Wednesday, 1 July 2026

Umar Ajiya Hope 4 NextGen Congratulates Alh. Umar Ajiya Isaa on Well-Deserved Honorary Doctorate Degree from Sokoto State University

Umar Ajiya Hope 4 NextGen Congratulates Alh. Umar Ajiya Isaa on Well-Deserved Honorary Doctorate Degree from Sokoto State University



SOKOTO, NIGERIA — The management and entire team of Umar Ajiya Hope 4 NextGen proudly extend their warmest and most heartfelt congratulations to Alh. Umar Ajiya Isaa on the prestigious conferment of an Honorary Doctorate Degree by the Senate and Management of Sokoto State University.

This highly distinguished honor is a fitting recognition of his outstanding, impactful, and lifelong contributions to community development, humanitarian service, and sustainable youth empowerment within Sokoto State and across the nation.

Through his unwavering philanthropy and vision, Alh. Umar Ajiya Isaa has consistently demonstrated what it means to be a true pillar of support for the vulnerable and an exceptional mentor to the younger generation. His deep-seated commitment to uplifting others has created sustainable pathways for youth growth, making him an enduring role model whose legacy will inspire generations to come.

Speaking on the conferment, a representative from Umar Ajiya Hope 4 NextGen stated:


This honorary doctorate degree is not just an award; it is a celebration of a lifetime dedicated to public good. Alh. Umar Ajiya Isaa’s selflessness in piloting community-driven projects and championing the cause of the next generation aligns perfectly with our core mission. We are immensely proud to be associated with his stellar leadership and vision."


As he formally steps into this new chapter as an Honored Doctor, Umar Ajiya Hope 4 NextGen prays for continued wisdom, robust health, and divine guidance for Dr. Alh. Umar Ajiya Isaa as he continues his noble service to humanity.

Congratulations, Sir!

Signed:

Management,

Umar Ajiya Hope 4 NextGen

Sunday, 2 November 2025

Silence Is No Longer an Option: A Call for Peace and Understanding in Nigeria By, Jamilu Sani Rarah Sokoto

 


I would normally not do this, however, silence is no longer an option.

The world woke up to a tweet from a global leader about 🇳🇬 Nigeria and as a Nigerian who is deeply passionate about peace in our world, especially in my home country, remaining silent would mean consent to a message that does not represent our reality.

As someone from Northern Nigeria  living in the North and a Muslim  I understand the pain and complexity that many cannot express in ways the world easily understands. Countless people suffer and die quietly, victims of insurgency, poverty, and neglect.

For over a decade, I have been involved in humanitarian and relief work across Northern Nigeria. In that time, I’ve seen unimaginable suffering  families displaced, communities destroyed, children orphaned  and I’ve faced personal threats from those who falsely claim to represent the same faith I hold dear.

Yet, I remain steadfast in my commitment to serve humanity, rebuild hope, and tell the true story of what is happening.

The heartbreaking truth is that the majority of those affected by the insurgency are Muslims. But whether Muslim or Christian, we must remember: the right to life is sacred — no one has the right to take what they cannot give.

Beyond our borders, the world has witnessed the devastating consequences of so-called “liberations” and foreign interventions. History teaches us that such actions rarely bring peace  they bring deeper chaos.

Nigeria, the most populous Black nation on earth, has produced some of the world’s finest leaders, thinkers, and peacemakers. Calls for war or external interference must be firmly rejected. What we need is healing, unity, and understanding not destruction.

As the Bible reminds us:

“Blessed are the peacemakers, for they shall be called the children of God.” —Matthew 5:9

Let us choose peace over provocation, compassion over division, and truth over propaganda. Nigeria’s story is not one of war  it is one of resilience, faith, and hope for a better tomorrow.

