Monday, 2 October 2017

SHIN A MALIYA (THE RED SEA) NE FIR’AUNA YA NUSTE? Fitowa ta farko



SHIN A MALIYA (THE RED SEA) NE FIR’AUNA YA NUSTE? Fitowa ta farko
******
Larabawa kan kira wannan teku da Bahar al-Ahmar Idan aka fassara zuwa Hausa kuwa sai a kira shi da (Bahar Maliya), Turawa kuma sukan kira wannan teku da “Red sea” wato jar teku. Kafin Jin shin ko anan ne Fi’auna ya nutse akwai bukatar Sanin Tarihin wannan teku kadan (Da yake wannan Teku na daga cikin tekunan duniya masu ban mamaki da marubuta da Masana Ilimin Kimiyya da yawa sukayi rubutu kan ta).
Turawa sun kira wannan wuri da Jar teku saboda yanayin jaja-jaja na tsaunukan da suke wannan wuri da ake kira Bahar-maliya.

Wani shahararren marubuci da ake kira da suna Mr E.M.Foster,ya bayyana cewa,tun tale-tale matafiya da yan safara wadanda suke ratsawa ta wannan teku, suka sa mata wannan suna “Red sea” ko kuma “Bahar-ahmar’’.

Wannan ruwa sune marraraba tsakanin yankin Afrika da kuma yankin Asiya. Ruwan wannan teku suna da tsawon kilomita 2000 sannan fadinsu ya kai kimanin kilomita 300. Zurfin su kuwa ya kai mita 2.500.

wayannan Ruwan suna iyaka da kasashe Takwas, wanda suka hada da kasashe hudu na Afrika, Masar, Eritrea,Jibuti, da Sudan,sai kuma ksashe hudu na yankin, Asiya Saudiya, Yamen, Israila da kuma Jordan.
Anyi ta muhawara akan wai me yasa ake kiran wannan teku da “Jar teku” Inda Wasu daga cikin marubutan kasar Birtaniya, da sukayi rubuce rubuce kan wannan Tekun sun tafi akan cewa, wannan suna na “Red sea’’ da Turawa suke kiran tekun Bahar maliya da shi, ba saboda yanayin jaja-jaja na tsaunuka bane, a’a, sakamakon yawan gamsakuka da take kewaye da gabar tekun wanda idan rana ta haska sai ta mai da tekun ta rinka daukar launin jaja-jaja ruwan dorawa-dorawa, da wasu kaloli daban wannan shine dalilin dayasa ake kiran ta da suna “Red sea’’ wato Jar-teku a hausance.

Masana ilimin kimiyya kuwa, sakamakon nazarin da wasu likitoci da kuma masana ilimin tarihi da halittun cikin ruwa suka gudanar,a shekarar 1646. Wani shahararren likita kuma marubucin litattafan turanci da ake kira da suna Sir Thomas Brown ne ya bayyana a cikin littafinsa cewa, wani masani akan halittun Ruwan-teku da ake kira da suna Sir Walter Raleigh, ya na kan ra’ayin cewa, Bahar maliya dai teku ce da take da launuka daban-daban, ya danganta da bangaren da mutum ya ke kallonta.

Sir Raleigh ya ci gabada bayyana cewa nazarin da yayi game da tekun baharmaliya ya tabbatar masa da cewar wannan teku tana da launuka daban-daban. Wani bangaren kore ne fatau,wani bangaren kuma zaka ganshi fari ne da ruwan dorawa-dorawa, wani gurimma ka gan shi shudi-shudi. Saboda haka kalar kowanne bangare na tekun ta dangantane da yanayin yashi ko kuma lakar da take acan kar kashin kasa.

Sai dai kuma har wa yau daya daga cikin malaman kimiyya kuma shahararren marubuci Carl Drews dan kasar Amerika shi ya musanta wancen zancen na Sir Thomas Brown Inda ya bayyana a cikin littafensa mai suna “Between Migdol and the Sea: Crossing the Red Sea with Faith and Science”, cewa, “ A’a, ruwan tekun maliya ba ja ba ne”. haka kuma ya musanya zance da wasu masana Ilmin Teku da Malaman Tarihi suka bayyana na cewa, A nan ne Allah (SWT) Ya halakar da Fir’auna da Jama’arsa lokacin da suka biyo Annabi Musa (AS).

In shaa Allahu Zan Dakata anan Sai mun hadu a Rubutu na Gaba da Iznin Allah.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
02/10/2017


No comments:

Post a Comment