Friday, 9 December 2016

SALLAR JUMA'A DA WASSU DAGA CIKIN HUKUNCE- HUKUNCENTA ( ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺃﺣﻜﺎﻣﻬﺎ )

SALLAR JUMA'A DA WASSU
DAGA CIKIN HUKUNCE-
HUKUNCENTA ( ﺻﻼﺓ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻭﺃﺣﻜﺎﻣﻬﺎ )

Bismillahir rahmanir rahim.
Wassalatu wassalamu ala rasulillah,
Bayan haka:

A nan –da izinin Allah- zamu gabatar da bayanai ne akan "sallar juma'a" da
wassu daga cikin hukunce-hukuncenta,
kamar haka:

Na Daya: Hukuncin yin sallar juma'a da
dalilinsa: Zuwa sallar juma'a farilla ce akan mazaje; saboda fadin Allah madaukaki:

}ﻳَﺎ ﺃَﻳُّﻬَﺎ ﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﺁﻣَﻨُﻮﺍ ﺇِﺫَﺍ ﻧُﻮﺩِﻱَ ﻟِﻠﺼَّﻼَﺓِ ﻣِﻦْ ﻳَﻮْﻡِ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ، ﻓَﺎﺳْﻌَﻮْﺍ ﺇِﻟَﻰ ﺫِﻛْﺮِ ﺍﻟﻠﻪِ ﻭَﺫَﺭُﻭﺍ ﺍﻟْﺒَﻴْﻊَ { ‏[ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ : ٩‏]

Ma'ana: (Ya ku wadanda suka yi imani
idan aka kira sallah a ranar juma'a to
ku tafi zuwa ga ambaton Allah, kuma ku bar kasuwanci) [Jumu'a: 9]. Da kuma saboda fadinsa (SAW):

"ﺭَﻭَﺍﺡُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺤْﺘَﻠِﻢ "‏( [1]‏) .

Ma'ana: (Tafiya sallar juma'a wajibi ne
akan kowani baligi). Da kuma saboda
fadinsa (SAW):

" ﻟَﻴَﻨْﺘَﻬِﻴَﻦَّ ﺃَﻗْﻮَﺍﻡٌ ﻋَﻦْ ﻭَﺩْﻋِﻬِﻢُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺎﺕِ، ﺃَﻭْ ﻟَﻴَﺨْﺘِﻤَﻦَّ ﺍﻟﻠﻪُ ﻋَﻠَﻰ
ﻗُـﻠُﻮﺑِﻬِﻢْ، ﺛُﻢَّ ﻟَـﻴُﻜﻮﻧﻦَّ ﻣِﻦَ ﺍﻟـﻐَـﺎﻓِﻠِﻲﻥ "‏( [2]‏) .

Ma'ana: (Wassu mutane su hanu kan
barin halartar juma'o'i, ko kuma Allah
ya yi rufi akan zukatansu, sa'annan su
kasance daga cikin gafalallu
rafkanannu).

Annawawiy yana cewa:
" ﻓﻴﻪ : ﺃﻥّ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ ﻓﺮﺽُ ﻋَﻴﻦ "‏( [3]‏) .
Ma'ana: (A cikin wannan hadisin akwai
bayani dake nuna cewa lallai sallar
juma'a wajibi ce ga kowani mutum). Da
kuma saboda hadisi mai zuwa bayan
Dan lokaci kaxan , wanda a cikinsa aka ce:

"ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔُ ﺣَﻖٌّ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺴْﻠِﻢ "...‏( [4]‏) .

Ma'ana: (Juma'a haqqi ne na wajibi
akan kowani musulmi…).

NA BIYU: Ga wa juma'a take wajaba?

"SALLAR Juma'a" tana wajaba ga kowani musulmi, namiji, da , baligi, mai hankali, wanda ke da ikon halartarta, mazaunin gida; Bata kuma wajaba ga: Bawa, ko mace, ko yaro, ko mahaukaci, ko maras lafiya, ko matafiyi; wannan kuma saboda faxinsa (SAW):

"ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔُ ﺣَﻖٌّ ﻭَﺍﺟِﺐٌ ﻋَﻠَﻰ ﻛُﻞِّ ﻣُﺴْﻠِﻢ ﻓِﻲ ﺟَﻤَﺎﻋَﺔٍ ﺇِﻻ ﺃَﺭْﺑَﻌَﺔً : ﻋَﺒْﺪٌ ﻣَﻤْﻠُﻮﻙٌ، ﺃَﻭِ ﺍﻣْﺮَﺃَﺓٌ، ﺃَﻭْ ﺻَﺒِﻲٌّ، ﺃَﻭْ ﻣَﺮِﻳﺾٌ "‏( [5]‏) .

