Nigeria Kasarmu Ta Gado.
********
Shuwagabanninmu na Sayen Manyan Motoci domin hawa wasummu Suna Bukatar In da Zasu sami kuddin Sanyen Abinci. Wasunmu ma na kwana da Yunwa.
ShuwagabanninMu na Daukar Shatar Jirgin Sama Su tafi Kasashen Waje. Amma a koda yaushe suna gaya mana Cewa An sace Kuddin Kasa.
ShuwagabanninMu na Biyawa 'Ya'yansu Manyan Makarantu a kasashen waje amma kullum Sai Su ce mana an wargaza mana kasarmu.
Shuwagabanninmu na Cin abinci su koshe su kwana wuri mai kyau amma idan munyi magana ace mana mun cika Gajen Hakuri.
Shuwagabanni Ku sani Manzon Allah (Saww) yana cewa:
ﻣﻦ ﺍﺳﺘﻌﻤﻠﻨﺎﻩ ﻣﻨﻜﻢ ﻋﻠﻰ ﻋﻤﻞ ﻓﻜﺘﻤَﻨﺎ ﻣﺨﻴﻄًﺎ ﻓﻤﺎ ﻓﻮﻗﻪ, ﻛﺎﻥ ﻏُﻠﻮﻻً ﻳﺄﺗﻲ ﺑﻪ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻘﻴﺎﻣﺔ.
Ma'ana: Duk wanda muka bashi wani aiki daga cikinku sai ya boye mana koda gwargwadon allura ko abinda ke sama da shi to wannan gululi ne da zai zo dashi a ranar tashin kiyama.
Imamu Abu dawud Ya Ruwaito Hadisin a Hadisi Mai lamba 2943.
MU DAI AIKIN MU GAYA MUKU KO KU DAUKA KO KUYI DARIYA, DARIYARKU TA ZAN KUKA GABA DA NADAMAR MAI QIN GASKIYA.
Da Muka Ce Kar Talakawa Suyi Sak wasu sun Kiramu da Maqiya. Yanzun ma idan mun hango mun fadi wasu na mana izgilanci.
A cikin Alqur'ani Mai Girma Suratu Yunus aya ta 58 Allah Yana Cewa;
ﻗﻞ ﺑﻔﻀﻞ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺑﺮﺣﻤﺘﻪ ﻓﺒﺬﻟﻚ ﻓﻠﻴﻔﺮﺣﻮﺍ ﻫﻮ ﺧﻴﺮ ﻣﻤﺎﻳﺠﻤﻌﻮﻥ.
Ma’ana: Ka ce: Ku yi farin ciki da falalar Allah da rahamarSa shi ne mafi alheri daga abin da suke tarawa.
Hakika mu bama bakin ciki da abinda wasu suka samu ko kuma suka tara. Mu ni'Imar da Allah ya mana ta Musulunchi ta Ishemu.
Alhamdul Lahi Ala Nee'Imatul Islam.
Jamilu Sani Rarah
Tue 19/04/2016.
No comments:
Post a Comment