Jamilu Sani Rarah

Sokoto-Nigeria


Wednesday, 29 October 2025

DANFODIO WEEK 2025: CELEBRATING THE LEGACY OF KNOWLEDGE AND JUSTICE



Introduction

The much-anticipated Danfodio Week 2025 is currently ongoing across Sokoto and several other cities in Northern Nigeria. The annual event brings together scholars, students, traditional rulers, and the general public to celebrate the timeless legacy of Shehu Usman É—an Fodio, the great Islamic reformer, scholar, and founder of the Sokoto Caliphate.

Theme of the Celebration

This year’s theme, “Reviving the Spirit of Knowledge, Justice and Leadership in the Legacy of Shehu Usman É—an Fodio,” focuses on reawakening the values that guided the Shehu and his companions in building one of the most influential Islamic civilizations in Africa.


Ongoing Activities

Throughout the week, various activities are taking place, including:

  • Public Lectures and Panel Discussions: Renowned scholars are delivering thought-provoking papers on the relevance of Shehu É—an Fodio’s teachings in modern governance, education, and social justice.

  • Qur’anic and Essay Competitions: Students from different institutions are participating in contests designed to promote scholarship and creativity inspired by the Shehu’s ideals.

  • Cultural and Art Exhibitions: Traditional poets, calligraphers, and historians are showcasing works that reflect the rich heritage of the Sokoto Caliphate.

  • Community Outreach and Special Prayers: The week also includes prayers for peace, national unity, and the continued progress of the Muslim Ummah.






Public Participation

The events have continued to attract large audiences including traditional leaders, government officials, scholars, youth groups, and media representatives. The atmosphere across venues is filled with inspiration, cultural pride, and deep spiritual reflection.

Conclusion

As Danfodio Week 2025 continues, participants are reminded of the Shehu’s enduring message: that knowledge, truth, and justice remain the pillars of a strong and peaceful society. The celebrations not only honour his remarkable life but also encourage a new generation to follow his path of wisdom and righteousness.

By,

 Jamilu Sani Rarah Sokoto

New Media Assistant to Sultan

Tuesday, 12 November 2019

MAGANAR MAULUDI ABUNE MAI SAUKI

Dukkan dangin Yabo da godiya da kirari su kara tabbata ga Allah (Swt), Salati da Sallama su kara zuwa ga Shugaban Annabawa Fiyayyen dukkan Halittu Muhammad 'dan Abdullahi (Saww).

Bayan haka Wannan rubutu zai haska ma akan Halaccin yin Mauludi ko kuma haramcin Yinsa a mahanga ta addini.

Farko hakika a cikin Qur'ani mai girma babu wuri daya In da Allah (Swt) yayi umurni da ayi Mauludi

Annabi (Saww) da kansa baiyi Mauludi ba kuma bai Umurci wani daga cikin Sahabbansa Suyi Mauludi ba.

Sai dai ma Annabi (Saww) ya Umurci Sahabbansa da kada su yi koyi da Nasara Domin Sune ke yin Biki domin Annabi Isa (Alaihis Salam).

Yace, "Kada ku rike ni kamar Yadda Nasara suka riki d'an Maryam. Ni bawa ne. Saboda haka kuce dani Bawan Allah kuma Manzon Allah (Saww)." (Buhari).

Ya tabbata Manzon Allah (Saww) ya kan dauki ranar haihuwarsa Ranar Ibada ba ranar Biki ba kamar yanda yazo a hadisi.

An Tambaye shi (Saww) game da Azumin Litanin da yake yi, sai yace, itace Ranar da aka haifeni kuma itace ranar da aka bijiromin da alkawali (Muslim, al-Nisaa’i da kuma Abu Dawood).

Baya ga haka mun san Cewa, Sahabbai (RA) sun fimu So da Kaunar Annabi (Saww).

Sayyidina Abubakar (RA) Wanda Yafi kowa kusanci ga Annabi (Saww) ba'a samu yayi Mauludi ba.

Ko An samo a littafan Tarihi Cewa, Sayyidina Umar (RA) yayi Mauludi ko Sayyidina Usman ko Aliyu (RA)?