Ma'ana: ("Juma'a" haqqi ne na wajibi
akan kowani musulmi, ya yi ta a cikin
jama'a, sai mutum hudu: Bawa da ake
mulkarsa, ko mace, ko yaro, ko maras
lafiya).

Matafiyi kuma juma'a bata zama wajibi
akansa saboda Annabi (SAW) bai
kasance yana sallatarta ba a halin
tafiye-tafiyensa ba, kuma yinin
ARAFAH –a zamaninsa- ya dace da
ranar JUMA'A, amma tare da haka sai
ya sallaci AZAHAR, ya kuma hada ta da
LA'ASAR.

Amma matafiyin da ya sauka a garin da ake tsayar da juma'a to mafificin lamari akansa shine ya sallace ta tare da 'yan'uwansa musulmai.

Kuma idan da bawa ko mace ko yaro ko maras lafiya ko matafiyi suka halarci sallar juma'a to sallarsu ta inganta, kuma ta isar musu; ba sai sun yi sallar azahar ba.

Na UKKU: Lokacin sallar juma'a:
Lokacin yinta shine lokacin yin sallar
azahar; daga bayan rana ta yi "zawali"
zuwa inuwar kowani abu ta zama kamar tsawonsa; wannan kuma saboda hadisin Anas dan Malik (RA) lallai Annabi (SAW) ya kasance yana yin sallar juma'a a lokacin da rana take
karkacewa([6] ).

Wannan kuma shine abinda aka rawaito daga sahabban Annabi (SAW) daga aikinsu ([7] ). Don haka; duk wanda ya riski raka'a daya kafin lokacinta ya fita to haqiqa ya riski
juma'a, in kuma ba haka ba sai ya
sallaci azahar; saboda fadinsa (SAW):

" ﻣَﻦْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺭَﻛْﻌَﺔً ﻣﻦ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻓَﻘَﺪْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺍﻟﺼَّﻼﺓ " ‏( [8]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda ya riski raka'a
Daya daga sallah to haqiqa ya riski
wannan sallar).

NA HUDU: Menene ya haramta a ranar
juma'a? Haramun ne "mamu" ya yi
magana alhalin limami yana huduba ;
saboda faxinsa (SAW):

" ﻣَﻦْ ﺗَﻜَﻠَّﻢَ ﻳَﻮْﻡَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻭَﺍﻹِﻣَﺎﻡُ ﻳَﺨْﻄُﺐُ ﻓَﻬُﻮَ ﻛَﺎﻟْﺤِﻤَﺎﺭِ ﻳَﺤْﻤِﻞُ
ﺃَﺳْﻔَﺎﺭًﺍ"‏( [9]‏) .

Ma'ana: (Duk wadda ya yi magana a
ranar juma'a alhalin limami yana
huduba to kamar jaki ne da ke dauke da
laftun littatafa). Da kuma saboda
fadinsa (SAW):

" ﺇِﺫَﺍ ﻗُﻠْﺖَ ﻟِﺼَﺎﺣِﺒِﻚَ : ﺃَﻧْﺼِﺖْ، ﻭَﺍﻹِﻣَﺎﻡُ ﻳَﺨْﻄُﺐُ ﻓَﻘَﺪْ ﻟَﻐَﻮْﺕَ "‏( [10]‏) .

Ma'ana: (Idan kace wa sahibinka: Yi
shiru, alhalin limami yana huduba to
lallai ka yi wargi). ''Lagawu'' shine:
magana na barna yasashshe.

Kuma haramun ne mutum ya tsallake wuyan mutane a lokacin huduba ; wannan kuma saboda fadinsa (SAW) ga mutumin da ya ganshi yana qetare wuyan mutane

"ﺍﺟْﻠِﺲْ ﻓَﻘَﺪْ ﺁﺫَﻳْﺖ"‏( [11]‏) .

Ma'ana: (Ka zauna saboda ka cutar).
Lallai kuma cikin wannan aikin akwai
cutar da masu sallah, tare da shagaltar
dasu ko hana su sauraron huduba .

