiga makewayi da kuma fita daga makewayin. Haka ya sake bayani kan ladduban cin abinci, da sauran abubuwa da suka kama daga saduwa, sanya sutura, kwanciya da sauransu. Ga dai kadan daga cikin ladduban cin abinci, kamar haka:

1.  Fadin BISMILLAH a lokacin fara cin abinci: Babu ko shakkah fadin bisimillah shine ladabi na farko wajen cin abinci saboda an karbo hadisi daga Umar bin Abiy-salamah (RA) yace: Na kasance yaro qarqashin kulawar Manzon Allah (saww) kuma hanuna ya kasance yana yawo a cikin akwashin abinci, sai yace dani: Ya kai yaro! Ka ambaci sunan Allah (ma’ana kayi Bisimillah) , ka ci da hanunka na dama, ka kuma ci daga abinda ke gabanka.
Jabir yace:- Daga wannan lokacin ban gushe ba; wannan ne irin cin abincina.
(Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5376, da Imamu Muslim hadisi mai lamba: 2022).

2.   Cin abinci da hannun dama: Hakika cin abinci da hannun dama shine ladabi na biyu daga ladubban cin abinci, Wannan kuma sunna ne saboda hadisin da ya gabata.

3.   Mutum ya ci gabansa: Shima wannan sunna ne saboda hadisin da ya gabata. Sai dai idan mutum ya san cewa mutumin da suke cin abinci tare da shi ba zai cutu ko kyamaci yawo da hannu a cikin kwaryar abinci ba, to a nan babu laifi kan ya ci daga ko-ina na kwano; saboda hadisin Sayyidina Anas bin Malik (RA)  a qissar  wani tela da ya gayyaci Manzon Allah (Saww) zuwa cin abinci Anas yace: Sai na ganshi –yana nufin: Annabi (saww) yana bibiyan kabewa daga geffen kwano. Ko kuma idan mutum ya kasance yana cin abincin ne shi kadai; babu wani a tare da shi, ko kuma abincin akwai launukan abun ci da dama; a irin wannan halin ya halatta ya ci abincin da ke gaban waninsa; matuqar dai bai cutar da wani da hakan ba.

4.     Fadin "Alhamdu Lillah" a qarshen abinci: Yana daga cikin ladubban cin abinci Saboda hadisin Abu-umamah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) ya kasance idan aka dauke akwashin abinci bayan kammala cinsa- daga gaba-gare shi sai yace:

Ma'ana: Yabo mai yawa daddada mai albarka sun tabbata ga Allah, Allah Ubangijinmu ba a barin yi masa da'a, ko kuma ace an wadata ga barinsa. (Imam Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5459).

Da kuma wani hadisi da Annabi (saww) ke cewa, Lallai Allah yana rubuta yardarsa ga bawa, idan ya ci abinci ya gode masa akanta, ko ya sha abun sha ya gode masa akansa. (Imamu Muslim ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 2734).

5.    Makruhi ne cin abinci a kishingide: Cin abinci a kishingide makaruhine (ma’ana ba lad aba zunubi) Wannan kuma saboda hadisin uwar muminnai A'ishah (RA) tace, Nace: Ya ma'aikin Allah! Ka ci abinci Allah ya sanya ni na zamo fansarka a halin kishingida; saboda zai fiye maka sauqi, Sai manzon Allah (saww) ya karkata kansa har sai da goshinsa ya yi kusan taba qasa, sai yace: A'a! zan ci abinci ne kamar yadda bawa ke cin abinci, zan kuma zauna kamar yadda bawa ke zaunawa. (Albagawiy a cikin littafin "Sharhus sunnah" ya rawaito shi (11/286-287), da Ahmad a "Zuhdu" (5-6) kuma Shu'aibul Arna'ud ya inganta shi da "wani hadisi mursal da ya ke masa shaida", a cikin (Hashiyar sharhus sunnah)
Da kuma saboda hadisin Abu-juhaifah (RA) yace: Manzon Allah (Saww) yace: Lallai ni bana cin abinci a kishingide. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba 5398).

6.    Mustahabbi ne hanuwa daga aibata abincin da mutum baya son cinsa: Hakika aibata abinci mustahabbine saboda hadisin Abu-hurairah (RA) yace: Manzon Allah (saww) bai taba aibanta abinci ba; idan ya yi sha'awarsa sai ya ci, in kuma bai yi ba, sai ya bari. (Imamu Bukhariy ya rawaito shi a hadisi mai lamba: 5409, da Imamu Muslim a hadisi mai lamba: 2064).