Ko an samu daga Cikin 'ya'yan Annabi (Saww) Wani yayi Mauludi? Shin basu san da mauludin bane ko kuma Son Annabi (Saww) ne basayi?

Bayan Sahabbai Shin Imam Abu Haneefah, Maalik, Shaafi’i, Ahmad, al-Hasan al-Basri, Ibn Seereen an samu Waninsu yayi Mauludi?

An samo a hadisi Ingantacce daga Ma'aiki (Saww) Cewa, Annabi (Saww) yace, Mafifitan mutane daga cikin Al'ummata sune Karni Na Farko (Sahabbai Kenan), Sannan masu bi musu (tabi'ai Kenan), Sannan Masu bi musu (Tabi'ut tabi'una Kenan)" (Bukhari, Muslim Da Tirmiziy Suka Ruwaito).

Idan Zamuyi duba Kenan Wannan Karni Namu Yana Kasa Kwarai game da Samun fifiko kamar yadda Annabi (Saww) Ya Fada.

Shin Ba Akan soyayya bace ake yin mauludin ba? Shin munfi Sahabbai Soyayyar Annabi (Saww) NE? Domin kuwa daga Cikin Sahabbai akwai Wanda Manzon Allah (saww) ya kwanta barci akan cinyarsa lokacin da suke cikin wani Kogo.. Sai Shi wannan sahabin ya rika yagar rigarsa yana tottoshe ramukan da suke cikin kogon. Amma duk da haka akwai sauran wani rami wanda bai samu abin tosheshi ba.

Chan sai ga wani Maciji ya leko ta cikin wannan ramin yana so zai fito. Don haka sai ya sanya Qafarsa ya toshe ramin don kar Macijin nan ya fito ya chutar da Manzon Allah (saww). Macijin nan yayi ta cizonsa yana zuba masa dafi. Amma duk da haka bai motsa ba, don kar ya tashi Manzon Allah (saww) daga Bacci. Wannan Sahabi Shine Sayyidina Abubakar.

Shine Makusancin Manzon Allah (Saww) na Kusa da Kusa Kai akwai ma Lokacin da Manzon Allah (saww) yazo gidan Sayyiduna Abubakr (ra) yace masa “ALLAH YA UMURCENI INYI HIJIRA”.

Sai Sayyiduna Abubakar yace “Ina fatan tare dani zaka tafi?” Sai Ma’aiki yace masa “KWARAI KUWA. ALLAH YACE MIN IN TAFI TARE DAKAI”. Sai Sayyiduna Abubakar ya fashe da kuka don murna Ganin Allah ya zabe shi ya Raka Wanda Yafi so a Duniya Fiye da Komai.

Kai Hatta Annabi (Saww) An tambayeka Shi Duk Duniya Waka Fi so Yace, Aisha, Aka sake Tambayar say Cikin Maza fa? Yace, "Mahaifinta (Wato Abubakar)".

Amma Duk Irin Wannan Soyayyah dake Tsakanin Sayyidina Abubakar da Manzon Allah Bai sa Sayyidina Abubakar Yayi Mauludi Don tunawa Da Annabi (Saww) ba.

Bayan Sayyidina Abubakar (rt), Sayyidina Umar (ra) na daya daga cikin zaratan mayaka wadanda su kayi ruwa da tsaki wajen kare martabar Musulunci da ruguza abokan fadansa.

Ya kusanci Manzon Allah (Saww) har ya kai matsayin wazirinsa na biyu. Bayan tsabar Soyayyar da Sahabi Umar Ke yiwa Annabi haka Allah ya karrama shi da surukuta da Manzon Allah (Saww) inda Manzon Allah ya nemi auren 'yarsa Hafsah, aka ba shi ita, aka daura aure, sai ta zama ita ce ta uku. Bayan Sayyidina Abubakar Yayi wafati Sayyidina Umar NE Yayi khalifanci Amma Baiyi Mauludi ba Bai Kuma yi Umurni da ayi Mauludi ba.

