Saturday, 24 November 2018

KUSKURE NE YARDA DA ALLURAR POLIO KO TA YELLOW FEVER

GAME DA ALLURAR POLIO KO TA ZAZZABIN SHAWARA MATSAYIN TUNANI NA DAYA DA BERAN BIRNI
********
Wata Rana Beran Birni Yaje Ziyara a wajen Beran Qauye, Sai Yace da Beran Qauyen, "Abokina amma fa kana shan wahala, kazo nan Qauye ka zauna kana cin Rogo da gyada idan ana ruwa kuma ka shige rame, kuma ramen Yazo ya cika da ruwa idan zai yiwu kazo muje Birni kaga Irin gidan da nake rayuwa a cikinsa (kaga yanda nake rayuwa mana)."

Beran Qauye Ya amince, Bayan Kwana biyu suka Kama hanya zuwa Birni. Daga isarsu sai Beran Birni yaja Beran Qauye a wani Katoton gidan bene.

Mai zai faru bayan Shiyarsu, sai Beran Birni ya kutsa kai ya shiga cikin rame, (nan Beran Qauye ya fara tunani, cewa, au yace inzo muje inga gidan da yake rayuwa a ciki amma kuma naga mun shiga rame).

Bayan shigarsu Ramen Da Dan lokaci sai Beran Birni Yace, To kaga zo mu fita mu gani ko Allah zaisa Masu gidan sun ajiye abinci India hannun mu zai kai mu ci. Anan ma Beran Qauye Ya shiga tunani amma kuma yayi shiru ya bishi suka fita daga ramen zuwa Neman abinci a cikin gidan.

Suna tafiya sai sukazo wajen wani plate Wanda aka ci abinci aka rage, sai Beran Birni yace wa Beran Qauye To Bisimillah yanzu kam ga abinci nan ya samu. Cikin mamaki Beran Qauye Ya Kalle shi tare da wasu tunane tunane a zuciyarsa amma dai yayi shiru baice komai ba, ya fara cin abincin.

Cen suna cikin Cin abincin sai suka jiyo takun kafafuwan mutane suna zuwa inda suke, cikin razani da tsoro Beran Birni Yace da Beran Qauye, Kai yi maza mu koma Rami ga masu gidanan sun dawo.

Bayan sun gudu sun buya Cen Sai Kuma Beran Birni Yace da Beran Qauye Zo mu fita ko za'a dace, Fitarsu keda wuya sai Beran Qauye Yaga An ajiye K'afar kaza a bisa wani faranti yaje haka ya dauka sai Beran Birni ya rike shi yace, dashi "Kai, Ai Mutum mugune, Kada ka dauka tarkone, KA SANI NI DUK INDA NAGA ABINCINA INDA BANA TSAMMANI TO BANA AMINCEWA DA SHI". Wannan Maganar ta Beran Birni Itace Maganar da Nake so mu sanya kwakwalenmu muyi nazari akanta.

Shin turawa Zasu Kashe Makuddan Kuddi su had'a Maganin Polio domin kawai Su taimaka mana? Wallahi A'a Sam Ba zasuyi ba.

Kaje ka karanta Qur'ani sura ta 2 (Al-Baqara) tun daga sura ta 38 har zuwa sura ta 138 Bayani take akan cewa su ba masu Qaunarmu bane.

Ni kam BANA (kamar Beran Birni) duk inda naga abincina Inda bana tsammani to Babu shakka ba zan Amince masa ba.

Jamilu Sani Rarah Sokoto
Sat 24-11-2018

Sunday, 12 August 2018

SIHIRIN DA AKAYIWA ANNABI (SAWW)

A madina lokacin da yake Saura Shekaru 4  Annabi (Saww) Ya Kaura ya bar Duniya Al-amarin ya faru.

Sahabban Annabi (Saww) mutum uku suka rawaito Yadda wannan Al'amarin ya faru daga ciki akwai Nana Aisha (RTa) da Abdullahi bn Abbas (RTA) da kuma Zaidu bn Arqam (RTA).

Dukkanin Wayannan sun bada labari cewa, A watan muharram yahudawan madina, (Wato maqiya Annabi (Saww) suka hadu sukayi Wata tattaunawa (meeting) ta sirri sukayi kancewa Annabi Muhammad (Saww) fa addinin shi na karbuwa ko Ina da ko ina, Kuma gashi a baya munyi sihiri kala-kala ya shanye, munyi tsafi don kashi shi bai mutu ba.

Gashi Anyi yaqin badar bai mutu ba, anyi yaqin uhud ma bai mutu ba, Mun shirya makaqarkashiya anyi yaqin kandab amma ya tsira bai mutu ba.

A Duba bayanin Wannan Zama a Cikin Adh-dabaqatul kubra na ibn Sa'ad.

A Wannan Zaman sai sukayi matsaya akan cewa zasu je wajen wani kwararren masihirci a garin madina Mai suna LABIDU BN A'ASAM (Shi wannan Labidu balarabe ne ba yadudu bane), Ya musulunta amma musuluncin Sa na kafircine.

Bayan Sunje Sun Sami Labidu Sai suka ce yayi musu sihirin Da zai kashe Annabi (Saww) zasu bashi dukiya me yawa (dukiya Mai Nishi), suka shirya suka dauki sule uku 3 suka bashi a lokacin sule 3 kudine masu yawan gaske.

Sai Shi wannan masihirci ya nemi akawo Masa Kayan Da zai hada yayi wannan Sihiri dashi da Farko a kawo Masa tokar Zuma (Bayan an tsotse Zuma Akwai Wata tuka tuka), Sannan A Samo Masa tsarkiya kwaya guda (Wani zare Mai Kama da Jijiya Wanda ake yin jita dashi), sannan aje a Samo Masa hudar dabino namiji da Macce, Sannan a Samo Masa Allura guda Goma Sha daya, Abu na karshe Yana so a Samo Masa gashin kan Annabi (Saww).