Amma shi kuma limami ba laifi ya
tsallake wuyan mamu idan ba zai iya
zuwa wajen minbari ba har sai ya
aikata hakan. Kuma ''makruhi'' ne a raba tsakanin mutum biyu; wannan kuma saboda fadinsa (SAW)

" ﻣَﻦِ ﺍﻏْﺘَﺴَﻞَ ﻳَﻮْﻡَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ... ﺛُﻢَّ ﺭَﺍﺡ ﻓَﻠَﻢْ ﻳُﻔَﺮِّﻕْ ﺑَﻴْﻦَ ﺍﺛْﻨَﻴْﻦِ ﻓَﺼَﻠَّﻰ ﻣَﺎ ﻛُﺘﺐَ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻟَﻪ ... ﻏُﻔِﺮَ ﻟَﻪُ ﻣَﺎ ﺑَﻴْﻨَﻪُ ﻭَﺑَﻴْﻦَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ
ﺍﻷُﺧْﺮَﻯ "‏( [12]‏) .

Ma'ana: (Wanda ya yi wanka a ranar juma'a,… sa'annan ya tafi sallah, bai
rabe tsakanin mutane biyu ba, ya kuma
sallaci abinda aka qaddara masa… an
gafarta masa abinda ke tsakaninsa da
juma'a ta daban –ta gaba-).

NA BIYAR: Da me ake riskar sallar juma'a? Ana riskar sallar juma'a ne da
riskar raka'a guda daya tare da limami;
saboda ya zo daga Abu-hurairah (RA),
daga annabi (SAW) yace:

" ﻣَﻦْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﻣِﻦَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﺭَﻛْﻌَﺔً ﻓَﻘَﺪْ ﺃَﺩْﺭَﻙَ ﺍﻟﺼَّﻼﺓ"‏( [13]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda ya riski raka'a
guda daga juma'a to haqiqa ya riski
wannan sallar).

Amma idan ya riski abinda ke qasa da raka'a to a nan sai ya sallaci azahar.

NA SHIDDA: Shin juma'a tana da wata
nafila? Juma'a bata da wata sunna ta
nafila da ake sallatarta a gabaninta, sai
dai wanda ya sallaci gamammiyar
nafila gabanin shigan lokacinta babu
laifi ga hakan; saboda kwadaitarwan
annabi (SAW) kan hakan, kamar yadda
ya zo a cikin hadisin Salman (RA) da
ambatonsa ya gabata anan kusa da ke
cewa: (Wanda yayi wanka a ranar
juma'a, … sa'annan ya tafi sallar
juma'a, bai rabe tsakanin mutane biyu
ba, ya kuma sallaci abinda aka qaddara
masa). Da kuma saboda sahabbai (RA)
sun aikata hakan, Sannan kuma ''sallar
nafila'' tana da girman falala.

Sai dai kuma ba za a yi "inkari" ga
mutum ba idan har bai yi sallar nafila
gabanin sallar juma'a ba; wannan
kuma saboda ''sunna ratiba'' ta kan
kasance ne, bayan yin sallar juma'a;
raka'oi biyu, ko hudu, ko shida; saboda
annabi (SAW) ya aikata hakan, kuma ya
yi umurni da cewa a aikata shi; Ya zo
cewa:

"ﻛَﺎﻥ ﻳُﺼَﻠِﻲ ﺑَﻌْﺪَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﺭَﻛْﻌَﺘَﻴْﻦِ "‏( [14]‏) .

Ma'ana: (Annabi ya kasance yana
sallatar raka'oi biyu bayan ya yi
juma'a), An samu kuma cewa annabi
(SAW) yace:

" ﺇِﺫَﺍ ﺻَﻠَّﻰ ﺃَﺣَﺪُﻛُﻢُ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔَ ﻓَﻠْﻴُﺼَﻞِّ ﺑَﻌْﺪَﻫَﺎ ﺃَﺭْﺑَﻊَ ﺭَﻛَﻌَﺎﺕٍ "‏( [15]‏) .

Ma'ana: (Idan dayanku ya sallaci juma'a to ya sallaci raka'oi hudu a bayanta), a wata riwayah kuma:

" ﻣَﻦْ ﻛَﺎﻥَ ﻣِﻨْﻜُﻢْ ﻣُﺼَﻠِّﻴًﺎ ﺑَﻌْﺪَ ﺍﻟْﺠُﻤُﻌَﺔِ ﻓَﻠْﻴُﺼَﻞِّ ﺃَﺭْﺑَﻌًﺎ"‏( [16]‏) .

Ma'ana: (Duk wanda zai yi sallah daga
cikinku bayan juma'a to ya sallaci
raka'oi hudu).