Sayyidina Usmanu Bayan zamansa Sahabi a gun Annabi (Saww) Kuma surukine na Annbi (Saww) domin ya auri 'Ya'yan Manzon Allah har Guda biyu Amma ba'a Taba samunsa ba dayi Mauludi ba.

Haka Dan baffansa Sayyidina Aliyu tun Yana karaminsa Ya Yarda da abinda Annabi (Saww) Yazo dashi, domin tun Yana Dan Shekara Bakwai ko Tara ya karbi Musulunchi Kuma surukin Annabi (Saww), Wanda ya auri Daya daga Cikin 'ya'yan Annabi (Saww) (Kusan ma Wacce Annabi Yafi so a Cikin 'ya'yansa).

Sayyidina Aliyu Shine, Wanda ya yarda ya amince ya kwanta akan Shimfidar Ma’aiki (saww) acikin daren da Mushrikai suke nufin su kasheshi (Saww).

Sayyidina Aliyu ya yarda ya kwanta amadadinsa, duk da yasan cewa zasu iya harbinsa da kibiya ko su kasheshi tun kafin su gane cewa ba Ma’aikin bane awajen. (saww), Amma Duk da Irin wanna So Annabi Ya yo wafati ya barshi Duniya baiyi Mauludiba Bai Kuma yi Umurni da ayi mauludin ba.

Sayyidina Bilal Shine Ladanin Manzon Allah (Saww) bayan Ma'aiki (Saww) Ya bar Duniya Saboda Tsananin soyayyarsa ga Ma'aiki (Saww) Sayyidina Bilal dena kiran sallah yayi!!

Bilalu (rta) bai Qara yin kiran sallah ba Sai rannan Sayyiduna Umar (ra) yace masa yazo yayi (aranar da aka karbo Masallacin Qudus).

Da Bilalu ya fara kiran sallah, yazo daidai wajen “ASH-HADU ANNA MUHAMMADAR RASULULLAH!! Yana fada haka, sai ya fashe da kuka, Sahabbai ma kowa sai kuka.

An ce ba’a ta’ba ganin ranar da daruruwan Sahabbai sukayi kuka suka zubar da hawayesosai kamar wannan ranar ba.. Sai sukaji Tamkar awannan lokacin ne Ma’aiki ya bar duniya!! Amma Duk da Wannan Basuyi Mauludi ba.

Imamu Malik Saboda Soyayyarsa ga Ma'aiki (Saww), Baya Fadin hadisi a Hanya, Idan Ka tambayeshi hadisi a hanya sa Yake a dake Ka, Idan zai Bayyana hadisi sai Yayi wanka ya Sanya Turare Saboda Tsananin Soyayyarsa ga Fiyayyen Halitta (Saww).

Har an Ruwaito Cewa, Baya hawan Doki a Madina, Baya saka takalma a Madina Da aka tbayeshi dalili Yace, Saboda Baya it's takin Kasarda Annabi (Saww) Yake a Ciki, Amma Duk da Irin Wannan Soyayyah da Yake yiwa Annabi (Saww) ba'a Samu Yayi Mauludi ba.

Shin kana tunanin duk sun Manta NE da Ranar haihuwar Annabi (Saww)? Ko Kuma basa son shine? Ko Kuma Tunaninsu da fahimtarsu Bata Kai Cen ba?

'yan Uwana Masu Murnar Mauludi Kuyi Hakuri Dolene sai Mun Tunatarda kanmu abinda Yake daidai ko zamu Samu Rabo a Gobe Qiyama.

Muna Rokon Allah ya nuna Mana Gaskiya Kuma ya Bamu Ikon Binta, Ya Kuma Nuna Mana Karya Ya Kuma Bamu Ikon Kauce Mata.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tue 12-11-2019

Tuesday, 13 August 2019

KA TABA SALLAR GAWA?