7.    Cin abinci daga geffan masaki, da kuma kasancewar cinsa daga tsakiyar kwarya makruhi ne: saboda hadisin Ibnu-abbas (RA), daga Annabi (Saww) lallai shi an zo masa da masaki da aka sanya kwababben alkubuz da nama mai suna (Sarid), Sai yace: Ku ci daga geffan masakin, kada ku ci daga tsakiyansa, saboda albarka tana sauka ne a tsakiyarsa.

8.     Cin abinci da yatsu guda uku, da kuma sude su bayan kammalawa, shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda hadisin Ka'ab dan Malik (RA) yace: Annabi (Saww) ya kasance yana cin abinci da 'yan yatsunsa guda uku, baya kuma wanke hannunsa har sai ya sude su.  (Imamu Ahmad ya rawaito shi (1/270), da At-tirmiziy (lamba: 1805), ya kuma ce: hadisi ne hasan ingantacce. Da Abu-dawud (lamba: 3772), da Ibnu-majah, (lamba: 3277), Albaniy ya inganta shi (Sahihu sunan Ibni-majah, lamba: 2650)).

9.  Cinye abin da ya zuba ana tsakiyar cin abinci, ko wanda ya warwatsu: Shima yana daga cikin ladubban cin abinci saboda fadinnsa (Saww): Idan lomar dayanku ta fadi to sai ya kade mata kura, sannan ya cinye ta, kada ya barta ga shedan.

10. Sude kwaryar da aka ci abinci a cikinta da lashe yatsu: Shima wannan na daga cikin manyan ladubban cikin abinci saboda fadin Sayyidina Anas (RA) a cikin hadisin da ya gabata, da yake cewa Kuma ya umurce mu yana nufin Annabi (saww) da mu katse kwaryar abinci. Ma'ana: mu sude ta, mu kuma bibiyi abinda ya rage a cikinta na abinci. A wata riwayar kuma aka ce: Annabi (saww) ya umurce mu da mu sude 'yan yatsu da kuma akwashi, yace: Saboda lallai ku ba ku san a ina ne daga cikin abincinku albarkar ta ke ba!.

Jamilu Sani RARAH

Sat 11/03/2016.

Monday, 7 March 2016

NASIRU ZARUMMAI YAYI BAN KWANA

Nasiru Zarummai Ya yi ban kwana da Gidan karya izuwa Gidan Gaskiya. Yanzu ya rage daga shi sai ayukkansa da ya gabatar a Gidan duniya.Sai da me kuma? Hakkinsa da ya rage a gareku abokansa da yaransa da matansa shine, Ku boye sharrinsa, ku yawaita fadin Alkherinsa a zamansa da ku.
Ku yawaita yi masa addu'ah a duk lokacin da kuka tuna shi (akan Allah ya gafarta masa kura kuransa ya kuma yi masa rahama). Abokanansa ku yawaita Ziyarar 'ya'yansa da ya bari da matasa domin jin abubuwanda suke ciki, idan na neman taimako ne ku taimakesu idan na shawara ne ku basu shawara.
Hakika muna kyautata zato na alkheri tare da samun Rahama ga Nasiru Zarummai domin Imamu Ahmad ya ruwaito cewa, Manzon Allah (saww) ya ce, “Babu wani mutum musulmi da zai mutu ranar juma'a ko yini Juma'a face Allah ya kare shi daga fitinar qabari. (Imamu Ahmad 6582-6646).
Marigayi Nasiru ya rasu a ranar Jumu'ah kafin rasuwar Marigayin Shine kwamisinan kimiya da Fasaha a wannan gwamnati mai ci yanzu ta Aminu Waziri Tambuwal. Manazarta suka ce, Tunda ake Mutuwa mutum biyu ne ke mutuwa, daga wanda ya mutu ya huta sai wanda ya mutu aka huta.

Ina rokon Allah jallah wa'Azzah da ya sanya Nasiru Zarummai da sauran mamatan Musulmi cikin wayanda Suka huta.

Jamilu Sani RARAH
Sat 05/03/2016.