Amma dangane da raka'oi shida kuma:

To saboda ya zo daga Abdullahi dan
Umar (RA) cewa lallai shi idan ya
kasance a garin Makka sai ya sallaci
sallar juma'a, to ya kan zakuda gaba sai ya sallaci raka'oi biyu, Sannan ya qara zakudawa gaba ya sallaci raka'oi hudu, idan kuma a garin Madina ya sallaci juma'ar; to sai ya koma gidansa ya sallaci raka'oi guda biyu bayanta, ba
zai yi sallah a masallaci ba, sai aka
masa magana, sai ya ce:

"ﻛَﺎﻥَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠﻪِ r ﻳَﻔْﻌﻞُ ﺫَﻟِﻚ"‏( [17]‏) .

Ma'ana: (Manzon Allah –SAW- ya
kasance yana aikata haka). Daga abinda ya gabata sai ya bayyana cewa: lallai mafi qarancin ''sunna ratiba ta bayan juma'a'' shine: raka'oi biyu, mafi yawanta kuma shine: shida. Wassu malamai kuma suna ganin cewa: in za a yi ''sunna ratiba'' ranar juma'a a masallaci to sai a sallace ta raka'oi hudu, in kuma a gida za a sallace ta sai a yi raka'oi biyu ([18] ).

Da wannan sai ya zama ana sallatanta akan halaye daban-daban.

NA BAKWAI: Ta yaya ake yin sallar juma'a? Sallar juma'a raka'oi ne guda
biyu, ana bayyana karatu a cikinsu;
saboda Annabi (SAW) ya kasance yana
aikata haka, aikinsa kuma wani yanki
ne na sunnarsa, kuma malamai sun yi
"ijma'i" akan haka. Kuma sunna ne
limami ya karanta ''suratu aljumu'at" a
raka'ar farko bayan ya karanta ''fatihah'', a ta biyun kuma ''suratu
almunafiqun ([19] )'', ko kuma ya karanta ''suratu al'aalah'' a raka'ar farko, a raka'a ta biyun kuma ''suratu
algashiyah ([20] )''; saboda annabi (SAW) ya aikata haka.

Wannan shine abinda ya sauwaqa na
bayanai akan sallar juma'a, da wassu
daga cikin hukunce-hukuncenta, da
fatan Allah ya fahimtar da mu addininsa, amin!

([1]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1371, 3/89), kuma Albaniy ya inganta
shi (Sahihu aljami'i, lamba:  3521).

([2]) Muslim ya rawaito su (lamba:
865).

([3]) Sharhin Annawawiy ga sahihu
Muslim (6/152).

([4]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1054), Albaniy ya inganta shi (Irwa'u
algalil, lamba: 592).

([5]) Abu-dawud ya rawaito shi (lamba:
1054), Albaniy ya inganta shi (Irwa'u
algalil, lamba: 592).

([6]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
904).

([7]) Ka yi dubi cikin littafin (Fat'hu
albariy, 2/450).

([8]) Abu-dawud ya rawaito shi, (lamba:
875), da Ibnu-majah (lamba: 468), kuma Albaniy ya inganta shi a cikin
(Irwa'u algalil, lamba: 496).

([9]) Ahmad ya rawaito shi (10230),
Alhafiz Ibnu-hajar a cikin Bulugu almaram yace: ''isnadinsa bashi da
laifi'' (Subulu assalam, 2/101-102,
hadisi mai lamba: 421).

([10]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
394), da Muslim (lamba: 851), ka duba
littafin (Irwa'ul galil, 3/84).

([11]) Abu-dawud ya rawaito shi
(lamba: 1118), da An-nasa'iy (3/103),
da Alhakim (1/288) kuma ya inganta
shi, Azzahabiy ya masa muwafaqa ,
kuma Albaniy ya inganta shi (Sahihu
Ibni-majah, lamba: 910).

([12]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
910). ([13]) Ibnu-majah ya rawaito shi
(lamba: 1121), kuma Albaniy ya
inganta shi (Sahihu Ibni-majah, lamba: 927, 928).

([14]) Bukhariy ya rawaito shi (lamba:
937), da Muslim (lamba: 882).

([15]) Muslim ya rawaito shi (lamba:
881). ([16]) Muslim ya rawaito shi (lamba: 881).

([17]) Abu-dawud ya rawaito shi
(lamba: 1130).

([18]) Duba littafin (zadu alma'ad,
1/440).

([19]) Muslim ya rawaito shi (lamba:
877).

([20])Muslim ya rawaito shi (lamba:
878).