Mutane da Yawa Sukanyi Sallar Janaiza (Sallar Gawa), Amma Kuma Basu San ya ake yin wannan Sallah ba (Ma'ana Basu San me ake fada a Sallar ba), ko Kuma Basu San hukunce hukuncen ta ba.

Da farko Ya Halatta Idan Liman yayi Niyar yin Sallar Gawa yayi Kabbara Hudu, Biyar, Shidda, Bakwai ko Kuma Tara, a Lokacin Sallar Gawa, Sannan ya sallame, domin duka An samu wannan dalilai daga Sahabban Annabi (Saww) Sunyi hakan.

Kabbara Hudu, Sayyidina Abu Huraira (RTA) Yace, " Lokacinda labarin rasuwar Najashi (Sarkin Habasha) ya zowa Annabi (Saww), A wannan Rana sai Annabi (Saww) Ya fita da mu a Wani wuri da ake yin sallah, mukayi sahu Annabi (Saww) yayi Mana Sallar Janaiza Yana Mai yin Kabbara hudu.
(Sahih Al-Bukhari, littafe na 2, shafi na 227, Hadith na 404; ko Kuma Sahih Muslim, littafe ba 2, shafi na 452, Hadith na 2077).
Kabbara Biyar, Abdurrahman Ibn Abi Laylah (RTA) yace, Zayd Dan Arqam ya kasance Yana Yana yin kabbarori Hudu Idan Dayan mu ya rasu, wata Rana sai ya yi raka'a Biyar sai muka tambayeshi Dalilin yin Haka, sai Yace, Ma'aikin Allah (tsira da amincin Allah Su tabbata a gareshi) ya kanyi Haka.[
(Sahih Muslim, littafe na. 2, shafina 453 Zuwa 454, Hadith na 2089).
Kabbara Shidda, Abdul Khayr Yace, Ali Ibn Abi Talib Ya kasance Yana yin Kabbarori Shidda (Idan Yana Bada Sallar Gawa), ga wayanda suka halarci yakin Badar, Kabbarori Biyar ga sauran Sahabban Annabi (Saww) da Basu halarci yakin ba, Sannan Yana yin Kabbarori Hudu ga gama GARIN Al'umma.
(Imamu Al-Bayhaqi da Ad-Daraqutni suka fitar dashi hadisi ne Mai kyau a duba a Cikin Ahkam al-Jana'iz, shafi na 113).
Kabbarori Bakwai, Musa Dan Abdullahi Dan Yazid yace, Sayyidina Aliyu ya yi Kabbarori guda Bakwai a lokacin da Yake sallatar gawar Qatadah, (Kuma Qatadah ya kasance daga Cikin wayanda suka halarci yakin Badar).
( Imamu Bayhaqi ya fitar dashi Kuma hadisi ne Mai kyau a duba a Cikin Ahkam al-Jana'iz, shafi na 113 Zuwa 4).
Kabbarori Tara, Abdullahi Ibn Az Zubar ya ruwaito Cewa, Annabi (Saww), ya sallaci gawar Sayyidina Hamza Yana mai yin Kabbarori guda Tara.
(At-Tahawi da kuma At-Tabarani suka fitarda shi hadisi ne Mai kyau a duba a cikin Ahkam al-Jana'iz, shafi na 114).
Ya Halatta Mutum ya daga hannayensa Biyu idan zaiyi Kabbara a kowace Kabbara ko Kuma Mutum ya daga hannayen a kabbarar farko kawai kowane Mutum yayi daidai ne.
(A duba a Sahih Al-Bukhari, littafe na 2, shafi na 228, 55).
Ana son Mutum ya karanta suratul fatiha da sauri a kabbarar farko.
(Sahih Bukhari, littafe na 2,  shafi na 236, Hadith na 419;  ko Kuma Sahih Al-Bukhari, littafe na 1, shafi na 397, Hadith na 710; Sahih Muslim, littafe na 1, shafi na 219, Hadith na 786).
A Kabbara ta Biyu Ana so ayi sauri ayiwa Annabi (Saww) Salati, duk salatin da Mutum yayi Amma salatin Ibrahimiyya Shine Wanda aka fiso a Yi domin shine salatin da ya zo a ingantattun hadisai.
A Kabbara ta ukku Ana so ne ayiwa Mamaci Addu'ar Samun Rahama, Tunda sallat anayinta ne ga Mamaci Ana so ayi Masa Addu'ah a Kabbara ta ukku, zuwa ta Hudu ko ta Biyar Zuwa Tara domin nema Masa rahamar Allah. (Abu Dawud, 2, shafi na 616-7, 2740).
Sallamewa, Akwai hanyoyi Biyu da Sunna ta amince A sallame Sallar kamar yadda Baihaqi da Tabaranj suka ruwaito a Cikin Ahkam al-Jana'iz, shafi ba 127, #83).
1. Ko dai Mutum yayi sallama daya kawai ta hanyar sallamewa a Bangaren Dama. Kamar yanda Hadisin Abu Huraira (RTA) ya nuna.
2. Ko Kuma Mutum ya sallame a duka bangarori Biyu (Dama da hagu) kamar yanda yazo a Hadisin Ibn Mas'ud.
Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tue 13-08-219