Wednesday, 2 March 2016

MASOYAN BUHARI NA GASKIYA KU GAYA MASA

MASOYAN BUHARI NA GASKIYA KU GAYA MASA
*************


Ku Gayawa Buhari kada ya gwada kama duk wani wanda yayi sata a cikin Gwamnatinsa a halin yanzu idan har ya kasance mai gaskiya ne.

 Domin A lokacin khalifancin Sayyidina Umar (RA) ya taba tura Amru bin Aass kasar Misra (Egypt) don ya zama gwamna a cen.Lokacin tafiyar Amru bin Aass yayi Sai Sayyidina Umar (RA) ya tambaye shi, Idan aka zo maka da barawo da laifin sata wane irin hukunci zaka yi masa?

Sai Amru bin Aass (RA) yace: zan yanke masa hannunsa kamar yanda shari'a ta tanada wa masu irin wannan laifin. Sai Sayyidina Umar (RA) ya ce, masa haka ne amma kai ma idan aka sami wani daga masar ya zo min da kukan yunwa kaima zan yanke hannunka.Hakika Shugaba Buhari 'yan Nigeria Musamman talakawa na cikin garari da matsi da yunwa, yana da kyau a duba lamarin talakawa idan akwai abinda za'ayi.

Nayi imani akan cewa, tun ranar da ka shiga Villah bada aljihunka kake sayen Abincin da 'ya'yanka da matanka ke ci ba, haka kuma bada albashin ka suke ci suke sha ba. Duk da kuddin jama'ah suke yi.
Shugaba Buhari ka sani Yahudawa suna ganin cewa, Muddin aka Sanya jama'ah a cikin talauci to kuwa ko mai zasu iya aikatawa.

Wasu da dama suna cikin gararin yunwa da rashin abinci. Hakika bama cewa kai ka kawo talauci amma muna tunatar da kai akan cewa duk wanda ya mutu da yunwa kamar kisan kai ne kuma Sai Allah ya tambayi shuwagabanni a Gobe Qiyama.

A gwamnatin da ta gabata anyi fama da tashe-tashen Bom Babu shakkah dukkan wanda ya mutu a sanadiyar tashin Bom sai Allah (swt) ya isar masa tare da biye masa hakkinsa akan duk wani mai hannu a ciki. Haka kuma duk wanda ya mutu ta dalilin Yunwa ko matsi ko wahala sai Allah ya tambaye ku shuwagabannin mu.

Gyara kayanka.....
 
Jamilu Sani RARAH
Tue 23/02/2016
.

TARIHIN KASAR ANDALUS (SPAIN)

TARIHIN DAULAR MUSULUNCI TA ANDALUS (SPAIN).


GABATARWA
Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin Allah su tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabi (saww), da Iyalansa da Sahabbansa da duk wayanda suka bi hanyarsu har ya zuwa ranar sakamako.

Bayan haka Ganin irin yanda al'ummar mu suka yi watsi ko wurgi da tarihin kasa mai matukar muhimmanci ga musulmi naga dacewar in bayar da wannan tarihi na Kasar Andalus ko Ince Spain a yanzu.
Andalus kasa ce mai tarihin gaske wanda ban isa in iya bada tarihnta duka ba sai dai in dan tsakuro wani abu in gabatar muku da shi, Kasar Andalus tayi zama kashi 95 cikin 100 na cikinta musulmi ne kashi 5 ne ba musulmi ba. Daga baya ne Yahudawa suka shiga kasar suka hada rikici tsakanin musulman kasar suka mamaye kasar suka kashe manyan malaman kasar suka cenja sunan garin da sunan garuruwan zuwa wasu suna na daban daga karshe ma sai da takai kafiran garin sune da kaso 95 musulmai kuma sune da kashi 5 daga cikin 100.

Kasar Andulus wadda a yau ake kira spain kasa ce wadda ta tara manyan-manyan malaman musulunci. kasa ce wadda ta tara gine-ginen musulunci na tarihi.