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Fri 09-12-2016

Thursday, 8 December 2016

MATSAFI YA FADA HANNUN 'YAR MADIGO

MATSAFI YA FA'DA HANNUN 'YAR MADIGO
********
Na hadu da wani daga Cikin Abokanai da na dau kusan Shekara 3 zuwa 4 bamu hadu ba, Sai dai a waya ko kuma A kafar sadarwa ta Facebook.

Ya bani Wani Labari da ya Girgizani tare da tunanin Anya kuwa irin wannan labari zan barshi a dunkule ba tare da na 'dan fincina wa mutane na shi ba. Ko ba komai wasu zasu fadaku tare da sanya Ido ga 'ya'yansu da Qannensu da matansu.

Shi Wannan abokin nawa yana da wani aboki wanda kusan baya jin shawararsu duk yanda suka bashi shawara (kuma zama dashi ya zamar musu dole ne.

Ablinda ke faruwa shine wannan abokin nasu ya kasance yana son wata kyakykyawar yarinya Qin wanda ya rasa Son wanda ya samu.

Yayi juyin duniyar nan akan ta so shi amma kuma ba ta ko sauraren shi balle har ya samu ta amince masa (ta yarda da soyayyarsa).

Kwatsam sai Zuciyarsa ta bashi shawara akan cewa, ai yaje ya kai ta wajen Wani wanda duk mai hankali ba zai so a kirashi da malami ba. Saboda yana amfani da malantaka ne yana bokanci.

Ya je ya sami bokan ya gaya masa shakkuwarsa. Nan take wannan bokan Sai ya je yayi tsibbace-tsibbacensa tare da kulle-kullensa da siddabaru akan yarinya ta so wannan yaron.

Ai kuwa cikin kan kanen lokaci sai wannan yarinya ta fada tarkon Aljannun da wannan yaron ya sa aka turo mata domin su rika nuna mata shi a matsayin masoyi.

Kwana tashi Sai ya zamo wannan yarinyar duk duniya bata ganin kowa face, wannan yaron. Shi kuma sai ya fara Jin dadi akan aikin boka yayi kyau.

To meya faru? Kwatsam sai Wata babbar macce ta kirayi wannan abokin nawa mai bani labari tare da gargadarsa akan ya yi maza ya umurci abokinsa ya rabu da wannan yarinyar saboda kayan su ne. Ina fatan wannan hausar ta fito da kyau.

Ma'ana Budurwarsu ce da suke yin madigo da ita (wa'iyazu billahi). Ya amince akan zai bashi shawara akan ya rabu da ita. Haka kuwa akayi ya kira abokinsu ya bashi shawara amma yaqi ji.

Bayan da wannan labari ya zowa saurayin sai kawai ya fara tunani a zuciyarsa cewa, dama wance tana madigo? Ai nan take ya shiga bincike akan ya gano gaskiya.

Ai kuwa sai ya gano Cewa, ashe tana Madigo kuma tafi kusan Shekara biyar tana wannan muguwar 'dabi'a (kenan wannan shibe dalilin da yasa taki amincewa da soyayyarsa tun farko, Sai da yaje wajen boka).

Nan ya fara nadama marar amfani. Eh nadama marar amfani kuwa saobda a duniya ya tsani yar madigo ko 'dan luwadi. Amma kash yau gashi ammasa Baiko da 'yar madigo.

Nan yaje wajen Bokansa akan a raba wannan magani da akayi domin ta soshi. Ai kuwa boka ya aiwatar da abinda ya umurce shi da yi (ya raba wannan magani).

Nan take taji bata sonsa kuma gashi an musu baiko. To meya faru ashe Ita ma tana da nata boka sai taje ta koka masa matsalarta.

Wannan boka yayi na shi tsafi ya gano cewa, tun daga farko magani yaron yayi mata. Ai kuwa da aka gaya mata sai tace ita ma ayi masa magani yaji duk duniya kowa baya so sai ita.

Nan take Wannan bokan ya aiwatar shi kuma wannan yaro sai gashi ya fada tarkon so da kaunar yarinyar baji ba gani.

Ganin irin yanda yake binta take wulaqantashi (kuma aurensu ya kusa), shi ya sanya wannan abokina mai bani labari ya shirya zama da yarinyar don yaji meye matsalar take yiwa abokinsa wulaqanci.

Ai kuwa sai ta fafe masa biri har wutsiya tare da gaya masa cewa, babu shakka ita 'yar madigo ce. Kuma ta lalata yara babu adadi kuma zata ci gaba da lalatawa.