UNGUZOMA (MIDWIVES)

UNGOZOMA (MIDWIFE) BAIWAR ALLAH

Wasu suna ganin kalmar Ungozoma ta samo asali ne daga "ungo-tsoma ".Wai don Idan mace ta yanke cibin jariri, kuma mabiyya (mahaifa) ta fado, to sai a dauko ta fito da ita waje ta mika wa masu taimaka mata, ta ce da su "Ungo-tsoma " A cikin masaki mai cike da ruwa. Wai ta haka ne sabida yawan fadar kalmar "Ungo-tsoma ". Sai ta koma Ungotsoma. "Ungozoma ".

A Al'adar Hausawa Ungozoma ta na da muhimmanci kwarai da gaske, domin kuwa kusan kowanne Kauye ko Gari ko Unguwa Inda jama'a su ke zaune akwai Ungozoma, kamar dai yadda ake samun Ruwa don bukatar rayuwa.

Saboda sanin muhimmancin Ungozoma a al'umar Hausawa har kirari su ke mata da cewa " Ungozoma kin fi mai da son da ". Haka har cikin Karin magana an ambaci Ungozoma, misali : "Komai saurin Ungozoma ta jira a haihu ".da kuma "Ai ba a Kare haihuwa ba wai an baiwa Ungozoma tuwan suna a hannu". Dasauransu. wannan shi zai Kara tabbatarma da muhimmamchin Wannan Mata a Cikin al'umma.

Akwai ire-iren Ungozoma guda biyar. (5times) a kasar Hausa kamar haka :

1-Ungozomar Gado, Wasu Gidajen Attajirai Sukan Ajiye Ungozoma wacce duk matarda zata haihu Gidan itace zata Kula da wannan matar tun daga rainon Cikin har Zuwa Haihuwa Itace zata Rika Kula da matar.

2-Ungozomar Sana'a, Akan Samu Wasu Masu Aikin Karbar Nakuda (Ungozoma), wacce Ita Zaman Kuddi take, 'yan Unguwa sun San da zamanta, Duk Gidan da za'a haihu akan Kira Irin wannan matar a sanyata ta karbi bikin Idan an haihu sai a biyata ladan aikinta.

3-Ungozomar Dangi, Kamar Gidan Attajirai Haka A Dangi Idan an samu Macce wacce ta iya Karbar haihuwar to Tana iya Zama ta Dangi, duk wani wata 'yar uwa ko matar Dan uwa da zata haihu akan je anemo ta ta karbi haihuwar.