Duk aka Samo Masa Wayannan Abubuwan Sai Gashin Annabi (Saww) Ne keda Wuya Sai aka samu Wata yarinya ko Yaro wanda yake shiga gidan Annabi (Saww) aka bukaci ta dauko matajin kan Annabi (Saww).

To da aka Sanya wannan yaro ko Yarinya ya dauko matajin Annabi (Saww) wanda yake taje kanshi, Bayan dauko matajin kai na annabi wanda ya tsufa Annabi (Saww) ya dena ma amfani dashi.

Akwai sauran dangashi daya makale jikin matajin, Da wannan gashi masihircin yasamu ya yiwa Annabi (Saww) sihiri dashi. Wannan matsafi Ya tara duk yaranshi mata suka yi ta yin tofi cikin kulli Da tsafe tsafe, daga cikin yayan nashi wata tace lallai indai har Annabin gaskiya ne To Zai bada labarin wannan sihiri Da aka Yi masa, ta fadi haka ne saboda yadda taga karfin sihirin domin sihirine Me hallaka mutum kai tsaye.

Wannan Masihircin yayi mutum mutumin Annabi (Saww) wato yayi gunkinsa Da danko, sai ya sanya gashin da aka samo na Annabi akan kayin gunkin Annabin da yayi. Yayi duk abinda zaiyi ya gama sihiri akaje can bayan gari ya samu wata tsohuwar rijiya wanda aka dena amafani Da ita, yasa aka shiga cikin rijiyar akwai wani duste cikin rijiyar Qato, aka daga wannan dutsen Akasa sihirin kasar aka danne da wannan dutsin.

To Bayan wannan Sai Annabi (Saww) ya fara rashin lafiya gashin kansa Yana zuba Haka kuma baya iya cin abinci sosai, saboda wannan Sihirin har sai da ta kaiga Annabi (Saww) yana ganin ya kwanta Da iyalinshi amma kuma ba haka bane.

Da ciwo yayi tsanani abu na na cigaba yana ramewa, sai Annabi (Saww) yayi ta addu'a yana addu'a yana neman Allah ya ya ye masa wannan ciwo.

Wata Rana Ya kwanta bacci sai yayi mafarkin mala'ika Jibril Da Mika'il su kazo daya ya zauna ta gefen damarsa daya ta gefen hagunsa sai suka Fara hira

mala'ika Mika'il Yace: Me yasamu wannan bawan Allah wato yana tambayar Jibri (AS), Sai Shi Kuma Yace Masa, Ai Anyi masa sihiri ne, sai Mika'il ya Kara tambayawa Cewa, Wayayi Masa sihirin? Sai Mala'ika Jibril Ya fadi Cewa, Labidu ne Dan A'asam, Kuma an binne sihirin ne akarkashin wata riji sunanta BI'IRI ZARWAN ( ﺏﺀﺭ ﺯﺭﻭﺍﻥ ) tana ciki Garin madina.

Wato kamar suna hirane shi kuma Annabi (Saww) yana jinsu. Suka gama suka tafi Sai Annabi (Saww) ya farka yaiwa Allah godiya, yace wa nana Aisha Allah yabani labarin abinda ke damuna kinji kinji wanene yamin sihiri ya binne a rijiya.

Nan take Anabi (Saww) Ya tura sahabbai suje wannan rijiya sukaje suka ya she rijiyar suka shiga suka daga dutsen da ya danne sihirin.

Suka ciro suka bawa Annabi (Saww) da Annabi (Saww) Yaga irin kulle kullen da ke jikin wannan mutum mutumin nashi, yaga ma sihircin ya soka Allurai goma sha dayane 11, a jikin dankon mutum mutumin.

Sai Allah ya saukarwa Annabi Da surori guda biyu wato suratul FALAQI DA NASI.

Idan Annabi (Saww) ya karanta aya daya daga suratul falaqi sai ya zare allura daya daga jikin wannan mutum mutumin nashi, sai yaji kamar ajikinsa aka cire.

Sai da Annabi (Saww) ya karanta surorin nan Masu dauke Da ayoyi goma sha daya ko wace aya in ya karanta sai ya cire allura daya har sai da yaji jikinshi ya warke yasamu lafiya.

A Duba A Cikin Sahihul bukhari Hadisi na 5763-66 har zuwa Da sittin Da shida.

Da sahihu Muslim hadisi na 2189.

Akwai Abubuwan Lura da Yawa a Cikin Wannan Hadisin Wanda ya kamata mu Yi la'akari dasu.

(1) Wannan Yana Nuna Mu'ujizar Annabi (Saww), Ga yadda aka Bayyana Sihirine Mai Girman Gaske Mai saurin Halakarwa. Amma Kuma Bai kashe Annabi (Saww) Ba.

(2) Na biyu Hadin Kai

Duk wani Abu duniya da kuke so ku aiwatar na Alkherine Kona Mugunta Sai Kun hada Kai kamar Yadda wayannan Yahudawa suka hadakansu suka tattauna.

Haka Shima Labid Sai da Taimakon 'Ya'yansa da suka hada Kai Suka You wannan mugun aiki.

(3) Na Ukku da Makusancinka Ake Hadawa Domin Ganin Bayanka.

(4) Tasirin Addu'ah Ga Dukkan wani Lamari da ya tsananta gareka.

Jamilu Sani Rarah Sokoto

Sun 12-08-2018