Kuma auren abokinsa babu mahani domin tunda yayi mata magani ita kuma sai ta gwada masa ko wacece. Domin sai ta aure shi kuma bayan auren sai ta mayar da gidansa Kasuwa ta Safarar mata domin yin madigo (Wa'iyazubillahi).

Yanzu dai kam An kusa Aure.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Thus08-12-2016

Wednesday, 7 December 2016

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

WASU DAGA CIKIN MUHIMMAN KALAMAI DA AKA GABATAR A TARON ZAMAN LAFIYA (PEACE AND UNITY CONFERECE) A ABUJA

"Musulunchi ba Yana Nufin Ka dauki Wuka ko Adda ba kayi kabbara ka kashe wani. A'a musulunchi na nufin zaman lafiya da kyakykyawar mu'amula."___ Cewar, Sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar III.

"Ga Wani gwaji da yakamata muyi domin samun Kyakkyawar dangantaka da mu'amula."

"Mazaje Ku taimaki matayenku a aikace-aikacen gida, Sannan Idan zakuci abinci (misali da dare) ku dauka da hannunku ku ciyar dasu. Idan ka ciyar da ita to ita ma ta sanya hannunta ta ciyar da kai."___Cewa, Mufti Menk.

"Rayuwarka Kamar Photo Ce, Shi kuma Musulunchi Kamar Gidan sanya photo ne. Idan har kai musulmin kirkine, to ka dauko gidan photon nan ka sanya shi ciki. Kayi amfani da ilmin da kaji. Ka tafiyar da maganganu a aikace musulunchi ya zamo a cikin kirjinka. Kayi maganar gaskiya kada ka karkatarda magana. Kuma kada kayi da'awar abinda baka da shi sannan ka aiwatar da musulunchi a dukkanin rayuwarka."

"Babu wata kasa ko Al'umma da zasu ci gaba makawar basu bi dokokin Allah ba Sannan basu girmama Shuwagabanninsu ba, kuma basu bi koyarwar malamansu ba. Ka mu'amulancin malamai tsawon kwanakki bakwai dake cikin sati. Ka roki Allah tsayuwa akan Ibada ba saudaya ba domin ita ke bunkasa kasa" ___ Cewar, Sheik Assim Al-Hakeem.

"Allah yana Son Masu son Junansu ba don komai ba sai domin Allah. Makasudin samun nasara a wannan rayuwa shine dukkannin mu mu zama abu guda saboda Allah"

"Kada mu bari Zuciyoyinmu su jamu zuwaga ganin kyashin juna ko kuma Yawaita ganin laifin juna idan muka hadu wuri daya hakika zamu kai ga dacewa. Mu rika yiwa junanmu godiya. Sannan mu so makwaftan mu kamar yadda muke son kawunan mu. Hakika murmushi abincin ruhine mu zama masu gaskiya game da rubutun mu. Ina rokon Allah ya taimake mu duka. Mu rika rokon hadin kai ba rarrabara kawuna ba."__ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Nawane ake Sayarda Manyan Gidaje a Abuja da Lagos? Hakika farashin da zaka biya ka shiga Aljanna Shine, ka yafewa dan uwanka duk laifin da yayi maka. Hakika hakkine akan kowanen mu akan ya yada zaman lafiya kuma umurnine akan mu rika yafewa juna. Ya ku mutane! Ku yada zaman lafiya tsakanin ku. Sannan ku ciyarda matalauta da masu jin yunwa. Ku sowa dan Uwanka/'yar uwarka abinda kake sowa kanka. Hakika ba zaka zama mai Imani ba har sai ka sowa dan uwanka abinda kake sowa kanka. Allah yana son masu gaskiya."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Idan har da gaske kana Son Manzon Allah (SAW) to kabi Allah sannan ka zama mai yafiya ka zama mai son Juna, Ka ajiye duk wani rudani gefe kada ka nuna kafi kowa iyawa domin yana kai mutum zuwa ga dolanci. Ka zama mai taka tsan-tsan ga lamurranka kada ka bari zuciyarka ta rufe ga gaskiya. Musulunchi ba addini ne kawai ba, A'a musulunchi hanyar Rayuwa ce. Nemi ilmin gaskiya. Allah ya Albarkacemu da kyakkyawar fahimta ka tsare mu da Ilmi mai yawa saboda ilmi mai yawa Wani lokaci cuta ne."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kayi hankali da yawan ganin laifin mutane da yawan ganin Laifin Shuwagabanni. Ka yarda da kanka ka gyara halayenka wannan shi zai cenja gidajenmu, da 'yan uwanmu da Al'ummar mu dama Duniya gaba ki daya ka yarda da kanka ka kauracewa miyagun halaye ka tuna cewa Adanannar dukiyarka na Aljanna. Ka yarda da Allah kada ka taba debe tsammani kayi kaffa kaffa kada ka taba debe tsammani daga rahamar Allah. Allah Yace; "KA GAYAWA BAYINA WAYANDA SUKA CUCI KAWUNANSU KADA SU TABA DEBE TSAMMANI DAGA RAHAMAR ALLAH"..Ya Allah ka hada mu a lambun Aljanna."____ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Kada ka shagaltu da ilmin da ka samu na Wannan taro (na wa'azi) na kwana biyu kace ya isheka kawai. Kayi godiya ga malaman kasarku da suka dade suna karantarda ku tare da tarbiyantar da ku."___ Cewar, Sheik Muiz Bukhari