Akwai wani masallaci da ke garin Qurdaba a cikin kasar ta Andalus. a lokacin idan an debe masallacin ka'aba da masallacin Annabi dake madina duk duniya ba masallacin dake bada abin mamaki irin masallacin na qurdaba dake kasar ta Andalus.
Garin na Qurdab na daga cikin garuruwan da yahudawa suka cenjawa suna yanzu haka ana kiran garin da suna cordoba.
                                                             Massallachin Qurdab
Masallacin garin na Qurdab tarihi ya nuna manyan-manyan malamai ne suke karantar da hadisi ba dare ba rana a cikinsa Malaman tarihi sunce babu Ranar da ba'a karanta hadisin Annabi (saww) kasa da dubu 10 a cikin masallacin. Baya ga haka masallacin na game da labrary wacce akwai littafai daban-daban acikinsa (babu kalar littafen da zaka nema a ciki baka same shi ba).

Manya-manyan daliban Imamu malik sune suke rike da masallacin. irinsu Yahaya bin Yahaya an andulusiy (Mutumen andalus) wanda shine mutumen da ya ruwaito muwadda na Imamu Malik daga Imamu Malik bin Anas.Baya ga shi akwai malamai da yawa da sunka fito daga sassa daban-daban na kasar.

Kasar ta Andalus tafara kasancewa Cibiyar musulunci hijirar Annabi (Saww) nada shekara 163. shekaru 16 gabanin rasuwar Imamu Malik bin Anas. kuma shekaru 69 da rasuwar Anas bin Malik daya daga cikin manyan sahabban Annabi (Saww).

Akwai malamai da yawa a kasar ta Andalus irinsu Ibn Hazbin Al-andalusiy da Imamu Qurdabi wanda yayi tafsirin aljam'un li ahakamun qur'an, wanda ankafi sani da tafsirin qurdabi. Akwai irinsu Ibn Rushidin al-Andulusi. akwai Ibn Al-Arabi wanda yayi tafsirin Ahakamu Qur'an.

 Wayannan kadan kenan daga malaman da sunka fito daga kasar ta Andalus. Kasar taci gaba da zama Cibiyar musulunci har sai da ankayi shekaru sama da 800 musulunci.

Ranar da Yahudawa sunka saka Andalus a gaba kasan cewa duka ka'idodin musulunci ake bi a kasar da kewaye har kafirai basa sha'awan shiga kasa, amma randa suka kularwa kasar ba'a dauki shekaru 50 ba saida suka juyar da musuluncin.sunka rushe duk wani abu na musulunci akasar. In shaa Allahu tarihi ya kan kama. Zan ci gaba.

 Jamilu Sani RARAH
Tue 01/03/2016.

Saturday, 20 February 2016

SAKO ZUWA GA MATASA

SAKO ZUWA GA MATASAN AREWA.
*********
Dukkan Godiya ta tabbatta ga Allah Ubangijin halittu. Salati da sallama su kara tabbata ga shugaban Manzanni, Muhammadu 'dan Abdullahi tare da iyalanSa da sahabbanSa da duk wayanda suka bi tafarkinsu har ya zuwa ranar Sakamako.

Wannan Sako Nawa ya shafi dukkanin Matasa 'yan Arewa musamman ma masu kishi tare da kaunar Arewa a zukatansu.

Hakika abinda ke faruwa a Facebook, Instagram, Twitter yana daga cikin dubban abubuwan da ke kawo matsala tare da tawayar arzikin da muke fama da su a halin yanzu.

Hakika ina lura tare da kula da cewa, babu wata rana ko wani dare da zan hau social media ba tare da na tarar wani ya aibata Shugaba Buhari ko wani daga cikin 'yan adawa ba.

Hakika zagin juna da cin mutuncin juna na daga cikin abubuwan da ke kawo matsala a wannan rayuwa da muke ciki.

Wani daga ya hau Facebook ba zaka ji ya fadi wata kalma ta alkheri abakinsa ba kawai zaka ji yana kokarin ci mutuncin da zagin 'yan adawarsa ne tare da kirkiro wasu maganganu marar tushe ya saka a bayanan nasa.

Ta 'bangaren Masoya Shugaban kasa Buhari zaka ji suna fadin, Rusashsiyar jam'iyar PDP, ko kuma Jam'iya mai kashin Mutane, ko kai tsaye kaji mutum yace, Jam'iyar kafirai.

To meye amfanin wannan? Ta bangaren 'yan jam'iyar ta PDP kuma zakaji suna Cewa, Tsohon nan ya kawo talauci, Tshohon nan yawonsa yayi yawa, Tsohon nan bazai iya gyara ba. Da dai wasu zan tuka marar amfani.