4-Ungozomar Masarauta, Duk Gidan sarauta akan samu Mai Karbar biki na matar Sarki ko Kuma 'ya'yan Sarki ko Kuma Matan 'ya'yan Sarki Dasauransu.

Ayyukan Ungozoma suna da yawa ga kadan daga ciki:

Akwai aikace -aikace da dama da Ungozoma ke gudanarwa kafin haihuwa, da kuma lokacin haihuwa, da bayan an haihuwa.

Sanin Lafiyar Abin da ke Ciki Tun kafin lokacin haihuwa Ungozoma takan je ta duba lafiyar jariri ,misali kwanciyarsa a ciki, motsinsa Dasauransu. Ta hanyar sunkuyawa ta kara kunnwanta kan cibiyar mai ciki, ta yadda Idan ta ji matsala ta gyara mata ta hanyar mulmula cikin a hankali da kuma yin amfani da wani dan karamin Koko wajan gyara Shi ta yadda lokacin haihuwa zai fito cikin sauki salamun -salamun.

Kula da mai Ciki Wani muhimmin aikin Ungozoma za taita kula da mai ciki wajan hanata yin wasu abubuwa ko sata ko hanata shan abu mai daci, da kuma bata magungunan rage Zaki, da kuma samun Karin karfin jiki a lokacin Nakuda.

Gyaran dakin Mai Ciki
Yanayin gyaran dakin mai ciki iri biyu ne kafin haihuwa da kuma bayan haihuwar. Ungozoma takan kawar da kayan dakin mai haihuwa gefe guda dan ta sami sararin da za ta haihu.

Gyaran daki na biyu Shi ne bayan an haihuwa Ungozoma zata gyara dakin tsaf ta maida Shi yadda yake.

Karbar Haihuwa  Dazarar anga Nakuda ta kankama, haihuwa ta doso gadan -gadan sai Ungozoma da dangi masu taimaka wa mai haihuwa su shiga shiri Karbar haihuwar.

Ayyukan Ungozoma suna da yawa kamar bata taimako na abinda za ta sha lokacin Nakuda yankan cibi dss. Amma konan muka tsaya Ina ga za mu iya fahimtar Wacece Ungozoma da kuma Ire-irenta da Irin gudunmawar ta ga mai ciki da kuma abin haihuwa (Jariri).

Babu Shakka Babu Wani mutum a Duniyar Nan da Ungozoma Bata Yi Masa Rana ba.

Jinjina Ga Ungozoma (Midwives).

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Tue 06-08-2019

Sunday, 2 June 2019

ZAKKAR FIDDA KAI DA HUKUNCE HUKKUNCENTA

ZAKKAR FIDDA KAI (ZAKKATUL FITIR)
Zakkar Fidda Kai Sadaka ce da Manzon Allah ya farlanta ta yayin da aka gama azumi, An kiran ta zakkar fidda kai ne saboda tana wajaba ne idan an gama Azumin Ramadan gabadaya. Da Larabci ana kiranta da Zakkatul Fitr Kalmar Fitr an ciro tane daga Iftar (Wanda yake nufin Buda baki), Haka Ita ma Kalmar Iftar an samo tane daga Kalmar Futoo (Wacce ake nufi da Karin Kumallo) (Wato Breakfast).

Hukuncin Zakkar Fidda Kai
Zakkar Fidda kai wajibi ce akan dukkan musulmi, wanda ya mallaki sa'i daya na abinci (kamar kwano daya kenan) wanda ya fi yawan abin da zai ciyar da iyalansa. Mai ba da zakkar zai fitar wa da kansa, matarsa, da duk wanda ciyar da shi take kansa, har ma dan jaririn da yake cikin ciki.
Dalilin wajabcinta shi ne abin da aka rawaito daga Dan Umar (RTA) ya ce, “Manzon Allah (Saww) ya wajabta zakkar fidda kai, sa'i daya na dabino, ko sa'i dayan da sha'ir, an wajabta ta a kan bawa, da da, namiji da mace, babba da yaro daga cikin musulmi. Manzon Allah ya yi umarni a bayar da ita zakkar kafin mutane su fita sallar idi”[Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi].

