TARIHIN DAULAR MUSULUNCI TA ANDALUS (SPAIN).
GABATARWA
Da sunan Allah mai yawan rahama mai yawan jinkai, tsira da amincin
Allah su tabbata ga fiyayyan halittar Allah Annabi (saww), da Iyalansa
da Sahabbansa da duk wayanda suka bi hanyarsu har ya zuwa ranar
sakamako.
Bayan haka Ganin irin yanda al'ummar mu suka yi watsi
ko wurgi da tarihin kasa mai matukar muhimmanci ga musulmi naga dacewar
in bayar da wannan tarihi na Kasar Andalus ko Ince Spain a yanzu.
Andalus kasa ce mai tarihin gaske wanda ban isa in iya bada tarihnta
duka ba sai dai in dan tsakuro wani abu in gabatar muku da shi, Kasar
Andalus tayi zama kashi 95 cikin 100 na cikinta musulmi ne kashi 5 ne ba
musulmi ba. Daga baya ne Yahudawa suka shiga kasar suka hada rikici
tsakanin musulman kasar suka mamaye kasar suka kashe manyan malaman
kasar suka cenja sunan garin da sunan garuruwan zuwa wasu suna na daban
daga karshe ma sai da takai kafiran garin sune da kaso 95 musulmai kuma
sune da kashi 5 daga cikin 100.
Kasar Andulus wadda a yau ake
kira spain kasa ce wadda ta tara manyan-manyan malaman musulunci. kasa
ce wadda ta tara gine-ginen musulunci na tarihi.
Akwai wani
masallaci da ke garin Qurdaba a cikin kasar ta Andalus. a lokacin idan
an debe masallacin ka'aba da masallacin Annabi dake madina duk duniya ba
masallacin dake bada abin mamaki irin masallacin na qurdaba dake kasar
ta Andalus.
Garin na Qurdab na daga cikin garuruwan da yahudawa suka cenjawa suna yanzu haka ana kiran garin da suna cordoba.
Massallachin Qurdab
Masallacin garin na Qurdab tarihi ya nuna manyan-manyan malamai ne suke karantar da hadisi ba dare ba rana a cikinsa Malaman tarihi sunce babu Ranar da ba'a karanta hadisin Annabi (saww)
kasa da dubu 10 a cikin masallacin. Baya ga haka masallacin na game da
labrary wacce akwai littafai daban-daban acikinsa (babu kalar littafen
da zaka nema a ciki baka same shi ba).
Manya-manyan daliban Imamu
malik sune suke rike da masallacin. irinsu Yahaya bin Yahaya an
andulusiy (Mutumen andalus) wanda shine mutumen da ya ruwaito muwadda na
Imamu Malik daga Imamu Malik bin Anas.Baya ga shi akwai malamai da yawa da sunka fito daga sassa daban-daban na kasar.
Kasar ta Andalus tafara kasancewa Cibiyar musulunci hijirar Annabi
(Saww) nada shekara 163. shekaru 16 gabanin rasuwar Imamu Malik bin
Anas. kuma shekaru 69 da rasuwar Anas bin Malik daya daga cikin manyan
sahabban Annabi (Saww).
Akwai malamai da yawa a kasar ta Andalus irinsu Ibn Hazbin Al-andalusiy da Imamu Qurdabi wanda yayi tafsirin aljam'un li ahakamun qur'an, wanda ankafi sani da tafsirin qurdabi. Akwai irinsu Ibn Rushidin al-Andulusi. akwai Ibn Al-Arabi wanda yayi tafsirin Ahakamu Qur'an.
Wayannan kadan kenan daga malaman da sunka fito daga kasar ta Andalus.
Kasar taci gaba da zama Cibiyar musulunci har sai da ankayi shekaru sama
da 800 musulunci.
Ranar da Yahudawa sunka saka Andalus a gaba
kasan cewa duka ka'idodin musulunci ake bi a kasar da kewaye har kafirai
basa sha'awan shiga kasa, amma randa suka kularwa kasar ba'a dauki
shekaru 50 ba saida suka juyar da musuluncin.sunka rushe duk wani abu na
musulunci akasar. In shaa Allahu tarihi ya kan kama. Zan ci gaba.
Jamilu Sani RARAH
Tue 01/03/2016.
Gaskiya na yaba sosai da wannan kokari naka amma idan kasamu lokaci kakawo dalilanda suka janyo nasarar yahudawa a Andalusia domin sarakunan mu,malaman mu da Matasan mu su fadaka.
ReplyDeleteIn shaa Allahu zan kokarta haka din
DeleteThanks
DeleteGaskiya ne
DeleteAllah ya saka ma DA l alkhairi
ReplyDeleteAllah ya saka da alkairi
ReplyDeleteAllah yayi maka albarka kuma
ReplyDeleteJamel sani Allah yasaka da alkairi
ReplyDelete