Shin ko mun Manta Abinda Allah (swt) ke fadi a citkin Alqur'ani mai Girma? Cewa, "SHIN BAKA GANI BA, YADDA ALLAH YA BUGA WANI MISALI; KALMA MAI KYAU, KAMAR BISHIYA CE MAI KYAU; TUSHENTA YANA TABBATACCE, RESSANTA KUMA SUNA CIKIN SAMA* TANA BAYAR DA ABINCINTA, A KOWANI LOKACI DA IZNIN UBANGIJINTA" (Suratul Ibrahim aya ta 24 zuwa 25).

A wani hadisi kuma Manzon Allah (saww) Cewa yayi, Sadaka ta zama wajibi a kan kowani Musulmi, Sai aka ce: To idan bai samu abin sadakar ba fa? Sai ya ce: Yayi aiki da hannayensa; sai ya amfanar da kansa, ya kuma yi sadaka. Sai aka sake tambayarsa: To idan bai samu iko ba fa? Sai ya ce: Ya taimaki ma'abucin buqata; wanda aka zalunta. Sai aka ce masa: To idan bai samu iko ba fa? Sai yace: Ya yi umurni da kyakkyawa, ko da alkhairi. Sai aka tambaye shi: To idan bai aikata ba fa? Sai ya ce: Sai ya kame daga aikata sharri; don yin hakan sadaka ne ".

Shin me yasa muke aibata 'yan uwanmu maimakon muyi shiru ko dan yin hakan ya zama sadaka a garemu?

Kusani ya Matasa Manzon Allah (saww) ya zo ne don ya zama aminci da rahama; kuma don ya tsamar da Mutane daga duhu zuwa ga haske. kamar cika alqawari, hana zalunci tare da qetare iyaka, da tsayar da adalci, da tunkude zalunci.

Ya kai me kiran PDP da Rusasshiyar Jam'iya, Ya kai mai Kiran Shugaba Buhari ya kashe Nigeria muyiwa Allah mu daina ko abubuwa zasu mana sauki.

Allah (Swt) Yana Cewa, "AKWAI TSAMMANIN UBANGIJINKU YA HALAKA MAQIYANKU, SAI YA BAKU MAYEWA A DORON QASA, DON YA GA YAYA ZAKU AIKATAWA (Suratul A'araf aya ta 129).

Hakika dukkan 'yan adawarku su mutu a barku a cikin duniya ba zata karaku da komai ba hasalima babu wani abu da zaku karu da shi sai hasara da tabewa (Allah ya tsare mu).

Ya 'dan uwa matashi kada arude ka da siyasa kaje ka manta dalilin da yasa aka halicce ka a duniya.

Da wannan Nake Rokon Matasa akan mu daina aibata junan mu saboda wani banbanci na siyasa

Haka kuma ina kira ga Shuwagabannin da suyi qoqarin tabbatar da zaman lafiya; ta hanyar tsayar da adalci, tabbatar da gaskiya. Kuma shugabani yakama ta su san wajibi ne  akansu su yi qoqari wajen aikata duk abinda zai amfani talakawa, da tunkude musu abinda zai cutar da su a cikin addininsu da duniyarsu.

Yana da kyau Malamai su san cewa, sune halifofin Manzanni, kuma magada Annabawa. Don haka wajibi ne akan ma'abuta ilimi su kare al'umma daga cutar jahilci, ko rugujewar aqidu da
lalacewansu. Sannan su riqa
haskaka hanyoyi ga Mutane ta
hanyar fada musu duk wasu abubuwan da suka shige musu
duhu.

Wajibine su tashi tsaye wajen ilmantar da Mutane lamuran addininsu da Siyasa; Saboda shi malami yana gyara abinda Mutane suka bata ne, yana! kuma fadakar da su zuwa ga alkhairi, tare da yin umurni da kyawawa, da kuma hani kan munana.

Ina Rokon Allah ya amfanar da mu Tare da Amintar damu aduk inda muke.

Allah (Swt) a cikin Alqur'ani Mai Girma yana Cewa, "Ya ku Mutane lallai ne alkawarin Allah gaskiya ne; kada rayuwar duniya ta rude ku, kuma kada mai rudi (wato Shedan) ya rude ku daga
Allah" (Suratul Luqman ayata 33).

Jamilu Sani RARAH
Sat 20/02/2016.