Lokacin Da Ake Fitar Da Zakkar Fidda Kai
An fi son a fitar da zakkar fidda kai ranar Idi, bayan alfijir ya bullo kafin sallar Idi. Kuma ya halatta a gabatar da ita kafin ranar idi da kwana daya ko biyu, saboda sahabbai sun yi haka.
Ba ya halatta a jinkirta ta har bayan idi, saboda hadisin Dan Umar wanda ya gabata in da yake cewa : “Manzon Allah (Saww) ya yi umarnin a ba da ita kafin fitar mutane zuwa sallar idi”.
Haka ma a cikin hadisin Abdullahi dan Abbas, Manzon Allah (Saww) ya ce, “Wanda ya bayar da ita kafin sallar idi, to zakka ce karbabbiya, wanda kuwa ya bayar da ita bayan sallah, to sadaka ce daga cikin sadakoki”[Abu Dawud ne ya rawaito shi].

Gwargwadon Abin Da Ake Fitarwa A Zakkar Fidda Kai
Kowane mutum sa'i [Sa'i Dayan na Alkama yana daidai da kilo biyu da giram arba'in.] daya ne, daga cikin abincin da dan mutane suke ci, kamar shinkafa, dabino, alkama, saboda hadisin Abu Sa'id Al-khuduriy – Allah ya yarda da shi – ya ce, “Mun kasance muna fitar da zakkar fidda kai daga abinci a zamanin Manzon Allah (Saww) ranar qaramar sallah”
Abu Sa'id ya ce, “Abincinmu a wannan lokaci kuwa shi ne Sha'ir da zabibi da cukwi [Cukwi : Shi ne nonon da ya bushe, a na girki da shi.], da dabino " [Bukhari ne ya rawaito shi].

Wadanda Ake Bawa Zakkar Fidda Kai
Ana bawa wadannan mutanen guda takwas zakkar fidda kai, saboda sun shiga cikin fadin Allah Madaukakin Sarki “Kadai Sadaka a bawa faqirai …”. (Attauba : 60).
Abin lura a wajen wanda za’a bawa har wayau shine, Za a bawa miskini ne ko fakiri wanda ba ya da hali, kamar dai yadda Annabi (SAW) ya ambaci lafazin Miskini, to shi ne za a ba shi, ba lallai sai an rarraba ga wadanda aka ambace su a cikin Ayar Zakka ba cikin suratul Taubah, amma wani yana iya hawa tudu biyu, a ba shi don ya cancanta, sannan sai ya bayar don ya samu wadatuwa.

Hikimar Zakkar Fidda Kai
1- Tsarkake mai azumi daga maganganun wofi da na batsa, saboda abin da aka rawaito daga Abdullahi Dan Abbas (RTA) ya ce, “Zakkar fidda kai tsarki ce ga mai azumi daga maganganun banza da ayyukan batsa, kuma ciyarwa ce ga miskinai”[Abu Dawud ne ya rawaito shi].
Saboda mafi yawanci mai azumi ba ya rabuwa da maganganun da basu da amfani da wasannin shirme, da maganar da ba ta da fa'ida, to wannan sadakar sai ta zamar masa tsarki daga irin wadanncan maganganun haramun da ya yi, wadanda suke rage ladan ayyuka, suna rage azumi
2- Yalwatawa miskinai da talakawa, da wadatar da su ranar idi daga roqon mutane, roqon da yake dauke da qasqanci da wulaqanci a ranar idi, wadda take rana ce ta farin ciki da murna, sai su yi tarayya da mutane cikin farin cikin ranar idi.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Mon 03-06-2019