"Allah ya kara mana Imani. Hakika addinin Musulunchi addini ne na Zaman lafiya ba na rikici ko tashin Hankali ba. Mu tashi tsaye kada mu sanya gajiyawa. Mu zama masu Alfahari ba masu girman kai ba."____Cewar, Ustaz Abubakr Sadiq

Ni da na fassara Ina fatan Wayannan Gwala-gwalan Kalamai zasu samu wurin zama a cikin Zukatan mu.

Anyi Wannan Wa'azin ne a  dakin taro da ke Abuja a Ranar 3 da Ranar 4  ga watan 12. 2016.

Fassarawa, Jamilu Sani Rarah Sakwkwato.

Monday, 5 December 2016

MEYE LAIFIN SHUGABAN KASA BUHARI GA SADAKIN ZARAH?

MEYE LAIFIN SHUGABA BUHARI A CIKIN SADAKIN ZARAH?
*******
Tunkusan Lokacin da Akayi Sadakin Zarah 'yar Gidan Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na ke samun Sak'onni akan ba'aji nayi sharhi ba game da wannan Sadakin.

Alhamduli Lahi bayan 'yan Uzurukka da suka sha gabada Sai yau Allah ya kaddare ni da Cewa wani abu game da wannan Sadaki.

Har yau har gobe Ina Kara kira ga 'yan Arewar mu akan Don Allah su daina Sanya Kansu cikin Kwano ko k'ok'o suna tunani su rika bude kawunansu suna tunani.

Da farko ina son mutane su san Wanene Ahmad Indimi sannan suyi tunani mai kyau game da shi Kafin Su rika yanke Hukunci game da duk wannan Sadaki na shi.

Kafin Nayi bayani akan Ahmad Indimi bari na fara bayani akan Jahar Borno (In da Cen ne Garin Su Ahmad da Mahaifansa).

Wani daga cikin Masu son jin ra'ayina game da wannan Sadakin ya min tambaya game da wannan sadaki na Zarah Buhari.

Amma mai makon In bashi amsa sai na kyale shi Na kira wata baiwar Allah Wacce 'yar asalin maiduguri ce.

Bayan na kira ta dauka sai na saka Speaker domin yaji me zamu tattauna ana akai. Bayan mun gaisa sai na tambayeta Cewa, "Shin har yanzu A maiduguri Miliyan daya ake Sadaki?"

Sai tayi dariya tace dani, "Humm yanzu wannan Recession da ake ciki wa zaiyi wani sadaki milion 1"

Sai nace, "To nawa ake yin Sadaki Maiduguri a yanzu?" Sai tace dani, "Dubu d'ari bakwai, d'ari biyar Ida kuma mutum bai da shi sosai Cikin Anyi hankuri an matse sai ya biya Naira dubu dari biyu da hamsin ko kuma dubu d'ari da Ashirin."

Bayan mun gama magana mukayi Sallama na kashe waya ta. Tare da tambayar wannan mai tambaya ta ko kaji wayar da nayi? Sai yace da Ni "Eh yaji ashe haka maiduguri suke."

Sai nace dashi to Wanda yayi wa Zarah Buhari Sadaki 'dan Maiduguri ne, kuma a maidugurin ma su ne manyan masu kuddi.

Baban Ahmad Wato Muhammad Indimi Surukine ga Tsohon Shugaban Kasa Ibrahim Badamasi Babangida IBB.

Sannan Muhammad Indinmi Shike da kamfanin nan na Oriental Energy Resources Limited, kamfanin da ke da rijiyoyin mai har guda uku da suka hada da: OML 115 da ta Oldwok da kuma ta Ebok.

Sannan Shi Ahmad Indimi yana daga Cikin Manyan Daretoci na Kamfanin domin Shine daracta na Ukku a kamfanin.

Sannan Ahmad Indimi din da kake ji yana daga Cikin Matasan Samari da ke da taimako domin IDPs INTERNAL DISPLACE PERSONS (Wato mutanen da rikici yasa suka bar mazauninsu) ya taimakesu kusan da Naira Miliyan d'ari biyu har da wani abu.

Sannan Idan ka koma B'angaren Ita kanta Zarah Duk kusan Cikin 'ya'yan Manyan Kasarnan Kaf (ban cire ma kowa ba daga cikinsu), ta fisu taimako tare da Neman Dukiya. Domin har Ophanage (gidan marayu) take da shi.

To mene A Ciki don Shi Wannan matashin Mai kuddi ya bi Al'adar Garinsu ta yin Sadaki da Tsada? Tun da dai ba'a kaiyade kuddin Sadakin ba a musulunce.

A musulunce Kuddin Sadakin Bana yanda malamai suka yi kiyasi shine naira 8400, Shin don Allah akwai wanda yaga In da akayi Sadaki 10,000 a bana? In kuwa babu inda akayi to me yasa don shi yayi al'adar garinsu (na yin sadaki da tsada) abu zai zama abin Ganin Laifi.

Ni banga laifin Wannan Ba Gaskiya sai dai abinda muke cewa da Su Wayannan Samarin Sunyi kwaikwayo da Sunnar Manzon Allah (Saww) na Takaita Sadaki da Sun kyauta. Domin Manzon Allah (saww) yake cewa, Aure Mafi albarka shine wanda sadakinsa ya zamo mafi sauki".Kuma da Sun bar tarihi a kasarnan.

Da kuma sun kwaikwayi auren Nana Fatima da Sayyidina Aliyu da Sun burge duk wani ma'abocin Sunnah.

Lokacin da Sayyidina Aliyu (Rta) ya nemi Auren Nana Fatima (rta) bayan Annabi (Saww) ya tambayeta kuma ta amince sai Manzon Allah (Saww) ya cewa Sayyidina Aliyu (RA): "Ya Aliyu, shin kana da wani abu da zan daura maka aure da shi (sadaki)?".

Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya ce: "Sai takobina da garkuwata, sai kuma rakumina na ban ruwa ", (a wata ruwayar an ce doki ne maimakon rakumin)

Sai Manzon Allah (Saww) ya ce: "Amma takobinka kana da bukatarsa, za ka yi yaki da shi a tafarkin Allah kuma ka kashe makiya Allah da shi.

Rakuminka kuma kana shayar da (gonar) dabinonka da shi, haka kana daukar kaya da shi, kuma yana daukarka a tafiye-tafiyenka.

Don haka je ka yi yadda za ka yi da
garkuwarka". Sai Sayyidina Aliyu (RA) ya je ya sayarwa Sayyidina Usman bin Affan (RA) da garkuwarsa a kan farashin dirhami 480, sai ya kawo wa Manzon Allah (saww).

Daga nan Manzon Allah (Saww) ya sanar da Musulmi zancen auren.

Haka kuma na So ace Zarah Buhari ta kwaikwayi Ummu Sulman An Ruwaito Cewa Sahabbai (RA) suna
Cewa, "FIYAYYEN AURE SHINE AUREN UMMU SULMAN (RA), DOMIN ITA SADAKINTA MUSULUNCI NE."

Ummu Sulman Itace Mahaifiyar Anas Bin Malik (Hadimin Manzon Allah (Saww)), lokacin da mahaifinsa ya rasu, taqi yin aure har Saida Abu Talha ya fito yana Sonta sannan ta amince zata aure shi amma da sharadi zaya Musulunta (Musuluntarsa Shine Sadakinta).

Bayan manyan attajirai da Masu mulki da Sadaukai sunyi ta fito mata amma taki amincewa dasu. To da ace Zarah Buhari ta Bukaci kada sadakinta Yayi tsada haka to babu shakka da ta kyauta.

Kuma ba zanga Laifinta ba ko na wanda zata aura ko mahaifanta don anyi mata sadaki naira miliyan 44, sai dai muna cewa a kamanta Sunnah ga dukkanin Abubuwa yafi.

Subhanallah...!

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Mon 5/12/2016